Sashe 16
Turken Gida Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba yadda na iya haka na shirya. Sai a lokacin na fahimci na rame sannan na ƙara haske, wani asibitin kuɗi muka je muna zuwa suka yi mini tambayoyi na faɗa musu wajen wata uku kenan ban ga al'adata ba sun ɗibi jinina da kuma fitsari muka zauna jiran sakamako Yallaɓai kuma sai kira ya ke yi Jidda ce ke ɗaga kiran ni ina ta kaina sai kwanciya nake yi a kujerun asibiti. Lokacin da sakamako ya fito likita ya ba ni farar takarda sannan ya faɗa mini ina da shigar ciki ɗan kimanin wattani biyu da kwanaki. Duk da alomomin masu ciki sun bayyana a tare da ni ban saka ma kaina yaƙini ba. Hawaye suka zubo minibsai na sharce su a cikin raina na yi ma Allah godiya sannan na yi masa kirari. Jidda na wajen domin ita ta riƙe ni muka shiga da muka fito ina riƙe da takardan muka samu adaidaita da zai mai da mu gida. Amma sai da Jidda ta biya Pharmacy ta siya mini magungunar da ya rubutamin na ƙarin jini da na cin abinci.
Da farko da Yallaɓai ya ce zai kira Salisu ya kai mu tun da motar na hannun shi in fita haka ta kama ina kiran shi ni na ce ya ƙyale shi mu fita mu hau adaidaita sahu. Har a cikin adaidaita kwanciya na yi da leda a hannuna ina tara miyau duk cikina da na yi da ga na Jidda har na Baby ban yi miyau ba, kai ban ma yi wannan laulayin mai wahalar wa ba. Tun kafin mu kai gida Jidda ta kira Yallaɓai tana murna tana faɗa mai likita ya ce Umma na da ciki.
"Jidda da gaske kike yi?
Ina ji saboda wayar an ƙure mata kara. A yanayin muryan Yallaɓai za ka san akwai zaƙuwa da zamuɗi.
"Na rantse da Allah Abba Umma za ta sake haihuwa."
Ta faɗa cikin har sai da mai adaidaitan ya juyo yana kallonta ina ganin shi sai da ya yi murmishi ya juya kai ya na faɗin" Hajiya yanzu daman wannan budurwan ƴar ki ce? Wallahi na dauka ƙanwarki ce ni dai dariya kawai na yi ba tare da na yi magana ba.
"Ma sha Allah. Allah ya inganta.'"
Na ce Amin ita Jidda ba ta ma jin sa ta na can ta na waya, ban yi mamakin kalamansa ba saboda ba shi kaɗai ya taɓa faɗan haka ba sau tari mutanen da ba su sani ba in suka ganni da Jidda sai su yi tunanin ƙanwata ce. Saboda na haifi Jidda da ƙananun shekaru shi ya sa muka ta so kamar ƴa da ƙanwa sannan na mori ƙaramin jiki.
Ji kawai na yi Jidda ta manna min waya a kunne ta ce ga Abba na mgana. Sai da na cire facemark na tofar da miyau a ledan da ke hannuna sannan na karɓi wayar
" Yallaɓai."
"Congratulations My Sady. "
"Congratulations Yallaɓai na."
Na faÉ—a a hankali ina murmushi.
"Alhamdulillah Allah abin godiya. Kin gani ko? Daman ni a jiki na na ke jin ba ki gama haifa min Æ´aÆ´a ba Sadiya. Yanzu kin aminta da magana ta?
"Na aminta Yallaɓai."
Na faɗa a hankali saboda jikina gabaɗaya ba ƙarfi, faɗi yake yi yana cikin farinciki mai tsanani sai na katse shi da cewa.
"Yallaɓai ban da lafiya. Jikina ba ƙarfi ba na iya cin abinci ba na shan ruwa."
Na ce kamar zan yi masa kuka shi kuma sai ya ruÉ—e.
"Sannu. Me likitan ya ce! Me ya sa ba su riƙe ki a can ba?
