← Book details Dukan Ruwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 16 OF 101

Sashe 16

Dukan Ruwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

***
  Washegari tun safe take dakon Raihana tana jira ta ga sadda za ta fita ta mara mata baya. Aikuwa wuraren karfe biyu tana zaune a falon da littafi a hannunta na koyon rubutun hausa tana ɗan duba inda muhsin ya biyamata, Mami kuwa na gefe tana yankewa Muhsin farce sai ga Raihanar,  ta tambayi Mamin zuwa gidan ƙawarta Munirat. Farko Mamin ta hana sai can kuma da ta dage da naci ta samu Mamin ta aminta. Humaira ba ta ko ɗaga kai ba balle ta yi yunkurin miƙewa, har sai da Mami ta soma barin falon, tana nan zaune ba ta ko motsa ba har Raihana ta fito cikin shigar fita, ta ci wani arnen kwalliya ta sanya riga da siket da ya yi matuƙar kama ta sai ta dora afterdress a sama wanda da shi da babu duk ɗaya. Tana fita Humaira ta yi wuf ta miƙe ta zari hijabinta dake hannun kujera. Tuni ta yi shirinta dama ta sa kuɗi a bayan gidan wayarta. Bayan Raihana ta bi, sai da ta kai ƙarshen layin ta nemi can jikin wata  bishiya ta ɓoye fuskarta cikin facemask. Haka ta shiga ɗan sahu ta bi bayanta har gidan su Munirat. Kamar yanda ta zata kuwa hakan ne, wani saurayi matashi ne tsaye jikin wata mota suna hira da wata budurwa. Raihana na karasawa ta cafke da budurwar da bayan ta matso ta gane Munirat ce saboda ta taɓa zuwa can gidannasu ba sau ɗaya ba ba biyu ba.
    Can kuma sai Munirat ta shige gida ita kuwa  saurayin ya buɗe mata gidan gaba ta shiga ya maida ƙofa ya rufe. Baƙar mercedez ce mai baƙin tinted wanda duk iyaka hangen mutum bai isa ya ga na ciki ba.

Humaira ta ji ƙirjinta na dukan tara-tara da wani irin sauri ta soma takawa ta nufi wajen kai ka ce kafin ta karasa abin da take tsoron afkuwarsa ya afku.

Da tsayuwarsu a wajen, da shigar budurwar motar, duka ya faru ne akan idanun Ibb da Fadeel wadanda ke tsaye a ƙofar gidan su Fadeel ɗin su na taɓa hira. Ya rako Ibb ne zai wuce gida suka tsaya. Ganin shigar budurwar ya sa Ibb jan tsaki.

"Wallahi ina mamakin rayuwar ƴan matan yanzu da ba su da kunya kuma ba su san mutuncin kansu ba. Yau da ƙanwata ce daga ita har shi sai sun raina kansu."

Ya faɗi ransa na wani irin ƙuna, Fadeel kuwa da zuciya ta kai mai wuya bai san sadda ya soma takawa ba da sassarfa hakan da ya yi ya sa Ibb bin bayansa da sauri ya dakatar da shi sanin hali.

"Aa Fadeel, please don't, ba ka san waye ba a.."

"Sai nasan waye? Idan ƙanwartaka ce za ka zuba ido kana kallo rayuwarta ta ɓaci!"

Yana kai wa nan ya fisge hannunsa, sai dai kafin ya kai ga tafiya suka hangi Humaira wacce gadan gadan ta nufo motar a fusace.
09

Zuciyar Humaira har wani tafarfasa ta ke yi, tana isa ta sa hannu ta ja murfin motar cikin sa'a kuwa ƙofar ta buɗe. Raihana wacce yatsunta ke sarƙe da na Musaddam gaba ɗaya ta kasa sukuni amma ƙarfin soyayyarsa a ruhinta ya sa ta daurewa ranta, daidai sadda ya kai bakinsa ne da nufin sumbatar hannun aka wangale ƙofar hakan ya sa a firgice gaba ɗaya suka juya. Humaira ta fisgo Raihana, ba shiri ta fito har tana tuntsirawa. Ba ta yi wata wata ba ta ɗauke ta da mari hagu da dama ga wasu zafafan hawaye da suka zubo saman fuskarta lokaci guda. Musaddam tuni ya fito ya zagayo wurinta, hannu ya ɗaga shi ga marar kunya zai ramawa Raihana marin, amma tuni Humaira ta riƙe hannunsa ta ba shi nasa rabon. Hannunta har rawa yake ta sa hannu ta fisge facemask din da ke rufe a hanci da bakinta.

