← Book details Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 97 OF 212

Sashe 97

Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hatta glass door din sai da tabi tayi scrubbing É—insu,ta goge yanar É—akin,lokaci guda kamanin É—akin suka canza,Komai na son gyara,Toilet ta shiga nan ma tataras dashi duk sai a hankali,sae da ta fara gyarashi fess,Sannan ta samu ta É—an watso ruwa tare da É—auro alwala,
  Darduma ta dauko cikin wadrobe ta shimfiɗata,ta kabbara sallar azhar,A tsanake tayi sallar tana kammalawa,agalabaice bacci ya ɗauketa saman dardumar,

Wuraren ƙarfe 2:30 Abusufyan ya shigo cikin gidan hannunshi ɗauke da Ledojin da yayi masu take away na restaurant,
  Da sallama ya shiga cikin falon,wuce wa bedroom ɗin yayi,ba ƙaramin mamaki yayi ba,ganin yadda Jahad ta gyara ɗakin tsaf,komai yayi fess,kamar lokacin da Zainabun shi na nan,
  Murmushi ya saki tare da samun wuri kasa gefenta ya zauna,Ya ajiye ledojin,Hannu yasa abayanta ya ɗan bubbugi kafaɗarta"Jahad!tashi muci abinci,"
  Firgita tayi ta farka tana Sambatu"Ya Rafayet,baisan na taho ba...,"
  Ƙiris ya rage yaji abunda tace,
Hannu tasa da sauri ta toshe bakinta,tana kallonshi,Shima kallon nata yake yi,
   "Me kika ce"?girgiza mashi kai ta shiga yi,tana faɗin"bakomai Daddy,Ashe ka dawo,nagaji ne shi ne na ɗan kwanta don in huta,"
  Murmushi yayi tare da cewa"Ae naga aikin da kikayi,kin yi ƙoƙari sosai,"
  "Bari na ɗauko mana plate,"ta miƙe tare da nufar hanyar fita daga ɗakin,
  Sai da tafito sannan ta dafe saitin zuciyarta tana faman sauke ajiyar zuciya,a ranta tace"Allah yaso daddy baiji abunda nace ba,dashi kenan zai gano ni,"_
Tayi maganar tare da yin saurin wuce wa cikin kitchen ɗin,A cikin kwandon wanke wanke ta samu tray da plates tare da cups,gaban basin taje ta wanke su tass da klin da soso,ta ɗaurayo su,bayan ta kammala wankesu saman tray din ta jera su,Ta ruƙosu a hannunta sannan ta dawo cikin bedroom ɗin,
  "Salamu Alaikum"Ta kwaɗa sallama ta shiga ciki,Zuƙunnawa tayi ta ajiye trayn agaban Abusufyan,
  Janyo ledar tayi ta buɗe,tare da sanya hannu ta curo fried meat(tsiren nama)ta jera masu shi asaman tray,hannu yasa ya taimaka mata wurin ɗauko sauran kayan,Cool Drinks ne da sauran kayan maƙwalashe,atare suka shiga ci suna fira gwanin ban sha'awa,bayan sun kammala cin abincin,Abusufyan ya tattara kayan abincin da sukayi amfani dashi,Ya wuce dasu kitchen yabarta zaune tana shan lemu,bayan ta shanye,ta sanya robar a dustbin,komawa tayi saman gadon ta kwanta,cikinta yayi haƙe² saboda cin muguntar da ta yi,wani baccin ne ya sake ɗaukarta,