Sai na kasa mgana domin maganar ma wahala take yi mini sai kawai na ce ya bari mu koma gida sai mu yi magana. Dalilin da ya sa ya katse wayar kenan muna ko komawa gida ya sake kira ya na tambayana yadda nake ji.
"Yallaɓai miyau ya yi ta taruwa a bakina. Ni komai ma baya mini daɗi ban iya zama fa sai kwanciya ban taɓa laulayi mai zafi irin wannan ba."
Yallaɓai duk ya damu sai lallashina ya ke yi, daga ƙarshe ya ce zuwa gobe zai dawo na kula da kaina. Sai da ya kashe wayar na ji taruwan kwalla ina tausayin kaina ina tausayin shi ban ɗauka bayan tsawon shekaru goma zan sake samun ciki ba. Amma na yi yaƙini da ubangiji mai bayarwa a lokacin da ya so da kuma wanda ya so. Na saka a raina in ina da rabo Allah zai sake ba ni sai ga shi kuma ashe ina cikin waɗanda Ubangiji ke yi ma Ni'ima in sun yi haƙuri ya ƙara musu a lokacin da ba su yi tssammani ba. Ban taɓa tunanin Yallaɓai zai yi mini rawan jiki in na samu ciki ba sai ga shi yana yi min bawan Allah ya na son haihuwa. Na ɗauka tun da Gimbiya ta haifa masa biyu duka maza yanzu ba ya zumuɗinta amma sai ya kore mini shakku. Lokacin da na faɗa masaa na yi ɓari da ya nuna da yakinin wata rana zan sake samun ciki na haihu bai ɗadani da ƙasa ba kamar yadda bayan samun cikin ya nuna farincikin sa.
Kwana ya yi ya na kirana yana jin jiki. Jidda kam ya yi mata kashedin ta kula da ni ban san adadi ba. Baby da Jidda ta faÉ—a mata Umma za ta haifa musu wata Baby yini ta yi tsalle da ihu ni dai ina kwance zama ma ba na so ina yi.
Washegari da rana Yallaɓai ya dawo duk da ba gidana zai sauka ba, yana gidan Gimbiya ne tun da ni ranar da zai bar gidana ya yi tafiyar. Amma duk da haka gidana ya fara sauka ya duba ni ya iske ni kwance da gwangwani miyau da a ka cika min da ƙasa. Ya rumgumeni nima na lafe a jikimsa shi ina sauke numfashi. Yallaɓai ya yi ta shafa marata kamar ya buɗe ya ga abin da ke ciki. Shi kan shi ya ce na rame bakina ya bushe ya yi ɓawo to ko ruwa fa ba na sha sannan ban iya cin komai sai kunin tsamiya.
Duk bakina da surutu na bakina ya mutu. Allah ya sa Jidda na gida ita ke kula da gidan da yin abinci. Yallaɓai ya faɗa ma Gimbiya ina da ciki ya kuma kawo ta ta duba ni ita da su Khalipa, ina kwance ne ina fama da kaina a saman kujeran falon su Jidda. Ina kallon Gimbiyar tun da muka gaisa ta koma gefe ta tsume. Duk da ban da lafiya amma na fahimci kamar ranar ranta na bace ne, sai na danganta haka da ƙila ita da Mijinta ne. Ko jiran shi da ya ce ta yi ma ba ta yi ba, la'asar na yi ta ce min za ta ta fi wai za ta biya ta shago. Su Khalipa ma da Jidda ta ce ta bar su sai ta ce wai daga Shago Gwammaja za ta biya shi ya sa ba za ta bar su ba. Ni dai ina kwance amma sai da na tofa na ce ta bar su mana in Yallaɓai ya dawo sai ya mai da su amma sai ta ce kar wai su dame ni ba ni da lafiya. Ina jin haka ban takura ma kaina ba na ce su gaida Nene in sun je.
