← Book details Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 121 OF 212

Sashe 121

Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Lokacin da suka sauko down,Su kanal Yousouf na ganinsu kowa ya miƙe fuskar nan ɗauke da farin ciki,Yayin da su kuma kowannansu ya dabarbarce,
Daƙyar suke gaisawa da ƴan uwan nasu,kowa ya lura da yanayinsu shiru kawai su kayi,Su fawan sai tambayar Junaid suke yi,Yana ina?basu ganshi ba,amsa daya suke basu ta yana a cikin toilet yana wanka,Duk wanda yaje ɗakin Junaid yaji sautin saukar ruwa daga cikin toilet,sai yayi tunanin cewa wanka yake yi,Ashe fanfo ne Aka bari a kunne ba'a kashe ba,
   Daƙyar suka samu kowa ya haƙura da ganin junaid,Omar yace su wuce ɗakunansu kowa yaje ya huta,an kwaso gajiya,
  "Nifa ban yarda dasu babban yaya ba,Shi da ya Omar akwai wani abu da suke 6oye mana Allah,"Acewar Jahan,
A yayin da suke shiga bedroom É—insu,
  Ayaan yace"nikaina na lura da hakan,musamman faces ɗinsu,kamar sunsha kuka Allah,Gaskiya hankalina bazai kwanta ba,sai naga junaid,ni ban yarda wanka yake yi acikin toilet ba,"
  Jahan yace"mu bari mu huta,Zuwa dare sai muje ɗakin nashi,nasan lokacin idan ma wankan ne ya gama,"
  Ƙarasa shiga cikin ɗakin sukayi,kowa ya shiga rage kayan jikinshi,Jahan ne ya fara shiga waka,Ayaan ya zauna gefen gadon yana jiranshi ya fito shima ya shiga wankan,
   A can falo kuwa,Mommynsu ta tsare Sgr da Omar,Tasa su gaba tayi tana binsu da kallo one by one,dama bakowa Sgr yafi ji ba fa ce Mommynsu,tana da wuyar sha'ani,
  "Mommy,"Sgr ne ya ambaci sunanta,
bata amsa mashi sunan nata daya kira ba,sai cewa tayi"you didn't answer my question,It seems like you are hidding something for us!Rafayet where is junaid!kada kuyi mun ƙarya nasan ba halinku ba ne,just ku faɗamun Gaskiyar abunda ya faru,"
  Murya na rawa Omar yace“Am..mommy,Junaid fa yana a toilet yana wanka zai fito ne...m"daƙyar ya ƙarasa maganar ganin irin kallon da take yi mashi,kallon tuhuma,kallon ban yarda dakai ba
"Wai taya za ku ce mun junaid yana wanka?Nifa ba ƙaramar yarinya bace,balle kuce zakuyi mun wayau,tun daga kan fuskarku na gane cewa akwai wani abu daya faru dashi...."
  Saussauta muryarta tayi,sannan taci gaba da magana"pls idan wani abu ne ya faru da Romeo ɗina ku sanar dani,i will accept it,"yadda tayi maganar yasa su kaji jikinsu ya ƙara mutuwa,
  "Am listening to u guys,ku faɗamun meya faru dashi ya mutu ko"?
  Gabansu ne ya faɗi rass!da sauri Sgr ya ruƙo hannunta muryarshi na kerma yace"Mommy dan Allah kiyi haƙuri,ki rufa mana asiri,I will explain to u mu shiga daga cikin bedroom ɗin..."
