Sashe 189
Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ki fadamun me nayi Maki da har kike guduna?Na ta6a cutar dake ne hakanan,bayan wannan abunda ya faru"?yayi maganar muryarshi tamkar zai fashe da kuka,yayin da idanuwanshi ke akan fuskarta,kwata kwata babu annuri akan fuskar Sehrish,ta canza tamkar ba ita ba,
"Idan har akwai abunda nake yi maki,wanda bakyaso ki fadamun zan daina,"cikin lalama yake lallashinta,
Ammi dai ta kasa kunne tana sauraron kowannansu,tana jira su gama,Ta zartar da hukuncin daya dace,
Fashewa Sehrish tayi da matsanancin kuka,tamkar ranta zai fita,cikin shessheƙar kuka take cewa"Don Allah A sanya ya sake ni,shi dakanshi yace duk hukuncin dana yanke mashi zai kar6a hannu bibbiyu don haka inaso Ya bani takardar Sakina,kuma bayan aurenmu saida ya bani damar cewar Zan iya kula duk wanda nakeso koda Namiji ne shi bai damu ba,don haka Ni Ina da wanda nakeso Yanzu haka ......... ."
 Gaban Sgr ne Ya faɗi rasss!lokaci guda yabi ya susuce ya dabarbarce,jikinshi sai kerma yakeyi,Zuciyarshi sai faman tafarfasa take yi,Ya harzuƙa sosai but he's trying to control his anger,don ta fara wuce gona da iri,
Kowa na wurin sai da yayi mamakin kalaman sehrish basu ta6a tsammanin zata iya furta su ba,gaba É—aya ammi ta karancesu tsaf,
Gyaran Murya ta É—anyi,hankalinsu ya dawo kanta,yayin da idanuwanta ke akan Sehrish dake ta faman matsar kwalla,
 "Share hawayenki,kukan ya isa haka!Ae dama nace zanyi maku adalci atsakaninku,To ki kwantar da hankalinki,"jin wannan maganar yasa Sehrish taji hankalinta ya kwanta,
 "Amma inaso ki natsu kiyi tunani kafin ki yanke hukunci,don na lura kina acikin fushi sosai,kada kiyi irin kuskuren da iyayenku suka yi na tursasa mashi akan Ya sake ki,wanda silar hakan ne yasa shi rafayet din Ya huce akanki,daga baya akazo ana danasani,to banaso kiyi danasani daga baya jikata,Tabbas Rafayet bai kyauta maki ba,amma inaso ki sani saboda son da yake yi maki ne duk yajawo hakan,saboda bayaso a rabashi dake,yayi tunanin hakan shi zaisa abarmashi ke sai dai kash Yayi abu cikin fushi,kuma daga baya yazo yana danasani,sannan kuma karki manta da kanshi ya gyara 6arnar da yayi maki,wanda da ace da mugunta yayi maki zai tafi ya barki ne,Kiyi rai ko ki mutu,Amma saboda yasan bai kyauta ba,Ya tsaya har sai daya ga kin samu Lafiya,Ina faɗa maki wannan ne ba don ina goyan bayanshi ba,Sai don ina guje maki yin danasani,musamman idan ya kasance kinason Shi tun fil,azal,"Ajiyar zuciya ammi ta ɗan sauke bayan takai ƙarshen maganarta,ɗaya bayan ɗaya take kallon fuskokinsu,ɗakin yayi tsit baka jin komai sai shessheƙar kukan Sehrish,
Cigaba da magana tayi a tsanake"zan tambayeki a karo na ƙarshe,Amma inaso Ki fara yin tunani kafin ki bani Amsa,kinaji ko"?