Tun kuma daga ranar sama da sati ba ta dawo ba na tuna lokacin cikin Khalipa da kwanciyar da ta yi ta yi a asiniti ina jigila da ita. A raina na ce da ban haihu ba da na ji haushin duniya. Munnira ce ta kira ni a waya tana faɗa mini haihuwar Salma Yayar Jawahir C.S a ka yi mata, a ranar da ta kira ni ta ce jiya da daddare ne ta haihun shi ne ta kira ni ta ji yaushe za mu je! Tun da anan Kano ne a Dala. Shi ne na ce mata ba ni da lafiya ma ina gida. A ranar ta zo duba ni kafin in faɗa mata ina da ciki ita ta fara cewa matar injinya ciki ne da ke na ce mata e sai ta buga shewa ta riƙe hanci ta rangaɗa guda ta kuma kira Hauwa tana faɗa mata sai Hauwa ta fara faɗa min an ware ta ba a faɗa mata ba. Ni ko na ce ba wanda na sanar ma wa, nan Munnira ta yini har da lissafin sai ta ɗauko DJ ranar sunan na yi dariya kawai a raina na ce Allah ya sa na rabu dai lafiya.
Washegari sai ga Hauwa ta zo duba ni. To su ne da aka haɗu ca gidan Salma ranar suna duk wanda ya ga bai ganni ba sai su ce ina gida ina fama da laulayi. Anan ne wasu suka ji, su Anty Bahijja kuma ina da tabbacin Gimbiya ta faɗa mata gwara ma Anty Maimuna in ta ce ba ta sani ba amma zai yi wahala Anty Bahijja ta ji abu ita ba ta ji ba musamman za ta kira ta a waya ta faɗa mata. Anty Zuwaira har gida ta zo ta duba ni ta ba ni dubu ashirin ta ce na siya gero tun da na ce kunu kawai nake sha ina son ta saboda wallahi tana da matukar kirki shi ya sa nake girmamata. Ita ta ce mini Nene ce ta faɗa mata ba ni da lafiya ta zo ta duba ni, Nenen kuma na san Yallaɓai ne ya sanar da ita. Mubeena na zuwa duba ni akai akai har Marwa ma ta zo ita kuma Kawu ne ya faɗa mata ita kuma ta yaɗa ma Ya Aina ta nan maganar cikina ya faso a dangin mu kowa ya ji sai ya ce ikon Allah lalle bayan wuya sai dai daɗi sannan ba a cire ma Ubangiji yaƙini in ka yi hakuri za ka ci riba. Sun zo dukkansu sun duba ni har da Ma'u Gwaggo ma ta zo har gida kuma na ji daɗi su Ya Hamza a waya suka gaishe ni da matan su. Zainatun Ya Abubakar ta zo yi min yini, ta yi mini wanki da girki ranar.
Da farko da Yallaɓai ya ce zai kira Salisu ya kai mu tun da motar na hannun shi in fita haka ta kama ina kiran shi ni na ce ya ƙyale shi mu fita mu hau adaidaita sahu. Har a cikin adaidaita kwanciya na yi da leda a hannuna ina tara miyau duk cikina da na yi da ga na Jidda har na Baby ban yi miyau ba, kai ban ma yi wannan laulayin mai wahalar wa ba. Tun kafin mu kai gida Jidda ta kira Yallaɓai tana murna tana faɗa mai likita ya ce Umma na da ciki.
"Jidda da gaske kike yi?
Ina ji saboda wayar an ƙure mata kara. A yanayin muryan Yallaɓai za ka san akwai zaƙuwa da zamuɗi.
"Na rantse da Allah Abba Umma za ta sake haihuwa."
Ta faɗa cikin har sai da mai adaidaitan ya juyo yana kallonta ina ganin shi sai da ya yi murmishi ya juya kai ya na faɗin" Hajiya yanzu daman wannan budurwan ƴar ki ce? Wallahi na dauka ƙanwarki ce ni dai dariya kawai na yi ba tare da na yi magana ba.
"Ma sha Allah. Allah ya inganta.'"
