← Book details Turken Gida Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 103

Sashe 15

Turken Gida Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Musbahu na nema tun da shi ne ɗan gida ne kuma idon gari ne kusan ya san ko'ina. In da Allah ya taimake ni kuɗin da Yallaɓai ya tura mini na hidimam makaranta da na ce zan mai da masa sai ya ce na riƙe na ƙara jari ya bar mini, da su na yi amfani domin ƙara bunƙasa kasuwancina. Musbahu ya shige mini gaba a ka buga mini ledojin da tambarin logona na SADY S YASHE HIJABS AND MORE. An yi manya da ƙanana sannan an yi na kwali su na manya costumer ne
Sannan an yi min sticker na mannawa a jikin kaya bayan na siya ledoji farare da zan riƙa saka hijaban da kayan in an siya. Tun dai an samu zaman gida bari mu kama sana'a zama bai ganmu ba. Musbahu ya saka cikin masu zanen su na kamfani ya zana min logo mai kyau na saka shi a duka handle ɗina na kafafen sada zumunta.

Kuma kowa ya gani sai ya ce sunan ya yi kyau. Ya Hamza sai da ya ce bai ga sunan Yallaɓai ba ina dariya ban ce komai ba har Ma'u da muka daɗe ba mu yi mgana ba da na ɗora a status a ƙasa na yi caption da cewa.

"SADY HIJABS AND MORE. Muna siyar da nau'in hijaban da kuke so sannan za mu fara kawo muku inners wears, kamar su pants, bra, sikat, mini trouser and more. Please potonorize your Sister. Sadiya Sulaiman Yashe C.E.O"

A nan Yallaɓai ya gani ya yi tagging ya turo mini dariya. Na shaka na auna masa naushin hannu na sticket kawai sai ya yo mini Vn ranar ma ba a gidana ya kwana ba yana gidan Gimbiya amma a daran zai dawo gidana.

"Daman shawaran nan na kawo miki tun farko kiƙa ƙi karɓa. Duk wanda ya tuba don wuya ba lada."

Haka ya ce min fa sannan ya ƙarishe da dariya. Ina masa Typing sai ga shi ya sake turomin mgana.

"Congratulation My Sady. Duk abin da kika saka ma suna ko hannu sunan shi Nasara. I wish you the best"

Kalamansa suka wanke mini zuciya na fasa tura masa abin da na yi niyya.

"Thank you Mijin Sadiya."

Kamar ya ijiye wayar amma dai ya tafi bai kashe data ba. Mutane sai fatan alheri suke yi mini har Anty Maimuna sai da ta ce yana da kyau kam na ƙara da wani abun Anty Zuwaira kuma ta yi tagging da zamu siya in sha Allahu. Daman ita ai ba ta da matsala Anty Bahijja ne ta gani ba ta yi mgana ba. Amma har Gimbiya ta yi mini murna sannan ta ce za ta yi mini talla a status ɗin mutanenta su gani ko za su siya na ce Na gode. Daga nan na kashe data na sauka sai zuwa can an juma Sameena ta kira ta ce ta na son hijabai da na pant da bra shi ne take faɗa min a status ɗin Yallaɓai ta gani ya ɗora sai da muka gama waya sannan na buɗe data na gani.

Ya saka ne amma bai yi wani rubutu ba. Na ga kara domin sun ta sakawa a status suna yi mini tallah. Marwa ma ta saka Hauwa ma da ta yi waya Munnira ma haka yan gidanmu Ya Balki sai Amina har da Datti Ya Auwal dai da Ya Hamza ba a saka su a lissafi su waɗanan ba su damu da saka statua ba irin Yallaɓai ne. Ya Abubakar kuma shi wannan ɗan buga buga ne bai ma cika hawa online ɗin ba. Gidan su Yallabai su Musbahu ne da su Adnan sai Jawahir da su Suwaiba sune daman nawa. Duk kuma wanda ya ga logon zai ce zane ne, ma su abu da abin su kura da kallabin kitse.

Kamar wasa na yi ta samun odar masu siyan hijabai da inners barin ma da azumi ya ke tunkaro mu. Da ya ke a mota kawai ake saka mun ina tura masa bayanan da kololin na Hijabai inners kuma sara na yi da yawa na yara da manya na tura kuɗi a ka kawo minI har na cin kasuwar salla. hijaban dai sai na ƙaro tun da guda 50 na ce a akawo mini. Da suka iso duk wanda ya siya ni da Jidda muka yi zaman saka su. A leda muna manna sticker sai lamarin ya burgeni ni kaina komai da tsari kan ya fi burgewa Jidda ta yi Vadeo muna saka sticker ta kuma ɗora mini a status ta ce kaya sun iso. Nan da nan cikin sati ɗaya kaya suka ƙare sai na sake tura kudi ɓarin ma Inners ɗin sun tafi yadda ma ban yi zato ba daman su Hijabai ana siyan su sosai. Wannan karon sai na ce a sako mini da mayafai da kayan barci suma dai ba laifin ana ta siye da na gida da na waje.