  "Rafayet,meyasa zaka sanar da ita"?Omar ne yayi maganar fuskarshi a yamutse,
  "To ya kakeso nayi Omar,Mommy bazata ta6a yarda ba,kwara kawai mu faɗa mata gaskiyar abunda ya faru,Ka wuce wurin Daddy,ni zanji da Mommy,'
  Ya ƙarasa maganar tare da jan hannunta,Suka wuce upstairs bedroom ɗinshi,
  Ajiyar zuciya Omar ya sauke,Ya jima atsaye yana tunanin Yadda zasu ƙare da Abbansu,tsoranshi kada farat ɗaya zuciyarshi ta buga idan yaji cewa Anyi garkuwa da junaid kamar yadda suka tsara,
  "Omar,lafiya kuwa,"firgit ya ɗanyi tare da kai idanuwanshi wurinta,Azmee ta nufo shi,Ganinshi a tsaye kamar akwai damuwa atattare dashi,
  Dakyar ya ƙaƙaro murmushin yaƙe yace"bakomai,"
    "Omar,dama inaso na tambayeka ne,Wai ina junaid ne?tun jiya da suka fita shi da jahad shiru har yau basu dawo ba,nashiga damuwa sosai akan rashin ganinsu,har cewa yayi idan suka je shan ice cream zaiyi min tsaraba," ta ƙarasa maganar tana kallonshi,
  "Aunty Azmee,bazan iya 6oye maki ba,Junaid da jahad anyi kidnapping ɗinsu...."jin wannan maganar yasa Azmee ta dafe ƙirjinta da ƙarfi,idanuwanta suka firfito waje,hankalinta yayi mugun tashi,
  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"kusan sau biyar tana maimata kalmar,
   siraran hawaye ne suka soma saukowa saman cheeks ɗinta,ji tayi tamkar bazata iya ɗaga ƙafafunta ba,saboda nauyin da sukayi mata,
  "Junaid da jahad suna buƙatar addu'armu Azmee,"acewar Omar,
  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Nashiga uku!Yanzu junaid da jahad aka ɗauke mana...."
Katse ta Omar yayi'pls Aunty azmee,ki daina É—aga sautin muryarki,na faÉ—a maki ne don ki taimaka mana,Wurin kwantar da hankalin sauran mutanen gidan nan,Mun shiga damuwa sosai,saboda gudun halin da zasu shiga,musamman mahaifinmu...."
  Cikin shessheƙar kuka tace"Ya Allah ga bayinka nan!ka tsare manasu a duk inda suke,Ya Allah ka ku6utar dasu daga hannun azzaluman da suka yi garkuwa dasu,wannan wata irin masifa ce......"kuka ne yaci ƙarfinta,da gudun gaske ta juya tare da tunkarar kitchen,zama tayi ta dingi kuka kamar ranta zai fita,gani take yi kamar zasu rasa su ne,Ta ƙwallafa rai akan junaid,tana jinshi tamkar ɗan cikinta saboda ta shayar dashi,baiwar Allah,
  Jiki asanyaye Omar ya wuce bedroom ɗin Abbansu,tsaye ya same shi har ya zura kayan bacci ajikinshi,ta cikin mirror ya hango Omar,juyowa yayi fuskar shi ɗauke da murmushi yace"halan junaid ya fito daga wankan ne"?yayi tunanin abunda ya kawo shi ne,
  "Abba,me kake buƙata na kawo maka"ya tambaye shi ne don ya kawar mashi da tunanin Junaid aranshi
Murmushi Abba yayi tare da cewa"Sannu Azmee,Yau kaine ka kar6i aikinta kenan"?
  Duk da halin daya ke ciki na fargaba sai da ya ɗan murmusa,jin abunda abban yace,
   "No,kawai inaso na baka kyakkyawar kulawa ne saboda nayi kewarka,ka fara faɗamun abunda kakeso sai in kawo maka,"
  Murmushi Abba ya ɗan yi kafin yace"shikenan,junaid nake son gani ka kawo mun shi,idan ma ya fara bacci ka ɗauko mun shi,ina jiranka,"ya ƙarasa maganar tare da samun wuri gefen gadonshi,yana kallon Omar da yayi mashi zuru da ido,
  "Omar,lafiya ka zubamin ido kana kallona'?
  "Babu komai Abba,bari na ɗauko maka junaid ɗin,"yayi maganar tare da juyawa yabar ɗakin,Zaman jiran dawowarshi Abba yayi,sai faman sakin murmushi yake yi,harya ƙosa Omar ya ɗauko mashi Baby Junaid ɗinshi,

A 6angaren Omar yana fita daga bedroom É—in abban nasu,kaitsaye kitchen ya wuce,Anan ya samu azmee zaune saman kujera tana ta matsar kwalla,
"haba Aunty azmee,meyasa zakiyi mun haka?Addu'a yakamata kiyi masu akan Allah ya bayyanar mana dasu,kukan da kike yi bazai amfane su ba,"
  Zame hannuwanta tayi daga saman fuskarta,idanuwanta sunyi jawur dasu luhu luhu,
  "Omar,ba zaka gane bane,dole inyi kukan rashin su junaid,ko ka manta shakuwar dake tsakanina dashi ne'?