*Boss Bature*

  ❤🤍❤

Wuraren ƙarfe 3 na rana Sgr ya dawo cikin gidan,Tun bayan da ya fita da safe Ko breakfast bai nema ba,saboda Emergency call ɗin da akayi mashi acan headquater ɗinsu,Jikinshi na sanye da Tank Top,light green,Tare da wandon kaki,Yayin da kunnanshi ke manne da wayarshi,Cikin harshen faransanci yake yin waya,
  Da sauri da sauri ya haye upstairs,direct ya wuce part ɗinshi,tunkan ya shiga ciki ya fara jin daddaɗan ƙamshi nakai mashi ziyara acikin hancinshi,gaba daya yayi tsammanin cewa zai same ta ne a part ɗin nashi amma baiga Kowa ba Wayaam,Bedroom ɗinshi ya shiga,Shaf shaf ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,After some minutes ya fito waist ɗinshi ɗaure da towel,Yana tsaye agaban mirror yaji motsin mutun acikin falonshi,
   "Who's there"?yayi tambayar yana jiran amsa,
  "Sehrish ce,"
Ajiyar zuciya ya É—an sauke tare da cewa"Come in,"
  Hannunta na ruƙe da tray na Lunch ɗinshi da ta shirya mashi,tana tafiya gabanta na faɗuwa rass rass
  Sallama ta fara yi mashi ya amsa,kafin ta sanya ƙafa ta shiga ciki,sum sum ta lalla6a ta ajiye mashi tray asaman table,Jiki na rawa ta juya zata bar ɗakin,
  Zuba mata ido yayi ta cikin mirror yana kallonta,tana ƙoƙarin ɗaga ƙafarta tabar ɗakin taji ya Ambaci sunanta kai tsaye"JAHAD"
  DARAAAM!!!!!!Taji gabanta ya faɗi,sanƙamewa tayi atsaye,hankalinta a matukar tashe,tuni zufa ta shiga wanke mata fuskarta,Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya abakinta,Abun ya ɗaure mata kai,farat ɗaya Sgr ya gane cewa ba Sehrish bace,Hatta junaid yau bai ganeta ba,kowa ɗaukar sehrish yake yi mata,saboda sunsa ma ransu cewa da jahad aka tafi,Shiyasa basu natsu sun gane cewa itace ba,"
   Wata irin zufa ce ta shiga gangarowa asaman fuskarta,ƙiris ya rage ta saki fitsari a wando,
Slowly ya juyo tare da tunkararta,jikinta sae kerma yake yi,hannunta ya ruƙo tare da juyo da ita ta gabanshi ya kasance suna fuskantar juna,wuƙi wuƙi tayi mashi da idanu tana faman mazurai na rashin gaskiya,
   Abun ya ɗaure mashi kai,Wai harshi zasuyi wa wayau,kamar wani soko,An gaya masu cewa a banza yakai muƙamin da yake dashi a yanzu,
   goya hannayenshi yayi asaman wide chest ɗinshi,Ya zuba mata ido yana kallon Ikon Allah,
   Saboda tsabar rashin gaskiya tun kafin ma yayi mata magana,murya na kerma tace"Amm...um..babban..yaya pls dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun,Wayyo Allahna na shiga uku,"a ruɗe tayi maganar,tana yarfa hannuwanta,tsoranta kada ya kwashe ta da mari,
  Ruke ha6arsa yayi cike da mamaki yake kallonta from head to toe,
   Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,tun kafin ma taji hukuncin da zai yanke mata,Zuciyarta sae bugawa take yi ba ƙaƙƙautawa,
   "Where's she"?fuskarshi a ɗaure yayi tambayar,
  Sunnar dakai tayi kamar munafuka,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Wlh baban yaya ni bani nace ta tafi ba,yau ne dama da asuba,ta same ni cikin damuwa take tambayata lafiya shi ne na sanar da ita cewa Ni banso nabi Daddy kano,bansan zuwa garin saboda abunda ya faru damu acikinshi...."
  Tunkan ta ƙarasa maganar yace"What!tafiya tayi without My Permission,"ranshi a matuƙar 6ace yayi maganar,
  "Ya salam"ya furta hakan tare da zura hannunshi cikin sumar kanshi,
Ya runtse idanuwanshi,
"Am sorry,babban yaya bazan ƙara ba,"_
Jinjina kanshi yayi tare da ware idanuwanshi akan fuskarta,yana kallonta duk tabi ta susuce,
   "Kin iya frog jump ko"?
Waro ido tayi tana kallonshi,girgiza kai tashiga yi alamar a'a,
...ruko hannunta yayi ya fito da ita cikin falonshi,fuskarshi a daure yace"Oya,start from here,karki kuskura ki tsaya,if not zaki ga abunda zai biyo baya,"
   Jahad tamkar zata fashe da kuka,Zuƙunnawa tayi tare da kama kunnanta kamar ɗan kwaɗo haka tafara yin tsallan tana zagaye kujerun,tun a first round jikinta ya fara gaya mata,Komawa yayi cikin bedroom ɗinshi ya ɗauki wayarshi daya bari agaban Mirror,Numbar Uncle Abusufyan ya lalubo,ya danna mashi Call,