Sana'ata na riƙe gadan gadan. In dai ka ganni da waya to ina can ina marketing. Yallabai har suna ya sauya min wai hajiyar Hijabai ni dai na ce ka ji da iyayin ka tun da karatun dai bai zo hannuna ba gwara na kama abin da ya zo hannuna. Ana cikin haka a ka kawo mana kayan saka ranar Suhailat ɗin Anty Bahijja bayan sallar azumi za a yi bikin kuma Kaduna za a kai Amarya. Ni da kaina na kira ta a waya na yi mata Allah ya sanya alheri. Ni ba na gaba da ita muna gaisawa in mun haɗu amma daga wannan gaisuwan kowa sabgan gaban shi yake yi tun da aka yi mana tsakani ni da ita.

Cikin ikon Ubangiji muka riski watan ramadana cikin lockdow abubuwa duk sai a hankali saboda yanayin zirgan zirgan gari duk da ba kamar lokacin gari na sake ba wannan karon ma Yallaɓai ya siya buhun gero da siga sai wake buhu ɗaya na alale da ƙosai na kai ma Maman Saude yin kunin ita kuma Maman Nana mai yi min kitso a ka ba ta yin ƙosai da alalen. Sannan ya rarraba ma matansa da ke aiki a ƙarkashin sa kayan abinci wasu kuma ya ba su kuɗi, daga can Rano Kawu Abba ya aiko mana da su ƙwai da dankalin turawa. Nima Yallabai ya ba ni kayan abinci har da kuɗi na kai gida duk da na san itama Gimbiya ya ba ta ta kai can Rano amma ni bai gaya mini ba, ban nemi da sai na ji ba kuma
Azumi ashirin da tara muka yi kuma ban sha ko ɗaya ba ko da ban ga period ɗina ban damu ba, ko watan da ya wuce ma bai zo ba saboda an sha yin azumi ni ban sha ba sai ban saka tunanin komai a raina ba. Yallaɓai ya yi mana kayan alfarma ni da yara har salla ta wuce muna saka sabbin kaya sannan ya yi ma iyayena har Inna Mariya ya yi ma turmin atamfa wannan shekaran. Ni kuma na caɓa da cinikin hijabai da inears wannan sallar kaf su Ya Hamza wajena suka yi ma iyalansu siyayya kuma na ji daɗi a dangin Yallaɓai kuma su Musbahu ne da su Anty Zuwaira har Anty Maimuna ta siya ma yara. Gimbiya ma ta siya kuma ta kawo mini costumer kuma na ji daɗi na gode mata. Yallaɓai ma kuɗi ya ba ni na yara sai kawai na cire musu a ciki da ni kaina na saka kuɗin a ciki. Kuma ba abin zan ce ma Allah sai godiya ina samu ina yi ma kaina hidima sannan abu na ƴan uwa ya ta so ina ɗauka na yi ba sai na je ina yi ma Yallaɓai yar murya ba.
An É—aga bikin É—iyar Anty Bahijja sai gab da babbar sallah a bakin Munnira nake jin wai uban mijin ne ya biya ma Sulaihait É—in kujeran makka tare da mijin ana É—aura auren za su tafi tare na ce Allah ya sa su je lafiya su dawo lafiya.

****

Kamar kar a yi salla sai na fara rashin lafiya. Kuma rashin lafiya irin a tsatsaye haka. Kasala ya riƙa damuna na dai na cin abinci komai ba ya mini daɗi ban da kunin tsamiya mai zafi ba abin da ke shiga cikina. Sannan ba na iya shan kowani ruwa. Ba ni da aiki sai kwanciya tun ina ganin abin wasa har dai na fara tunanin watakila ina da ciki. Tun da in dai na ci abinci sai na yi amai ga Yallaɓai ba ya nan ya je Dutse wajen kwanan su huɗu a can, karyata kaina nake yi da ba ciki gare ni ba saboda ko wancan da na yi ɓarin shi ban ga alamomin shi ba sai kawai na fi amimta da maleria ke damuna na saka a ka siya mini mganin maleria na fara sha. Ai duk ranar da na sha sai na yi amai sannan sai na fara miyau
ba na iya haɗiye miyau. Sannan na yi ta kwana da zazzaɓi gari na wayewa sai na ji sauki. Jidda ta ce za ta rakani asibiti na ce ba zan je ba har waya ta sata ta yi ma Yallaɓai waya ta faɗa mai halin da na ke ciki sai ya ce ta ba ni wayar haka ya riƙa mini faɗa ya kuma ce umarni ne maza maza na tashi na shirya Jidda ta rakani asibiti na ga likita.
Chapter 15 · 0% Book details