← Book details Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 191 OF 212

Sashe 191

Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

 
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💖💖💖💖
💖💖💖
💖💖
💖 *ABBAN SOJOJI* 💖
💖💖
💖💖💖
💖💖💖💖

```The father Of Soldiers```

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*

Story
&
Written
by
*_Hafsat Bature_*

~(Boss Lady)~

Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1

Dedicated to my beloved sisters. 😍

Proud Of My First Novel💋

_Warning banyarda wani yayi amfani da wani sashe na littafina ba, kada a ta6amin komai na littafina,Sannan kar a kuskura a haɗamun document,Ga mai buƙatar karanta Littafin Abban Sojoji from Book one to 3 yayi mun magana ta whatsapp 08103884440_

قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

Baccine ya fara ɗaukarshi,a hankali ya ƙarasa hawa saman gadon ya kwanta gefenta,duk bata sani ba,saboda baccin da yayi awon gaba da ita,bai jima da kwanciya ba,bacci ya ɗaukeshi,can cikin bacci ta dinga jin numfashinshi asaman neck ɗinta,mutsu mutsu ta soma yi zata buɗe idanuwanta,ta ko'ina taji tamkar an ɗaureta,gaba ɗaya sumar kanshi ta lullu6e idanuwanta,ƙoƙarin raba jikinta ta soma yi da nashi,kiciniyar data rinqayi ne tana kokarin janyeshi,Yasa shi farkawa,shi kanshi baisan ya akai suka haɗe da juna ba,sun manne sosai,gaba ɗaya ta shige ƙirjinshi,hannunshi na dafe da ita,

Fashewa tayi da matsanancin kuka,na takaicin haɗa jiki da sukayi,ga baƙin cikin hannunshi daya sanya abayanta,ta kasa janyewa,saboda nauyi,ta haɗa uban gumi akan fuskarta,

Daƙyar ya iya buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci,ɗago da kanshi yayi,ya kasance tsinin hancinshi na gogar forehead ɗinta,janye hannuwanshi yayi daga saman bayanta,karaf idanuwanshi suka sauka akan surar jikinta,rigar ta cukuikuye ta nannaɗe,Fararen cinyoyinta sun fito waje,daga sama rigar ta zame,har ta sauko under boobs ɗinta,fatar jikinta har wani salƙi take yi saboda kyau,

Kasa janye idanuwanshi yayi daga kan jikinta,Sam bata lura ba,tana ta shessheƙar kuka,hawaye sun wanke fuskar sae kace ta haɗa jiki da wanda ba muharraminta ba,

Lokacin data buɗe idanuwanta sosai,taga yadda ya zuba mata ido batare da ƙyaftawa ba,a hanzarce Ta soma bin jikinta da kallo,ranta yayi mugun 6aci duk a tunaninta shiya yaye mata rigar,don ya biya buƙatarshi,jikinta har kyarma yake yi wurin sanya hannu ta janyo rigar ta mayar da hannunta,taja can ƙasan ya rufe ƙafafun,

Shi dai baice mata komai ba,zuba mata ido kawai yayi yana kallonta,
  Cikin shessheƙar tace"Dama abunda kakeso kenan,ina jinya ma ba zaka ƙyaleni ba,"
  Aruɗe Sgr ke kallonta don bai fahinci inda zancen nata ya dosa ba,wani irin kallon tsana take jifarshi dashi,Saukowa tayi daga saman gadon,da gudu ta fuce daga ɗakin tana kuka,

Runtse idanuwanshi yayi tuni sun cicciko tab da kwalla,ta harzuƙashi sosai ranshi ya 6aci,sai daga baya ya gane me take nufi,hannu yasa ya daki mattress din,Zuciyarshi sai tafarfasa take yi,

Cusa hannunshi yayi acikin sumar kanshi yana cakuÉ—ata,har lokacin bai buÉ—e idanuwanshi ba,sai faman cizon le6ensa yake yi,har sai da ya fasa shi,

Almost 15 mins,kafin ya sauko daga saman gadon ya nufi hayar fita daga ɗakin,Lokacin daya fita,Bai sameta ba,tuni ta shige bedroom ɗinsu,ta faɗa cikin toilet ta rufo ƙopar,wani irin ƙululun baƙin cikine ya tsaya mata aranta,aduk lokacin da ta tuna cewa Sgr ba sonta yake yi ba,Jikinta yake so,shiyasa har ya gaza hakura ta samu sauƙi yazo yana neman ƙara yi mata illa,hakan yasa ta ƙara jin tsanarshi acikin zuciyarta,a jikin ƙopar ta zuƙunna tana shessheƙar kuka,

Jiki a sanyaye Sgr ya wuce upstairs,kaitsaye yana shiga bedroom ɗinshi,Ya zube ƙasa saman guwowinsa,Ya kwantar da kanshi agefen gadon,Batare daya hau saman gadon ba,wani irin raɗaɗi yake ji acikin zuciyarshi,yayi mamakin dabai iya tsawatar mata ba,lokacin da take gaya mashi maganar nan ba,Ƴar ƙaramar yarinya tana shirin Zautar dashi,ta ko'ina ta gama dashi,ta kanainaye dukkan wani sashe na zuciyarshi,

Acikin wannan yanayin Omar ya same shi,yazo tashin shi sallar asuba,hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,A sukwane ya tsaya a ƙopar ɗakin yana kallonshi,still Yana zuƙunne saman guiwowinsa,ya kifa kanshi saman gadon daga gefe,sumar kanshi duk ta rufe kanshi,

A hankali Omar ya ƙarasa cikin ɗakin,zugunnawa yayi agefen Sgr,cikin sanyin murya ya ambaci sunanshi"Rafayet,"shiru bai amsa mashi ba,hannu yasa ya ɗan bubbugi shoulder ɗinshi,Sai lokacin Sgr ya amsa mashi"na'am,"
  Xama Omar yayi tare da janyoshi zuwa jikinshi,a saman kafadarshi Sgr ya ɗaura kanshi,
  "Meya faru ne"?