Cikin shessheƙar kuka tace"Eh ammi,"
Ita kanta ammin bason rabasu takeyi ba,don ta fahimci akwai soyayya mai ƙarfi atsakaninsu,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Har yanzu kina akan bakanki na son rabuwa dashi"?cike da fargaba ammi tayi maganar,ba ita ba hatta su Mommy,kowa hankalinshi ya tashi,Sgr kuwa tuni Ya karaya,ya rufe fuskarshi da tafin hannunshi,
Cike da kwarin guiwa tace"Eh,Nidai arabani dashi,"yadda kasan Ya shako wuyanta haka yake ji,takaishi ƙarshe,tuni ciwon kai ya farmasa,
Duk yadda Abusufyan yaso ta É—ago su hada ido don ya dakatar da ita,Amma yarinyar nan ta kafe,taki kallon kowa daga cikinsu,
Jinjina kai ammi tayi"Shikenan,rafayet ina fata kaji abunda tace!tana buƙatar ka sake ta,"Yadda kasan tayi magana da bango haka Sgr yayi masu shiru,baice uffan ba,domin kuwa baya acikin hayyacinsa,Sama sama yake jinsu,
"Amma kuma wani hanzari ba gudu ba,"ammi ce tayi maganar tana kallon Sehrish,
 "Har yanzu da sauran jikinki kuma shine likitan dake dubaki,ni aganina,me zai hana ki bari kiji sauƙi sosai sai ya sake ki?Ni nayi maki alƙawarin da zarar kinji sauƙi zansa ya sake ki,"
Tunda Ammi taso ma magana,Abba ya fara sakin murmushin gefen fuska,don ya gane wayau ammi takeso tayi mata,don tasan kafin lokacin zaiyi wuya in bata sauko daga fushin da take yi dashi ba,
 "Ki amince Sehrish,kinga baki da lafiya kuma shi kaɗaine zai iya dubaki acikin gidan nan,shi yasan kan abun,kuma kinga da igiyar auran nan kawai zai iya yin hakan,"Hajiya Azeema ce ke yi mata raɗa acikin kunnanta,shiru sehrish tayi da alama tana yanke shawara da zuciyarta ne,ita aganinta za'a iya ɗauko wani likitan yaci gaba da dubata ba dole sai shi ba,tana kokarin bude baki tayi magana Hajiya azeema tayi saurin cewa"Ta amince,"
 Ammi tace"Nafiso naji ta bakinta,"
 Nauyin Hajiya azeema da take ji ne yasa tace"Na amince,"saboda bata son ta ƙaryatata," dama da biyu Hajiya Azeema tayi mata hakan,don tasan Sehrish bazata Iya musawa ba,in har tasa baki,"
 Ajiyar Zuciya kowannansu ya sauke,har Lokacin Sgr bai ɗago ya kallesu ba,
"Shikenan magana ta ƙare,Zamu zuba ido har Allah ya baki Lafiya,daga nan ni kuma zan Kar6ar maki takardar sakinki,"tana kai ƙarshen maganar,Tace ma azeema"Ki taimaka mata,ta koma ɗaki,"
 "To ammi,"ta amsa tare da ruko sehrish ta miƙe daƙyar,suka fuce daga dakin,
Bayan fitarsu ammi taci gaba da magana"kar kuga laifinta,tana cikin wani hali ne wanda dama karshe hakance zata faru,anma ci sa'a da ta dawo hayyacinta don mafi akasarin wadanda irin hakan ya faru dasu sukan fita hayyacinsu tsawon lokaci wasu ma ta6in hankaline ke samunsu,yayin da wasu kuma daga haka sai su fara tsoron maza....." dan dakatawa tayi sakamakon shigowa da Hajiya Azeema tayi,ta koma kan hannun kujeran data tashi ta zauna,
Ammin ta dasa"kamar ita dae,na tabbatar bata rasa son shi kawae abunda yayi mata ne yasa take tsoron cigaba da zama dashi",
"Tabbas Ammi tana son shi wllh don ni shaida ce baki na da nata munyi maganar lokacin da aka daura masu Auren,wanda hakanne ma yasa lokacin da ta gano dalilin da yasa ya auretan ba don yana sonta bane don tayi masa aikine yasa ta shiga wani hali har ta kulle kanta acikin Toilet"Hajiya Azeema ce tayi maganar,gaba daya suka shiga jinjina kai,
Kallon Sgr Ammi tayi wanda har lokacin tafin hannunshi na rufe da fuskarshi,sai dae duk abunda suke fada yana jinsu,
"Rafayet",Ammi ta kira sunanshi,a hankali ya zame tafin hannunshi ya kalleta, blue eyes dinshi sun canja launi don ba karamin sarawa kanshi ke mashi ba,