Na ce Amin ita Jidda ba ta ma jin sa ta na can ta na waya, ban yi mamakin kalamansa ba saboda ba shi kaɗai ya taɓa faɗan haka ba sau tari mutanen da ba su sani ba in suka ganni da Jidda sai su yi tunanin ƙanwata ce. Saboda na haifi Jidda da ƙananun shekaru shi ya sa muka ta so kamar ƴa da ƙanwa sannan na mori ƙaramin jiki.
Ji kawai na yi Jidda ta manna min waya a kunne ta ce ga Abba na mgana. Sai da na cire facemark na tofar da miyau a ledan da ke hannuna sannan na karɓi wayar
" Yallaɓai."
"Congratulations My Sady. "
"Congratulations Yallaɓai na."
Na faÉ—a a hankali ina murmushi.
"Alhamdulillah Allah abin godiya. Kin gani ko? Daman ni a jiki na na ke jin ba ki gama haifa min Æ´aÆ´a ba Sadiya. Yanzu kin aminta da magana ta?
"Na aminta Yallaɓai."
Na faɗa a hankali saboda jikina gabaɗaya ba ƙarfi, faɗi yake yi yana cikin farinciki mai tsanani sai na katse shi da cewa.
"Yallaɓai ban da lafiya. Jikina ba ƙarfi ba na iya cin abinci ba na shan ruwa."
Na ce kamar zan yi masa kuka shi kuma sai ya ruÉ—e.
"Sannu. Me likitan ya ce! Me ya sa ba su riƙe ki a can ba?
Sai na kasa mgana domin maganar ma wahala take yi mini sai kawai na ce ya bari mu koma gida sai mu yi magana. Dalilin da ya sa ya katse wayar kenan muna ko komawa gida ya sake kira ya na tambayana yadda nake ji.
"Yallaɓai miyau ya yi ta taruwa a bakina. Ni komai ma baya mini daɗi ban iya zama fa sai kwanciya ban taɓa laulayi mai zafi irin wannan ba."
Yallaɓai duk ya damu sai lallashina ya ke yi, daga ƙarshe ya ce zuwa gobe zai dawo na kula da kaina. Sai da ya kashe wayar na ji taruwan kwalla ina tausayin kaina ina tausayin shi ban ɗauka bayan tsawon shekaru goma zan sake samun ciki ba. Amma na yi yaƙini da ubangiji mai bayarwa a lokacin da ya so da kuma wanda ya so. Na saka a raina in ina da rabo Allah zai sake ba ni sai ga shi kuma ashe ina cikin waɗanda Ubangiji ke yi ma Ni'ima in sun yi haƙuri ya ƙara musu a lokacin da ba su yi tssammani ba. Ban taɓa tunanin Yallaɓai zai yi mini rawan jiki in na samu ciki ba sai ga shi yana yi min bawan Allah ya na son haihuwa. Na ɗauka tun da Gimbiya ta haifa masa biyu duka maza yanzu ba ya zumuɗinta amma sai ya kore mini shakku. Lokacin da na faɗa masaa na yi ɓari da ya nuna da yakinin wata rana zan sake samun ciki na haihu bai ɗadani da ƙasa ba kamar yadda bayan samun cikin ya nuna farincikin sa.
Kwana ya yi ya na kirana yana jin jiki. Jidda kam ya yi mata kashedin ta kula da ni ban san adadi ba. Baby da Jidda ta faÉ—a mata Umma za ta haifa musu wata Baby yini ta yi tsalle da ihu ni dai ina kwance zama ma ba na so ina yi.
Washegari da rana Yallaɓai ya dawo duk da ba gidana zai sauka ba, yana gidan Gimbiya ne tun da ni ranar da zai bar gidana ya yi tafiyar. Amma duk da haka gidana ya fara sauka ya duba ni ya iske ni kwance da gwangwani miyau da a ka cika min da ƙasa. Ya rumgumeni nima na lafe a jikimsa shi ina sauke numfashi. Yallaɓai ya yi ta shafa marata kamar ya buɗe ya ga abin da ke ciki. Shi kan shi ya ce na rame bakina ya bushe ya yi ɓawo to ko ruwa fa ba na sha sannan ban iya cin komai sai kunin tsamiya.
