← Book details Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 166 OF 212

Sashe 166

Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Azmee bata haihu ba Sae daren Ranar Allah yayi zata haifi santalelen ɗanta Namiji,Ko wanke jikin jaririn ba'a kaiga Yi ba,Kwatsam Ba zato ba tsammani Sojoji Su kayi masu dirar Mikiya,A fusace sojojin nan suka shigo,Kuma sunci sa'a Gaba ɗaya family ɗin sun taru a gidan suna jiran Haihuwar Azmee,Bisa umarnin Salahuddeen A lokacin shine shugaban sojoji na Nigeria,Umarni aka basu kai tsaye su kashe duk wanda suka Gani acikin Family house ɗinsu,amma banda mata da ƙananun Yara,Nan fa sojojin nan suka buɗe masu wuta,ta ko'ina sautin bindigu kake ji,Sunga tashin hankalin da basu ta6a gani ba,Anan Suka kashe ubaid da kuma Uba,Daga ciki hada iyayensu mata,domin sunyi ƙoƙarin Ɗauko makamai a cikin ɗakunansu da niyyar su taimaki Mazajensu,wannan ya tabbatar masu da cewa suma matan suna da sa hannu a aikata ta'addanci tunda har sunsan suyi harbi da bindiga,aikuwa suka kashesu gaba ɗayansu,A ranar an zubda jini kamar kamar mi,Daga cikin waɗanda tsautsayi Ya ritsa dasu,Hada Jabeer bawan Allah baiji ba bai gani ba,Suka kashe shi,A lokacin yazo duba jikin Azmee yaga in ta sauka lafiya,Shigowarshi keda Wuya,Sojojin suka harbeshi saitin zuciyarshi,Anan Ya yanke jiki ya faɗi matacce,

A ƙarshe mutun uku suka tsira,Azmee data 6oye a ƙarkashin gadon mahaifiyarsu,hannunta ruke da jaririnta, itama Saratu Ta tsira a wannan Lokacin,Sae kuma Gali tare da Ya sayyadi da basa acikin gidan abun Ya faru,

Azmee bata tashi sanin Jabeer ya rasu ba,Sae a washe garin ranar,ta fito daga ƙarkashin gadon hannunta ruƙe da jaririnta,jini duk ajikinshi domin ba'ayi mashi wanka ba,haka ta fito dashi rungume a hannunta,ta tsorata da ganin yadda sojoji suka wanke gidan da jinin Iyayenta,Tasha kuka kamar ranta zai fita,A lokacin Allah ne kawai Yayi zata rayu,A nan tsakar gidan taga gawar Jabeer yashe a ƙasa,ga gawawwakin Sauran Ƴan uwanta,nan take ta yanke jiki ta faɗi kasa a sume,jaririn hannunta ma Ya faɗi wanwar yana ta tsala kuka,

Bayan wasu kwanaki da yin wannan Tashin tashinar,Azmee ta farka a gadon asibiti,bayan ta shafe sati biyu kwance bata acikin hayyacinta,

Tasha kuka kamar ranta zai fita,ita sam bata damu da iyayenta da aka kashe mata ba,Mijinta tafi ji,shi da baisan komai ba,Bai aikata laifin komai ba,Amma an haÉ—a dashi an kashe,

Hamma Ghali ne Ya kawo ta asibitin,Lokacin data farka tare da sayyadi da saratu tagani tsaye akanta,sune ke jinyarta tun daga wannan lokacin rayuwarsu ta tagayyara,mutane suka ƙyamace su,kowa gudunsu yake yi,saboda sanin Abunda iyayensu suka aikata,Idan suka biyo hanya har jifarsu akeyi da duwatsu ma,Dole suka daina shiga cikin jama'a,

Tundaga wannan Lokacinne,Hamma ghali Ya tunzurasu akan su ɗauki fansar kisan wulakancin da Family ɗin SALAHUDEEEN HOSSEIN suka Yi masu,Kunji silar shigar Azmee ƙungiyarsu,Wadda bayan Su salahuddeen sun ruguzata a karo na biyu,Ghali kuma Ya tada ƙungiyar ta hanyar wasu abokanan Iyayensu da suka rage ba'a kamasu ba,A lokacin ne kuma Salahuddeen yabar duniya,Saboda ɗaukar fansa Azmee ta jefa kanta cikin halaka,duk don saboda Mijinta da aka kashe,ko lokacin bataso shiga ƙungiyar ba,Hamma ghali ne Ya tunzurata sosai har saida ta amince Ta tsunduma tsulundum,Da ita da Ya Sayyadi da saratun dukkansu,Jinjirin da Azmee ta haifa ba kowa bane,Face Haroon shine ɗanta da take dashi ɗaya tilo,