"Matarka tana son ka tunda ga tabbaci nan daga Azeema,muma kuma ba son rabuwarku muke ba,don haka inason kayi amfani da wannan damar dana samar maka wurin ganin ka shawo kanta daga dokin zuciyar da ta hau,kaima kuma inason na kara jan hankalinka,ba komae ne karfi ke samarwa Mutun ba,wani abun in kace zaka sa mashi karfi to kuwa zaka rasa shine gaba daya kamar dae aurenka yanzu,inason kabi komae a hankali in sha Allah komae zai zama daidai,sannan wannan bakar zuciyar dole sai ka rinka yin yaki da ita,ka rinka neman tsari daga wurin Allah akan ya rabaka da sharrinta don in dae zaka rinka yanke hukunci cikin fushi to wllh ka dinga yin dana sani kenan,A duk lokacin da wani abu ya 6ata ma rae kayi kokarin ganin ka daidaita natsuwarka kafin ka yanke hukunci,Yadda kake yin nasara Akan aikinka haka nikeson ka rinka yin nasara akan zuciyarka aduk lokacin da ta taso maka kaji?" dan jinjina mata kae yayi,
Cike da zolaya ta juya ta kalli su Abba tace"Yakamata a siyo mashi buta ya rinka yin alwala da ita,yana rage sauran ruwan yana sha ya daina yi a famfo ko Allah ya sanyaya mashi ita"gaba daya sukae Murmushi,shi dai still yayi bai tanka ba,
"Ko akwae mai magana?" gaba daya suka ce a'a,kallon Marshal Omar tayi"sai ka rufe mana da Addu'a"gaba daya suka daga hannu harda Mommy,Omar ya shiga jero Addu'oi daga bisani suka shafa.
Daga haka Ammi ta basu Iznin Tafiya,
ƙoƙarin miƙewa Sgr yayi wani irin Jiri ne ya soma ƙoƙarin kwasarshi,da sauri Omar ya ruƙe shi,ya taimaka mashi har suka fita daga ɗakin,
A bedroom É—inshi Omar ya shigar dashi,Kaitsaye ya faÉ—a yaraaaf saman gadon,jiki babu kwari,yadda kasan baya numfashi,hawa saman gadon Omar yayi,Yasa hannu ya cire mashi rigar jikinshi,ganin yadda zufa ke tsastsafowa daga jikinshi,
"Bro,Are u not feeling well"?yayi tambayar yana kallonshi,ya runtse idanuwanshi sai faman Cizon pink lip ɗinsa yake yi,daƙyar ya iyacewa"Omar,zuciyata babu daɗi,yarinyar can ta 6ata mun rai,wai har ni zatace bataso?bata ra'ayin zama dani?wacece ita?mata nawa suke neman wannan damar a wurina"?......daƙyar sautin muryarshi
ke fita,da wani irin hucin zafin zazza6in jikinshi,
murmushin gefen fuska Omar ya saki,wato har yanzu rafayet bai gane cewa Ya afka tarkon so ba,babban takaicinshi Yadda Sehrish ta furta bata ra'ayinshi agaban kowa,ba ƙaramin ƙona mashi rai tayi ba,
"Am sorry bro,just forget about her,idan ka shareta zata dawo maka ne"
 A hasale yace"tafita daga cikin zuciyata mana,"
 Ƙiris ya rage Omar ya fashe da dariya,Aranshi yace"Kaine ka sanyata acikin zuciyarka malam,"
  Miƙewa yayi daga kwancen da yake,Ya sauko ƙafafunshi ƙasa,sumar kanshi duk ta rufe mashi gefe da gefen fuskarshi,
   "Zan shiga toilet,pls before na fito,ina bukatar magani ciwon kai,"yana kai ƙarshen maganar,ya sauko daga saman gadon Ya nufi toilet ya shige,kafin ya fito Omar ya ajiye mashi medicine ɗin asaman side drawer tare robar ruwa,
Sehrish kuwa,bayan mommy azeema takaita ɗakinsu,Saman gadon ta haye fuskarta sharkaf da hawaye,taso ace Sgr ya sake ta,don yanzu batason duk wani abu da zai alaƙantata dashi,ta wani 6angaren kuma taji daɗin hukuncin da Ammi ta yanke,koba komai tayi mata alƙawarin zata amsar mata takardar sakinta,
"Idan har akwai abunda nake yi maki,wanda bakyaso ki fadamun zan daina,"cikin lalama yake lallashinta,
Ammi dai ta kasa kunne tana sauraron kowannansu,tana jira su gama,Ta zartar da hukuncin daya dace,
Fashewa Sehrish tayi da matsanancin kuka,tamkar ranta zai fita,cikin shessheƙar kuka take cewa"Don Allah A sanya ya sake ni,shi dakanshi yace duk hukuncin dana yanke mashi zai kar6a hannu bibbiyu don haka inaso Ya bani takardar Sakina,kuma bayan aurenmu saida ya bani damar cewar Zan iya kula duk wanda nakeso koda Namiji ne shi bai damu ba,don haka Ni Ina da wanda nakeso Yanzu haka ......... ."