Shiru bai amsa mashi ba,
  "Plss tell me what's wrong with u?Meya hanaka bacci?meyasa kayi kneeling?
  Dogon numfashi yaja kafin yace"Omar,she's trying to kill me,bansan me na mata ba,ta tsani koda kallo na,Why zata yi mun haka?sai da ta bari ta saba mun da kanta sannan zatayi mun Illa"
  Tsananin tausayinshi ne ya kama Omar,don ba ƙaramin jiki yake ji ba,tun daga kan yarda yake magana,nunfashinshi na fita da huci....'
  "Pls rafayet,just be strong,har yanzu fa ita matarka ce,Mallakinka,so bai kamata kana sanya damuwa ba akanta,"
  "Omar,ba zaka gane bane....'
Shafa Sumar kanshi Omar yayi"Ka kwantar da hankalinka,zanyi magana da ita,"
  Daƙyar ya samu ya lalla6a Sgr,ya shiga toilet ya ɗauro alwala ya dawo ya shirya cikin jallabiya,jikinshi duk ba daɗi,tare da Omar suka tafi masallaci,

Bata fito daga cikin toilet din ba,Sai da tayi alwala,tukunna ta fito tana faman ɗan gyasa ƙafa,Still bata daina zubar da hawayenta ba,
  "Sehrish!"oummansu ce ta ambaci sunanta,firgit tayi tare dakai idanuwanta kan oummansu tana kallonta,zaune take saman gadon bata jima da farkawa ba,
  "Lafiyarki kuwa?yaushe kika shigo ɗakin?a ina kika kwana ne"?
  Cikin sanyin murya tace"daga ɗakin aunty azmee nake,acan na kwana,"
  "Ya jikin naki"?tayi tambayar a yayinda take saukowa daga saman gadon,Ta nufi inda sehrish take a tsaye,"da sauƙi Oumma,"rungumota abu tayi ajikinta,
  "Allah ya baki lafiya rishi ɗina,na damu sosai akan halin da kike ciki,"
  Sosai sehrish ta ƙankameta"Oumma,dan Allah ki tayani da addu'a,Akan Allah ya yaye mun damuwata,"
  "Wata irin damuwace wannan?ko zan iya sani"?shiru tayi tana tunanun amsar da zata bata,
  Jin haka yasa abu ta gane cewa bataso ta faɗa mata ne,
  "Shikenan,Zan tayaki da addu'a,kema kuma ki dage da yin addu'ar,"ta ƙarasa maganar tare da sanya hannu ta raba sehrish daga jikinta,suka dan zauna gefen gadon,
  Zuba mata ido abu tayi tana kallonta,maganar da abusufyan ya sanar da ita take tariyowa acikin kanta na cewa Sehrish tana da aure,taso suyi maganar da ita,Amma ta kasa,ta zuba mata idone har zuwa lokacin da Sehrish ɗin taso ta sani,don ta lura 6oye mata take yi,
  "Kinsan wani abu"?