Shiri na musamman sukayi domin ganin sun tarwatsa Family ɗin salahuddeen,Wannan yasa suka raba kansu,Ya sayyadi yabi Ta 6angaren Abusufyan dake zaune a kano,Da biyu ya shiga rayuwar abu saboda kawai Ya cimma burinshi na Ƙuntata rayuwar Abusufyan,Azmee kuma ta hanyar hajjaju ta biyo masu,Sai da tayi bincike sosai ta gano cewa hajjaju tana da kusanci sosai da mutanan gidan kuma itace ke kai masu ƴan aiki duk in suka buƙata,Wannan dalilin ne yasa taje har gidan hajjaju ta nemi da ta taimaka mata ta samo mata aiki a gidan Abban sojoji,
Ganin yarda take roƙonta,Ga ƙaramin yaro yasa hajjaju ta tausaya mata,har dai ta amince zata sama mata aiki a gidan,kuma cikin sa'a Batare da ta sha wahala ba,ta samu aiki agidan duk da dama sai da tayi ma hakan shiri........"

  *Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*
 
 

  *Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*
 
 
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋

𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1

قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤
𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠

*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*

_Ga masu karanbanin haɗa mun document,koda gigin wasa kada wanda ya kuskura Ya ƙara haɗamun document,kuma bazaku ta6a samun Complete document na takun ƙarshe ba,saboda ba yanzu zan haɗa shi ba koda na kammala littafin,Dole sai a wurina za'a same shi from page one to the end,if not babu wanda zai baku shi cikakken shi,Sannan Zan canza Lokacin posting_

Lokacin dana fara aiki acikin gidan nan,mahaifinku ya mayar dani tamkar ba ƴar aiki ba don alokacin ya tambayeni game da mahaifin yarona,na sanar dashi cewa ya rasu dalilin hadarin mota,daga haka kuma na kulle bakinshi don kar ya nemi jin wani bayani agame da dangina,Ya ɗauki Haroon ɗansa,Kuma Ya nuna yana so inbar mashi haroon ya kasance acikinku,baya son Ya taso a matsayin bare,Ba ƙaramin daɗi naji ba,Duk da mummunan ƙudirin da nake dashi,

Tsawon Lokaci da fara aikina cikin gidan nan,na fara shirya maku maƙarƙashiya,da niyyar tarwatsa farin cikin gidan nan,Amma silar kyautatawar da mahaifinku keyi mun da kuma wasu daga cikinku yasa na ɗan dakata,Akwai wani hadithi da manzon Allah (SAW) yake cewa"Jubilatul ƙulubu ala hubbi man ahsana ilaiha,Wabugudi man Asa'a ilaiha,(An halicci zuciya da Son mai kyautata mata da kuma ƙin mai munana mata),Wannan kyautatawar da kuke Yi mun ita ta Jani har izuwa tsawon lokacin nan Batare dana Aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ba,a lokacin banyi tsammanin zan faɗa tarkon son wani acikinku ba,Sai gashi na kamu da tsananin Son mahaifinku,Saboda yafi kowa kyautatamun,Ya yarda dani sosai Kuma ya damu dani akan kowa na cikin gidannan,Da yake ita zuciya ba ƙashi ne da ita ba,bansan lokacin dana afkawa Sonshi ba,sai kuma na fara kishi da Alexandra,don nasan cewa muddin tana acikin gidan bazan ta6a samun soyayyar mahaifinku ba,Wannan dalilinne Yasa nayi Amfani da sihirina wurin Ƙuntata mata,ta fara jin ƙunci acikin ranta,Zaman Nigeria ya gagareta,babu arziƙi ta tattara tabar ƙasar nan,batare da ta ƙarasa shayar da Junaid ba,ta barshi cikin tsummanshi yana ɗan jinjirinshi.......... "