A lokacin Abusufyan,Na acikin kitchen ya tu6e rigarshi daga shi sai shorts,ya dage sai aikin goge goge yake yi da Æ´an wanke wanke,ya gyara kitchen É—in tsaf,
  Fitowa Sehrish tayi hannunta ruƙe da wayarshi,har tuntu6e take yi wurin yin sauri donta kai mashi wayar,tana baccinta mai daɗi ringing ɗin wayar shi ne ya tashe ta,

"Daddy,ana kira,"ta ƙarasa maganar yayin da take shiga kitchen ɗin,hannu abusufyan yasa ya kar6i wayar,duba screen din wayar ya fara yi,
   *My first in-Law* Shi ne sunan daya bayyana akan screen ɗin,Yayi mamakin ganin kiran Sgr,Picking call ɗin yayi ya kara wayar a kunnanshi,
   "Assalamu Alaikum"
On the other hand,Sgr ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,Uncle kun isa Lafiya"?
.  "lafiya Lou,ae tun ɗazu muka ƙaraso,"
   "Okey,inason magana da sehrish ne,tana a kusa"?
   Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"Ae bada ita muka zo ba,ko ka manta ne?
   "Uncle,Da ita ka tafi bada Jahad ba,yanzu haka jahad tana a part dinta,Sunyi musaya ne,"
  Cike da mamaki abusufyan yace"Jahad tana a gida!"
  Gaban Sehrish ne ya faɗi rass,wuƙi wuƙi tayi da ido,ɗagowa abusufyan yayi tare da kallonta,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin ya shaida cewa Sehrish ce,ya ɗauko amatsayin Jahad,Ko ya akai suka shirya Wannan batare da kowa ya ankara ba,
  Sunnar dakai ƙasa tayi,ganin irin kallon da daddynsu yake yi mata,
  Rai a6ace ya miƙa mata wayar"Kar6i nan,"
  Hannunta na kerma ta kar6i wayar,hankalinta a matuƙar tashe,ta sanya wayar a kunnanta,muryarta tamkar zata yi kuka tace"Ya rafayet........"
   Tunkan ta ƙarasa maganar ya daka mata tsawa"Shut up!"nan take ta shiga taitayinta,
    "da iznin wa kika bar garin nan"?_
  Idanuwanta ne suka cicciko da kwalla,Sae faman kallon uncle take yi,sam baiji daɗin abunda sehrish tayi ba,don yasan ƙarshe kanshi abun zai ƙare,
   "Am sorry ya rafayet,dan Allah kayi haƙuri,Bazan ƙara ba,"
  dogon tsoki yaja,Kafin yace"Come back home,In ba haka ba,Ranki zai 6aci,"yana faɗin hakan yayi rejecting kiran,
  Fashewa tayi da matsanancin kuka,
Hannu abusufyan yasa ya kar6e wayar,
  "Koma meya laifinki ne!Ashe baki da hankali Sehrishi!Why kike son Jamin ina zaman lafiyana?,Taya zaki kamo hanya batare da iznin Mijinki ba,?"
   Cikin shesshekar tace"dan Allah daddy,kayi haƙuri,na kwallafa raina ne akan son zuwa,nasan nayi laifi,Kuma nayi danasanin yin hakan,Amma dan Allah daddy,Ka roƙan mun alfarma a wurinshi,Yabarni in zauna,Saboda yace in koma gida yau ɗin nan,"ta ƙarasa magana tare da sanya hannu tana share hawayenta,
  "I can't Call him Sehrish,rafayet bazai saurari kowa ba a halin yanzu,Kawai kije ki shirya kayanki,in kaiki tasha ki hau mota,"
Jin haka yasa ta ƙara fashewa da matsanancin kuka,tana faɗin"dan Allah daddy,kada ka mayar dani,Nashiga ukuna,"
  Sosai take kuka,Shi kanshi ya tausaya mata,duk yadda take shakkar Sgr amma ta kama hanya ta baro gidan batare da izninshi ba,tabbas ba ƙaramin son zuwa takeyi ba,
   Muryarshi a sanyaye yace"Kiyi hakuri daughter,babu yadda zamuyi dole ki bi umarnin Mijinki,lokaci yana ƙurewa,ki je ki shirya kayanki,mu tafi tasha,"
  Juyawa tayi da gudun gaske,Ta koma ɗaki,Saman gadon ta faɗa tare da fashewa da wani sabon kukan,
Chapter 97 · 0% Book details