← Book details Turken Gida Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 103

Sashe 8

Turken Gida Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai da na yi mata wani kallo sannan na ce" Ke in kika ƙara zuwa min ikina wani iyayin ga Abba ya zo sai na yi fata fata dake wallahi."
Sai Jidda ta kasa mgana ta tsaya ta na kallona kafin ta ce" Amma Umm."
"Fita ki ba ni waje. Shi bai san in da nake ba ne? Ko sai kin zo kina damuna? Ki sake dawo ki gani in ban yi miki bugun tsiya ba."
Ai Jidda da sauri ta fice tana mai rufomin ƙofa na bi ta da ƙwafa ina faɗin" Ka ji min munasiran yarinya."
Sai da yi kyafci sannan na cigaba da rubutuna amma a kasan raina ina jin zafi shi ai ya san in da nake, tun da bai neme ni ba ni kuma me ya sa zan nuna na san da zuwan shi?
Jira ya ke yi har yanzu na zo ina bashi haƙuri lalle ko bai san taurin kaina ba ne shi ya sa. Wallahi ba zan ba shi haƙuri ba, domin ni ban ga laifin da na yi masa ba. Sai ma shi ne ya yi min laifi da yake buƙatar ya ba ni haƙuri amma ya yi fuska yana jiran ne na fara ba shi haƙuri ai ko sai da ya bushe.

Da safe Amina ta kirani bayan mun gaisa tana mini tambayar banza wai na faɗa ma Yallaɓai na yi ɓari kuwa?
Ƙaramin tsaki na ja kafin na ce" Ban faɗa masa ba. Wani abu ne?
"Kai Ya Sadiya ai kamata ya sani ko?
"To ke sai ki faÉ—a masa tun da ya kamata ya sani É—in"
Sai ta fara dariya ƙasa ƙasa ta na faɗin Allah ya ba ni haƙuri sai na fara masifa ina faɗin.
"Ai bai nemi ya sani ba, tun da na dawo ba ya mini mgana bai ma san ina rayuwa ba sai ni ce zan bishi ina faɗa masa na yi ɓari? A she ma yana gaba na kenan"

Sai Amina ta kashe wayarta ta bar ni ina ta masifa ni kaɗai. Haushin kowa na ke ji yanzu ina shiri zan je Ɗorayi, saboda Balaraba ta kirani kan zuwa Jigawa gobe sunan Saude daman na ce zan je, da safen ba a gidana ya kwana ba saƙo na tura masa kuma har na gama shirina na fita bai dawo mini da amsa ba. Sai da na fara biyawa gida na gaida Gwaggo Alhaji ba ya nan ya tafi Yashe duba gonakinsa. An kusa fara noma damina ta fara mana sallama na ɗan jima a gidan sannan na shiga gidan su Saude. Ma su zuwa sunan ƙannenta ne guda biyu sai ƙannen Saude da maƙota haka gobe za mu tafi sai jibi mu dawo tare da Sauden gabaɗaya tun da mijin ya amince ta dawo gida ta yi jegon ta.  Sai azahar na baro ɗorayi bayan na yi salla a gida shagon Amesty na biya na yi tsifa sannan na yi Saloon yau ma sai da ta yi mini mganar ya mganar buɗe shagona na ce mata ya na nan soon in sha Allahu.

Ban ji a raina zan haƙura da burina ba so kawai nake yi na tsaya da kafafuna amma sai na cika burina na buɗe shagon saloon in sha Allahu. Daga nan na dawo gida sai ma da na dawo gida ne na duba wayata na ga saƙon Yallaɓai na adawo lafiya a raina na ce aikin ɓur in ji tusa, na fara shirin tafiya jigawa suna. Daman tuni na siya Atamfa wajen Dija collection da pampers tare da rigan yaro sai na haɗa mata da setin mayukan jarirai, ina da ƴan kuɗaɗena da su na yi amfani da daddare daman Yallaɓai zai dawo gidana shi ya sa sai da na bari ya shigo gidan yana falo tare da su Jidda sai na fito na kira Jidda ta na zuwa na ce ta je ta faɗa ma Babanta gobe zan je Jigawa Saude ta haihu. Na ga ta tsaya ta na kallona amma yadda na haɗe rai ne ya sa ba ta samu damar mgana ba ta wuce ta koma falon ni kuma na koma bedroom na zauna ina jiran ta.

Can ba daɗewa sai ga shi ta dawo da kuɗi a hannunta sabbi yan dubu ta miƙa mini tana na faɗin" Abba ya ce Allah ya kiyaye hanya."
Ban karɓa ba na bi kuɗin da kallo kafin na ce" Wannan kuɗin fa?
"Shi ya ce na ba ki."
Karɓa na yi na kirga 10k ne cif kamar wata almajira ai ko siyayyan da na yi ma Saude ta fi karfin 10k ballanta a zo maganar kuɗin mota.

Mai da ma Jidda kuɗin na yi sai ta ƙi karɓa ta tsaya tana kallona.
"Ki mayar masa. Na gode."
Kuma yarinya sai ta ƙi karɓa wani kallo na yi mata kafin na ce" Ki karɓa mana."
Sai ta noƙe hannu tana faɗin" Umma kar ki yi haka"
Bai kamata Abba ya ba ki kuɗi kuma ki ce ba za ki karɓa ba."
Baki na saki kawai ina kallon Jidda. Wai ta na faÉ—a mini abin da ya kamace ni.