Bata ƙarasa maganar ba,Sakamakon wani irin kukan Kura Da Mommy tayi takai mata damƙa a wuyanta,Muryarta adisashe take magana hawaye na zuba"Amma kin cutar dani Azmee,Kin cuci rayuwata,Da kuma rayuwar Junaid,Ashe kece silar dana tafi nabar mijina da ƴa'ƴana,I will neva forgive you....."kasa ƙarasa maganar tayi,nan take ta fashe da kuka,Daƙyar Abba ya samu ta saki wuyan Azmee,har tangal tangal tayi zata faɗi da sauri Jahan ya ruƙota,Ya taimaka mata ta zauna saman hannun kujera tana kuka"matar nan tajima tana cutar da rayuwarmu,Dama ance makashinka Yana tare dakai"Sosai take kuka,Ita kanta Azmeen kukan takeyi,Su Sehrish da Jahad dukkansu kuka sukeyi,Oummansu ma idanuwanta cike tab da kwalla,
Bayan ta tsagaita da yin kukan taci gaba da cewa"A lokacin mahaifinku Ya ɗauki Junaid ya bani shi don inci gaba da shayar dashi,babu yarda Hajiya azeema batayi ba akan Ya bata Junaid ta shayar dashi,Amma ya nuna cewa yafison na shayar dashi,Ba don komai ba Sae don baison Junaid Yayi nisa dashi,tunda ita a lagos take zaune,bayan ya damƙamun Amanar Junaid,naci gaba da shayar dashi,Allah shine shaidata,Inason Junaid sosai,Fiye da son da nake yi ma haroon,Sai na dinga ji kamar ni na haifeshi,har banso su Fawan suzo ɗaukarshi,gashi lokacin haushina suke Ji saboda ina ƴar aiki ƙasƙantacciya an bani Ƙaninsu ina shayarwa,ni kuwa daɗi na dinga Ji,Saboda ina tunanin ta hanyar Junaid zan samu soyayyar mahaifinku don tsakani da Allah nike sonshi hakan yasa banyi mashi wani sihiri ba wai don ya so ni,babu wanda yasan Inasonshi,Sae Laila matar Ishaq da yake ƙawatace duk da ba wani shiri nake da ita ba,Amma ina neman shawara awurinta,haka Hajjaju ma muna mutunci da ita,Dukkansu babu wanda yasan Ainihin wacece Ni,Duk irin son da nake yi ma Abbanku bai ta6a lura ba,Naso na sanar dashi amma ina tsoron Yace baiso na,bansan wani hali zanshiga ba,Lokacin da Junaid Ya fara tasawa,abunda Ya bani tsoro dashi irin wayon dake gare shi,Kullum agabanshi nake yin waya cikin harshen fulatanci,kwatsam wata rana,bayan na kammala waya,sai yake ce mun ae Yaji duk abunda nace,A lokacin na ɗauka da wasa yake yi don nasan baijin fulatanci,Sai cewa nayi toh ya faɗamun me nake cewa acikin wayar,ba zato ba tsammani Yaron nan Ya fassara mun maganganun da nayi acikin wayar,hankalina yayi mugun tashi,Ko makaranta ba'a sanyashi ba,na ruƙe shi ina tambayarshi a ina ya koyi harshen fulatanci,Sae ce mun yayi a wurina yaji ina yi,duk in zanyi waya,tunda naji haka saina tsorata dashi,tabbas wata rana zai iya tona mun asiri,tunda har ya iya yaren da nake yi wanda a waya kawai nake magana da harshen,Kawai na yanke shawarar In juye mashi tunaninshi ta yadda bazai ta6a fahimtar komai ba,Tun daga wannan lokacin Junaid Ya zama soko,Bai ɗaukar karatu ko mis'ƙala zarratin,Nasan na cuci Junaid,Da ace Yayi ilimi da ina da tabbacin cewa zai kasance ɗaya daga cikin ƴaran da duniya zatayi alfahari dasu saboda baiwarsu,A kwana a tashi,Rana ta farko dana fara Yin tozali da Rafayet,Bazan ta6a mantawa da wannan Lokacin ba,dawowarshi kenan daga U.S,Ya soma tambayar ina Babyn da Mommynsu ta bari,Su fawan ke sanar dashi cewa Yana a wurin mai aikinsu har suke bashi labarin cewa ni na shayar dashi,Ranshi yayi mugun 6aci Yasa su kirani,Na fito ɗauke da Junaid a hannuna,ya rufesu da faɗa don me za'a ba mai aiki ta shayar da ƙaninsu,sun tabbatar da tsaftar jikina ne,A karshe ya kar6e Junaid daga hannuna,Ya wuce dashi dakinshi,
Chapter 166 · 0% Book details