 Gaban Sgr ne Ya faɗi rasss!lokaci guda yabi ya susuce ya dabarbarce,jikinshi sai kerma yakeyi,Zuciyarshi sai faman tafarfasa take yi,Ya harzuƙa sosai but he's trying to control his anger,don ta fara wuce gona da iri,
Kowa na wurin sai da yayi mamakin kalaman sehrish basu ta6a tsammanin zata iya furta su ba,gaba É—aya ammi ta karancesu tsaf,
Gyaran Murya ta É—anyi,hankalinsu ya dawo kanta,yayin da idanuwanta ke akan Sehrish dake ta faman matsar kwalla,
 "Share hawayenki,kukan ya isa haka!Ae dama nace zanyi maku adalci atsakaninku,To ki kwantar da hankalinki,"jin wannan maganar yasa Sehrish taji hankalinta ya kwanta,
 "Amma inaso ki natsu kiyi tunani kafin ki yanke hukunci,don na lura kina acikin fushi sosai,kada kiyi irin kuskuren da iyayenku suka yi na tursasa mashi akan Ya sake ki,wanda silar hakan ne yasa shi rafayet din Ya huce akanki,daga baya akazo ana danasani,to banaso kiyi danasani daga baya jikata,Tabbas Rafayet bai kyauta maki ba,amma inaso ki sani saboda son da yake yi maki ne duk yajawo hakan,saboda bayaso a rabashi dake,yayi tunanin hakan shi zaisa abarmashi ke sai dai kash Yayi abu cikin fushi,kuma daga baya yazo yana danasani,sannan kuma karki manta da kanshi ya gyara 6arnar da yayi maki,wanda da ace da mugunta yayi maki zai tafi ya barki ne,Kiyi rai ko ki mutu,Amma saboda yasan bai kyauta ba,Ya tsaya har sai daya ga kin samu Lafiya,Ina faɗa maki wannan ne ba don ina goyan bayanshi ba,Sai don ina guje maki yin danasani,musamman idan ya kasance kinason Shi tun fil,azal,"Ajiyar zuciya ammi ta ɗan sauke bayan takai ƙarshen maganarta,ɗaya bayan ɗaya take kallon fuskokinsu,ɗakin yayi tsit baka jin komai sai shessheƙar kukan Sehrish,
Cigaba da magana tayi a tsanake"zan tambayeki a karo na ƙarshe,Amma inaso Ki fara yin tunani kafin ki bani Amsa,kinaji ko"?