Girgiza kai sehrish tayi"A'a"
Murmushi abu ta ɗan saki kafin tace"Lokacin da mahaifinku ya nuna yana sona nayi matuƙar yin mamaki sosai,Saboda ni bakowa bace,mata dayawa suna sonshi,Suna rubibinshi kamar suyi hauka,Kuma abunda zai baki mamaki waɗannan matan dake sonshi,Sunfi ni komai,gasu ƴa'ƴanmasu kuɗi ni kuma ƴar maigadi,Amma a haka Ya nace ya like yace dole saini,Ni kuma saboda kafiyata da taurin kai irin nawa,Sai zuciyata ta dinga saƙa mun cewa yana mu'amala da mata don kawai ina ganinshi atare dasu shiyasa na fara zarginshi,ashe bansani ba nayi kuskure,sau dayawa muna samun dama a rayuwarmu sai muyi watsi da ita,kuma sai daga baya muzo muna danasani,Na yanke ma mahaifinku hukunci batare dana tabbatar da abunda nake zargi akanshi ba,wanda silar hakan na jefa rayuwata cikin haɗari........"dakatawa abu tayi tuni hawaye sun soma sauka daga kan fuskarta,Sehrish kuwa tunda Oummansu ta soma maganar nan,ta natsu tana sauraronta,
  "Ba'ason yankewa mutun hukunci cikin sauri,batare da an tabbatar da abunda ake zargi akanshi ba,Akwai buƙatar yin bincike sosai,hanyoyi dayawa da zaka iya jaraba mutun kafin ka yanke mashi hukunci,Wanda ni banyi tunanin yin hakan ba,A wannan lokacin,kawai idona ya rufe saboda kishi,nayi wasa da damar da nake da ita,Sai gashi nazo ina danasani mara amfani....."kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,Sai ta dinga jin maganar oummansu tamkar da ita take yinta,wasu siraran hawayene suka soma sauka akan fuskarta,
  "Ita dama sau ɗaya take zuwa ma mutun,da ace a wannan lokacin nayi amfani da damar da nake da ita,da ban jefa rayuwata cikin hatsari ba,da kuma rayuwar ƴa'ƴana,sai gashi ata dalilin hakan Har gidan mahaukata aka kaini,ni nasan bankyauta ma rayuwata ba,Mutanan da su kayi mun halacci na butulce masu,mutumin dayasoni ya qaunace ni,duk da matsayina na ƴar maigadi,hakan baisa ya ƙyamace ni ba,wlh danasani bata da amfani......"
  Cikin shessheƙar kuka Sehrish tace"dan Allah Oumma kidaina tuna abunda ya wuce,banason ina ganin hawayenki,"
  Girgiza kai abu ta ɗanyi kafin tace"indaina tuna abunda ya wuce?baƙya tunanin wannan zai zama darasi ga ƴan baya?waɗanda Allah yaba ma dama irin tawa suke ƙoƙarin yin watsi da ita....."
  Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,gani take kamar oummansu tana yi mata gargaɗine a fakaice,duk da tasan batasan abunda ke wakana ba,Amma tasha jinin jikinta,
  "Don me ake bamu tarihin Annabawa da waɗanda suka zo kafin mu?Ba don muji daɗinshi ba kawai face don muyi koyi da kyawawan dabi'unsu da halayansu,mu kuma ɗauki darussan rayuwa acikinsu,"
  Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tare da sanya tafin hannunta asaman fuskar oummansu tana share mata hawayenta,
  "Hakane oumma,kin faɗi gaskiya,"
Murmushi abu tayi"banaso kuma kuyi irin kuskuren da nayi,shiyasanya nake faɗa maki wannan,"ta ƙarasa maganar tare da wuce wa ta gefen Sehrish ta nufi toilet tana faɗin"Ki tada su hosana da jahad,su tashi suyi sallah,"
  "To oumma,"abu na shiga toilet,hakanan tadinga jin gabanta na faɗuwa,kalaman oummasu sunyi matuƙar ta6a mata zuciyarta,hankalinta ya tashi ba kaɗan ba,kokwanto ta shiga yi Akan Sgr,Gaba ɗaya ta rikita kwakwalwarta,tayi zurfi acikin tunaninta Muryar Jahad ta katse ta"My Own sis!"firgit tayi tare da juyawa tana kallon Jahad,dake ƙoƙarin miƙewa zaune,
  "Lafiya naganki zaune kamar kina acikin damuwa"?
  Da sauri tace"babu komai,Oummace tace na tashe ku daga bacci lokacin sallah yayi,"
  "Ya jikin naki"?
"Jiki Alhamdulillah,"
Murmushi jahad ta É—an saki tana satar kallonta,
  "Na nemeki banganki ba,"
"Ina É—akin aunty azmee ne,"
  Jinjina kai jahad ta ɗanyi"dama saida raina ya bani cewa kina acan,naso nazo,amma dare yayi sosai ga bacci daya fi ƙarfina,"
  Kafin sehrish tace wani abun,Oummansu ta fito daga cikin toilet,fuskarta da hannunta duk lemar ruwan alwalan da tayi,

"Xaman me kuke yi ne"?tayi tambayar tana kallonsu,miƙewa sehrish tayi,Jahad kuma ta sanya hannu tare da janye bargon jikin hosana,kafin ta ɗan bubbuga hannunta"Get up hosana,Time ɗin sallah yayi,wai bazaki tashi ba "
Chapter 191 · 0% Book details