Fadeel ya yi mata ƙuri da idanu babu ko kyaftawa yana jin tamkar gangar jikinsa ne kawai tsaye a wurin, hannu ya sarƙe a kirji yana so ya ga matakin da za ta ɗauka. Humaira da ba ta san wainar da ake toyawa ba, gaba ɗaya ba ta tattare da nutsuwa hankalinta kacokam a tashe yake, yana kan Musaddam da take jin kamar ta shaƙe shi. Ɗan firit da shi sai sirantaka, fari ne yayinda lebbansa suke baƙake wuluk shaidar yana shan sigari. Hannunsa dafe da ƙunci yake duban Humaira rai ɓace ya ce.

"Ke! Ni kika mara?"

Bai yi aune ba ta kara wanke shi da mari.

"Yanzun ka daina tantama? Eh marinka nayi! Da kuma ace ni wata mai ikon ce, abin da ya fi mari shi zan maka. Ɗan iska marar tarbiyya! Ka yi amfani da son da ka ga yarinya na maka za ka cutar da ita saboda a gidanku ba a baka isassan tarbiyyar islama ba sai na bokon da bai amfaneka da komai ba. Idan har ba ka raba kanka da kanwata ba ina maka rantsuwa da Allah sai na yi maganinka ta yadda rayuwarka za ta ƙare a kurkuku. Ke kuma..."

Ta juya gaba ɗaya ga Raihana wacce ke kuka ga dukkan ilahirin jikinta na rawa. Ba ta jin an taɓa tozarta ta irin yau, a gaban saurayin da take yiwa son duniya? Lallai Humaira ba ta da kirki ko kaɗan. Aljanun nata ma ƴan iska ne na ƙarshe da alama.

"Kin ɗauka ba shi jikinki shi ne zai sa ya ga mutuncinki ya gane irin son da kike mishi har ta aureki? Toh kin yi kuskure, wallahi wallahi duk sadda kila bari wannan ɗan akuyan ya kusanceki kin cuci rayuwarki har abada Raihana, za kuma ki yi kukan nadamar da babu mai share maki hawaye. A haka kuke kirana da ƴar kauye, wannan ita ce wayewar? Toh wannan birnin naku na jahilai ku ke ciki, idan za ki farka tun wuri ki farka idan kuwa ba haka ba wallahi muddin irin haka ta ƙara faruwa a kunnen Abba. Wuce kuma mu tafi tun ban kakkaryaki ba."

Raihana ta dubi Musaddam da ya haÉ—e girar sama da ta kasa yana kallonta, ta maida duba ga Humaira wacce ke cika da batsewa kiris take jira ta fashe ga hawaye kace-kace a fuskarta. Ta lura ma jikin Humairar har rawa yake.

"Muddin kika bi umarninta ki sani daga yau babu ni babu ke Raihana, alaƙarmu ya zo karshe. Sannan ke kuma ba ki san waye ubana a ƙasar nan ba ko? Zan nunamaki daga kaina ba za ki ƙara gangancin marin wani namijin ba."

"Musaddam É—an gidan Alhaji Jafar Nababa, right?"

Gaba daya har Humaira suka juya a inda suka tsinci muryar, Raihana ta yi mutuwar tsaye ganin Ibb Gusau mutumin da yar uwarta Futuha ke mahaukacin so tare da wani haÉ—aÉ—É—en guy wanda ko fuskarsa da take a haÉ—e ka kalla, sai ya burgeka. Kunyar da ta ji ne ya sa ta saurin amfani da gefen mayafinta ta rufe baki da hancinta gudun kar su gane ta. Humaira kuwa kallo É—aya ta musu ta maida duba ga Musaddam É—in fuskarta har lokacin a mugun É—aure tana jiran ta ji amsar da zai ba da.