Cikin shessheƙar kuka tace"Eh ammi,"
Ita kanta ammin bason rabasu takeyi ba,don ta fahimci akwai soyayya mai ƙarfi atsakaninsu,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Har yanzu kina akan bakanki na son rabuwa dashi"?cike da fargaba ammi tayi maganar,ba ita ba hatta su Mommy,kowa hankalinshi ya tashi,Sgr kuwa tuni Ya karaya,ya rufe fuskarshi da tafin hannunshi,
Cike da kwarin guiwa tace"Eh,Nidai arabani dashi,"yadda kasan Ya shako wuyanta haka yake ji,takaishi ƙarshe,tuni ciwon kai ya farmasa,
Duk yadda Abusufyan yaso ta É—ago su hada ido don ya dakatar da ita,Amma yarinyar nan ta kafe,taki kallon kowa daga cikinsu,
Jinjina kai ammi tayi"Shikenan,rafayet ina fata kaji abunda tace!tana buƙatar ka sake ta,"Yadda kasan tayi magana da bango haka Sgr yayi masu shiru,baice uffan ba,domin kuwa baya acikin hayyacinsa,Sama sama yake jinsu,
"Amma kuma wani hanzari ba gudu ba,"ammi ce tayi maganar tana kallon Sehrish,
 "Har yanzu da sauran jikinki kuma shine likitan dake dubaki,ni aganina,me zai hana ki bari kiji sauƙi sosai sai ya sake ki?Ni nayi maki alƙawarin da zarar kinji sauƙi zansa ya sake ki,"
Tunda Ammi taso ma magana,Abba ya fara sakin murmushin gefen fuska,don ya gane wayau ammi takeso tayi mata,don tasan kafin lokacin zaiyi wuya in bata sauko daga fushin da take yi dashi ba,
 "Ki amince Sehrish,kinga baki da lafiya kuma shi kaɗaine zai iya dubaki acikin gidan nan,shi yasan kan abun,kuma kinga da igiyar auran nan kawai zai iya yin hakan,"Hajiya Azeema ce ke yi mata raɗa acikin kunnanta,shiru sehrish tayi da alama tana yanke shawara da zuciyarta ne,ita aganinta za'a iya ɗauko wani likitan yaci gaba da dubata ba dole sai shi ba,tana kokarin bude baki tayi magana Hajiya azeema tayi saurin cewa"Ta amince,"
 Ammi tace"Nafiso naji ta bakinta,"
 Nauyin Hajiya azeema da take ji ne yasa tace"Na amince,"saboda bata son ta ƙaryatata," dama da biyu Hajiya Azeema tayi mata hakan,don tasan Sehrish bazata Iya musawa ba,in har tasa baki,"
 Ajiyar Zuciya kowannansu ya sauke,har Lokacin Sgr bai ɗago ya kallesu ba,
"Shikenan magana ta ƙare,Zamu zuba ido har Allah ya baki Lafiya,daga nan ni kuma zan Kar6ar maki takardar sakinki,"tana kai ƙarshen maganar,Tace ma azeema"Ki taimaka mata,ta koma ɗaki,"
 "To ammi,"ta amsa tare da ruko sehrish ta miƙe daƙyar,suka fuce daga dakin,
Bayan fitarsu ammi taci gaba da magana"kar kuga laifinta,tana cikin wani hali ne wanda dama karshe hakance zata faru,anma ci sa'a da ta dawo hayyacinta don mafi akasarin wadanda irin hakan ya faru dasu sukan fita hayyacinsu tsawon lokaci wasu ma ta6in hankaline ke samunsu,yayin da wasu kuma daga haka sai su fara tsoron maza....." dan dakatawa tayi sakamakon shigowa da Hajiya Azeema tayi,ta koma kan hannun kujeran data tashi ta zauna,
Ammin ta dasa"kamar ita dae,na tabbatar bata rasa son shi kawae abunda yayi mata ne yasa take tsoron cigaba da zama dashi",
"Tabbas Ammi tana son shi wllh don ni shaida ce baki na da nata munyi maganar lokacin da aka daura masu Auren,wanda hakanne ma yasa lokacin da ta gano dalilin da yasa ya auretan ba don yana sonta bane don tayi masa aikine yasa ta shiga wani hali har ta kulle kanta acikin Toilet"Hajiya Azeema ce tayi maganar,gaba daya suka shiga jinjina kai,
Kallon Sgr Ammi tayi wanda har lokacin tafin hannunshi na rufe da fuskarshi,sai dae duk abunda suke fada yana jinsu,