"Kuma Umma ni dai ba zan iya mayar masa ba sai dai ki mayar masa da kan ki"

Kafin ta rufe baki na watsa mata kuɗin a fusace na miƙe ina faɗin" Ke da kuɗin kar ki bari na buɗe idanuwana na gan ku a ɗakin nan. Ki kwashe su salim alim ki fice ki ba ni waje Jidda."
Amma sai ta tsaya za ta mini mgana ai ko na da ka mata tsawa ina faÉ—in.
"Ki fita na ce ko?
Sai ta duka ta tattara kudin ta fice cikin san yi jiki na dafe kaina ina tsaki, Jidda ma laifina ta ke gani, uban ta na yi min wulakanci tana ƙoƙarin kare masa saboda ba ta da tunani sakarya ce. Ni kaɗai a ɗaki ina ta masifa sai ma na tattara kayana da duk abin da zan buƙata na kai ɗayan ɗakin na can na kwana da asuba ma kuma mun haɗu na fito daga cikin ɗakin shi kuma ya fito daga tiolet muka kusa cin karo, ya yi baya nima na yi baya. Ya kuma kalleni ni ma na kalle shi amma kowannen mu sai ya kauda kan shi, ya shiga ɗakin barcin mu ni kuma na shiga tiolet.

Tun safe na shirya takwas da wani na safe aka kirani an samu mota ana jirana. Kuma ga Yallaɓai bai fita ba. Ba domin yana falon shi ba da ba abin da bai hana ni tafiyata ban yi masa sallama ba. Amma ganin shi a falo ya sa da na fito na yi masa sallama na ce na tafi amma mutumin nan ya na ta duba abu a system ɗin shi bai ko ɗago ba ya ce min Allah ya kiyaye hanya. Kamar zan ce masa zan yi kwana ɗaya amma yadda ya nuna mini halin ko in kula, ya sa na yi tafiya ta ba tare da na yi masa wata mgana ba amma har na kai ɗorayi raina na ƙuna.

Na fara shiga gida na gai da Gwaggo na iske ƴaƴan Ya Abubakar wai zaituna ta tafi Funtua biki, na ce sai su ɗebe miki kewan Alhaji Gwaggo. Ƙarfe tara da rabi muka kama hanya a golf da aka yo mana tasha. Balaraba 5k na ba ta sannan na nuna mata abin da na siya ma Saude ta yi ta mini godiya. Ni ko na ce haba ai Saude ƙanwata ce ballantana ta yi min alheri ƙwarai kuma sakamakon alheri to ya zama alheri ne. Mun isa da azahar lafiya mun iske ana ta suna dangin miji da makota sun cika gida Saude ta ji daɗin ganina sosai ta nuna murnan ta mun sha suna Rahila ta kirani ta ce ta zo gida Gwaggo ta ce ina Jigawa na je suna. Na ce mata wallahi ga shi sai ma gobe zan dawo mun daɗe muna waya da ita kafin mu yi sallama.

Da daddare mu muka gyara gidan da aka ɓata sannan muka shirya ma Saude kayan ta na tafiya. Ta samu kayan suna ba laifi, sai godiya shima mijin na ta ya iya bakin ƙoƙarin shi, bayan duk mun gama ayyukan ina kwance a kan kafitar da aka shimfiɗa mana ni da kanwar maman su Saude Yallabai ya kira waya ta sai na fita falo ina duba agogon bangon da ke ɗaki goma har ta gota amma abin mamaki me ya sa ya ke kirana?

"Assalamu alaikum"

"Kina ina ne?

Ko amsa sallama ta bai yi ba ya tare ni da mganar ko ina ina ne ?

"Ina gidan Saude a jigawa."

"Can za ki kwana ne?

Sai na haɗiye wani abu a maƙoshina saboda na ji kamar a zafafa ya ke mgana.

"E sai gobe za mu dawo tare da ita."

"Da izinin wa za ki kwana? Kin faÉ—a min kwana za ki yi Sadiya?

Sai na kasa magana tun da dai ba ni da gaskiya.

"Sadiya don kina gaba da ni ba shi zai hana tasirin ni mijin ki ba ne ya yi aiki a kan ki ba. Ki na yin abubuwa gaban kan ki ina ta kauda kai amma wallahi kin fara ƙure ni kar ki bari na faɗo kan ki"

Ban yi mamaki ba. To daman ni da ya ke ji ra bai samu dama ba sai yanzu.

"Kin aiko min Jidda da cewa za ki je suna na ce sai kin dawo na aika miki da kuÉ—i kin dawo min da su Sadiya me kike nufi
da ni? A she ba zan ci albarkacin Jidda ki karɓi kuɗin nan ba? Dole sai kin nuna mata ni da ke babu jituwa ko! To kin kyauta kuma ya yi miki kyau."

Ashe dai ya ji haushin dawo masa da kuÉ—in da na yi. Na ko ji daÉ—i a cikin zuciyata da ya ji shima haushin da na daÉ—e ina ji.

"Allah ya kai mu goben ki dawo. Za mu zauna sai ki faɗa min duk abin da na yi miki da zafi da ya sa kika maidani  ni da banza duk ɗaya Sadiya."

"Ka yi haƙuri."

Na faɗa saboda ina so ya ƙyale ni barci nake ji na gaji.
Chapter 8 · 0% Book details