Duk bakina da surutu na bakina ya mutu. Allah ya sa Jidda na gida ita ke kula da gidan da yin abinci. Yallaɓai ya faɗa ma Gimbiya ina da ciki ya kuma kawo ta ta duba ni ita da su Khalipa, ina kwance ne ina fama da kaina a saman kujeran falon su Jidda. Ina kallon Gimbiyar tun da muka gaisa ta koma gefe ta tsume. Duk da ban da lafiya amma na fahimci kamar ranar ranta na bace ne, sai na danganta haka da ƙila ita da Mijinta ne. Ko jiran shi da ya ce ta yi ma ba ta yi ba, la'asar na yi ta ce min za ta ta fi wai za ta biya ta shago. Su Khalipa ma da Jidda ta ce ta bar su sai ta ce wai daga Shago Gwammaja za ta biya shi ya sa ba za ta bar su ba. Ni dai ina kwance amma sai da na tofa na ce ta bar su mana in Yallaɓai ya dawo sai ya mai da su amma sai ta ce kar wai su dame ni ba ni da lafiya. Ina jin haka ban takura ma kaina ba na ce su gaida Nene in sun je.
Tun kuma daga ranar sama da sati ba ta dawo ba na tuna lokacin cikin Khalipa da kwanciyar da ta yi ta yi a asiniti ina jigila da ita. A raina na ce da ban haihu ba da na ji haushin duniya. Munnira ce ta kira ni a waya tana faɗa mini haihuwar Salma Yayar Jawahir C.S a ka yi mata, a ranar da ta kira ni ta ce jiya da daddare ne ta haihun shi ne ta kira ni ta ji yaushe za mu je! Tun da anan Kano ne a Dala. Shi ne na ce mata ba ni da lafiya ma ina gida. A ranar ta zo duba ni kafin in faɗa mata ina da ciki ita ta fara cewa matar injinya ciki ne da ke na ce mata e sai ta buga shewa ta riƙe hanci ta rangaɗa guda ta kuma kira Hauwa tana faɗa mata sai Hauwa ta fara faɗa min an ware ta ba a faɗa mata ba. Ni ko na ce ba wanda na sanar ma wa, nan Munnira ta yini har da lissafin sai ta ɗauko DJ ranar sunan na yi dariya kawai a raina na ce Allah ya sa na rabu dai lafiya.
Washegari sai ga Hauwa ta zo duba ni. To su ne da aka haɗu ca gidan Salma ranar suna duk wanda ya ga bai ganni ba sai su ce ina gida ina fama da laulayi. Anan ne wasu suka ji, su Anty Bahijja kuma ina da tabbacin Gimbiya ta faɗa mata gwara ma Anty Maimuna in ta ce ba ta sani ba amma zai yi wahala Anty Bahijja ta ji abu ita ba ta ji ba musamman za ta kira ta a waya ta faɗa mata. Anty Zuwaira har gida ta zo ta duba ni ta ba ni dubu ashirin ta ce na siya gero tun da na ce kunu kawai nake sha ina son ta saboda wallahi tana da matukar kirki shi ya sa nake girmamata. Ita ta ce mini Nene ce ta faɗa mata ba ni da lafiya ta zo ta duba ni, Nenen kuma na san Yallaɓai ne ya sanar da ita. Mubeena na zuwa duba ni akai akai har Marwa ma ta zo ita kuma Kawu ne ya faɗa mata ita kuma ta yaɗa ma Ya Aina ta nan maganar cikina ya faso a dangin mu kowa ya ji sai ya ce ikon Allah lalle bayan wuya sai dai daɗi sannan ba a cire ma Ubangiji yaƙini in ka yi hakuri za ka ci riba. Sun zo dukkansu sun duba ni har da Ma'u Gwaggo ma ta zo har gida kuma na ji daɗi su Ya Hamza a waya suka gaishe ni da matan su. Zainatun Ya Abubakar ta zo yi min yini, ta yi mini wanki da girki ranar.