"Rafayet",Ammi ta kira sunanshi,a hankali ya zame tafin hannunshi ya kalleta, blue eyes dinshi sun canja launi don ba karamin sarawa kanshi ke mashi ba,
"Matarka tana son ka tunda ga tabbaci nan daga Azeema,muma kuma ba son rabuwarku muke ba,don haka inason kayi amfani da wannan damar dana samar maka wurin ganin ka shawo kanta daga dokin zuciyar da ta hau,kaima kuma inason na kara jan hankalinka,ba komae ne karfi ke samarwa Mutun ba,wani abun in kace zaka sa mashi karfi to kuwa zaka rasa shine gaba daya kamar dae aurenka yanzu,inason kabi komae a hankali in sha Allah komae zai zama daidai,sannan wannan bakar zuciyar dole sai ka rinka yin yaki da ita,ka rinka neman tsari daga wurin Allah akan ya rabaka da sharrinta don in dae zaka rinka yanke hukunci cikin fushi to wllh ka dinga yin dana sani kenan,A duk lokacin da wani abu ya 6ata ma rae kayi kokarin ganin ka daidaita natsuwarka kafin ka yanke hukunci,Yadda kake yin nasara Akan aikinka haka nikeson ka rinka yin nasara akan zuciyarka aduk lokacin da ta taso maka kaji?" dan jinjina mata kae yayi,
Cike da zolaya ta juya ta kalli su Abba tace"Yakamata a siyo mashi buta ya rinka yin alwala da ita,yana rage sauran ruwan yana sha ya daina yi a famfo ko Allah ya sanyaya mashi ita"gaba daya sukae Murmushi,shi dai still yayi bai tanka ba,
"Ko akwae mai magana?" gaba daya suka ce a'a,kallon Marshal Omar tayi"sai ka rufe mana da Addu'a"gaba daya suka daga hannu harda Mommy,Omar ya shiga jero Addu'oi daga bisani suka shafa.
Daga haka Ammi ta basu Iznin Tafiya,
ƙoƙarin miƙewa Sgr yayi wani irin Jiri ne ya soma ƙoƙarin kwasarshi,da sauri Omar ya ruƙe shi,ya taimaka mashi har suka fita daga ɗakin,
A bedroom É—inshi Omar ya shigar dashi,Kaitsaye ya faÉ—a yaraaaf saman gadon,jiki babu kwari,yadda kasan baya numfashi,hawa saman gadon Omar yayi,Yasa hannu ya cire mashi rigar jikinshi,ganin yadda zufa ke tsastsafowa daga jikinshi,
"Bro,Are u not feeling well"?yayi tambayar yana kallonshi,ya runtse idanuwanshi sai faman Cizon pink lip ɗinsa yake yi,daƙyar ya iyacewa"Omar,zuciyata babu daɗi,yarinyar can ta 6ata mun rai,wai har ni zatace bataso?bata ra'ayin zama dani?wacece ita?mata nawa suke neman wannan damar a wurina"?......daƙyar sautin muryarshi
ke fita,da wani irin hucin zafin zazza6in jikinshi,
murmushin gefen fuska Omar ya saki,wato har yanzu rafayet bai gane cewa Ya afka tarkon so ba,babban takaicinshi Yadda Sehrish ta furta bata ra'ayinshi agaban kowa,ba ƙaramin ƙona mashi rai tayi ba,
"Am sorry bro,just forget about her,idan ka shareta zata dawo maka ne"
 A hasale yace"tafita daga cikin zuciyata mana,"
 Ƙiris ya rage Omar ya fashe da dariya,Aranshi yace"Kaine ka sanyata acikin zuciyarka malam,"
  Miƙewa yayi daga kwancen da yake,Ya sauko ƙafafunshi ƙasa,sumar kanshi duk ta rufe mashi gefe da gefen fuskarshi,
   "Zan shiga toilet,pls before na fito,ina bukatar magani ciwon kai,"yana kai ƙarshen maganar,ya sauko daga saman gadon Ya nufi toilet ya shige,kafin ya fito Omar ya ajiye mashi medicine ɗin asaman side drawer tare robar ruwa,
Sehrish kuwa,bayan mommy azeema takaita ɗakinsu,Saman gadon ta haye fuskarta sharkaf da hawaye,taso ace Sgr ya sake ta,don yanzu batason duk wani abu da zai alaƙantata dashi,ta wani 6angaren kuma taji daɗin hukuncin da Ammi ta yanke,koba komai tayi mata alƙawarin zata amsar mata takardar sakinta,