Musaddam ya kai duba ga me maganar, nan da nan ya ji gumi ya karyo masa, Malaminsa ne a jami'a da ya taɓa yiwa gadara da matsayin Ubansa, shi kuwa ya nuna masa nashi Uban da matsayi sun kere na babansa. A sanadin wani rikicinsu sai da Musaddam din ya yi kwanaki uku a ofishin ƴan sanda kafin a fiddo shi. Ya kasa cewa komai sai shafar ƙeya, Ibb Gusau ya nuna shi da yatsa.

"Kai ba za ka taɓa nutsuwa ba kenan a rayuwa ko? Ina mai gargadinka, wannan ya zama na ƙarshe, ke kuma zan ba ki lambata duk sadda kika ƙara ganinsa da ƙanwarki ki kirani kai tsaye nasan maganinsa. Ke kuma ki yiwa kanki faɗa ƴanmata, kar ki bari shaiɗan ya kaɗa maki ganga, irin su Musaddam ba su dace da ke ba. Daga ganin yanayin ƴar uwarki an san daga gidan mutunci ki ka fito saboda haka please be careful."

Raihana da ta yi mutuwar tsaye da mamakin mutumin da Futuha ta ce ba ya magana mai tsawo yana zuba zance ta gyada kai. Ga kuma wani iri da ta ji cewa wai zai ba Humaira lambarsa. Aikuwa Humaira ta miƙa mishi wayarta ya sanya mata lambar ya danna kira ta fito kan wayarsa sannan ya miƙa mata. Musaddam dai na tsaye kamar an kafe shi a wurin ya kasa motsi sai wani ɗaci da ya ke ji a maƙoshi ganin an dake shi an kuma hana shi kuka. Ya yi biyu babu kenan.

"Ko za su bi ka ka sauke su a gida?" Ya yi furucin da sassanyar murya. Sai a sannan ma hankalin Humairar ya kai gareshi karo na biyu don ta mance ma  da wanzuwarsa, ranta ya yi fari sol da taimakon da Ibb ya yi mata, ko ba komai ta ga tsoro fal a saman fuskar Musaddam wanda hakan ya fi komai faranta mata. Ganin irin kallon da Fadeel ke jifanta da shi ya sa ta kauda kai.

"Aa mun gode, zamu hau É—an sahu."

Fadeel kamar ya tanka sai kuma kawai ya basar bai ce uffan ba. Humaira ta kalle su, kalmar godiya ce kadai ta fito a bakinta kafin ta juya ta dubi Raihana.

"Muje." Ba musu kuwa Raihana ta bi umarninta, zuwa yanzu jikinta a mugun sanyaye yake. Ta dai tabbata Humaira ta fi ƙarfinta. Ba kuma ta son tada wani borin su Ibb su ƙara ganin rashin kunyarta ƙarara.

Bayan tafiyarsu, Ibb ya shiga yiwa Musaddam faɗa mai haɗeda nasiha, a karshe  ya ba shi damar tafiya. Sai da ya bar wurin sannan ya dafa kafaɗar Fadeel yana murmushi.

"Toh ya aka yi?"

Fadeel ya zura hannuwansa cikin aljihu ya fiddo hannunsa na dama riƙe da waya ya miƙawa Ibb gami da ɗan ɗara  gira kaɗan. Dariya Ibb ya yi ya girgiza kai.

"No, haba Malam, da wuri haka?"

Ya narkar da wuya.

"Please, ina rantsuwa da Allah ban taɓa jin abin da na ji a kan wata ba sai ita."

Murmushi Ibb ya faÉ—aÉ—a.

"Alhaji da sannu dai Allah zai cika masa burikansa."

Guntun murmushi Fadeel ya yi.
Chapter 16 · 0% Book details