  Shiru omar yayi yana kallonta,Allah yaso bai sanar da ita gaskiyar abunda ya faru ba,da baisan abunda zai biyo baya ba daga gareta itama,
Lallashinta ya shiga yi har ya samu ta saukko,Tsayawa yayi ta shirya mashi dinner asaman tray,ya kar6a ya wuce É—akin Abbansu,ita kuma ta shiga É—aukar kayan abincin da ta shirya masu tana kaiwa dining,

Lokacin da Omar ya koma bedroom É—in Abbansu,yana shiga ciki Abbansu yaga tray a hannunshi sai ya É—aure fuskarshi tare da cewa"Nifa ba yunwa nace maka inaji ba,Junaid nace ka É—auko mun,"
  Saman table omar ya ajiye tray din tare da samun wuri gefenshi ya zauna,ruƙo hannayenshi yayi tare da sassauta muryarshi
   "Abba pls,kaci abincin ka ƙoshi,idan ka kammala zamuyi magana dakai,"
  Shiru yayi yana kallonshi kamar mai nazarin wani abu yace"Shikenan zuba mun abincin naci,Allah yasa naji alkhairi,"
Serving É—inshi Omar ya soma yi,sosai yaci abincin bayan ya gama da abincin,Omar ya tsiyaya mashi Lemu me sanyi a cup,yasha,
  "Yanzu ina sauraronka,wata maganace zamuyi,"
  "Abba ko zaka ɗan kwanta ne?ina ga kamar hakan zaifi,muna magana inayi maka tausa,"
  Abun ya daurewa Abbansu kai,gyara kwanciyarshi yayi saman gadon sannan yace"ina sauraronka toh,"
  Hawa saman gadon Omar yayi,A hankali ya fara yi mashi massage ɗin kafarsa,
   A tsanake ya soma magana"Abba dama game da junaid ne,nasan ka yarda dani sosai,kuma zaka fahimce ni ne,
  Tunda ya ambaci sunan Junaid,Abba ya miƙe daga zaune da sauri yana kallonshi
  daurewa Omar yayi tare da cigaba da cewa"mun shiga matsananciyar damuwa Abba,idan ka lura da fuskokinmu duk sun sauya saboda tsabar tashin hankalin da muke ciki...."dakatar dashi Abba yayi ta hanyar ɗaga mashi hannu,
   "Ka fito fili ka faɗamun ainihin abunda ke faruwa Omar,sai 6oye 6oye kake yi mun,dama ni tuni sai da raina ya bani cewa wani abu ya faru da junaid,dan Allah ka sanar dani!ina ɗana yake"?hankalinshi atashe yayi maganar,
  Cike da fargaba Omar ya ɗaura da cewa"Abba,junaid yana cikin ƙoshin lafiya,sai dai baya atare damu,Jiya bayan fitarsu shan ice cream tare da jahad,kidnappers su kayi garkuwa dasu,bana so ka tashi hankalinka Abba,Ni nayi maka alƙwarin zan dawo maka da ƴa'ƴanka,cikin ƙoshin lafiya batare da sun samu koda ƙwarzane ajikinsu ba....."duk wannan surutan da Omar keyi baisan cewa Abbansu ya jima da sumewa ba,tunda ya ambaci sunan kidnappers sunyi garkuwa dasu,Bai ƙara sanin inda kanshi yake ba,
  "Abba!"ya ambaci sunanshi,yayin da yake kallon fuskarshi,Hannu yasa tare da dafe goshinshi,Dama saida ranshi ya bashi cewar hakan zata iya faruwa,
  Idanuwanshi ne suka cuccuko da kwalla,kamar ya fasa ihu haka yake ji,ta ko'ina babu sauƙi,dirshan ya zauna saman gadon fuskarshi a yamutse,ya zuba ma Abban nasu ido yana kallonshi,
Chapter 121 · 0% Book details