Sashe 167
Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda na koma É—aki,na kasa runtsawa saboda tunanin Rafayet,Kyawun fuskarshi dana surarshi suka É—ebeni har na Fara kamuwa da sonshi,Maimakon da yayi mun faÉ—a inji haushinshi,Sai ma sonshi da nake kara Yi,na kasa samun natsuwa kullum in naje kai mashi abinci,ban iya kawar da idanuwana daga kallonshi,shi kuwa bai ta6a É—ago da idonshi ya kalleni ba a wannan lokacin balle insa ran zan same shi........."dakatawa ta É—anyi da yin maganar,Yayin da hawaye ke cigaba da wanke fuskarta,
Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,Kallon Sgr kawai take yi,Shi kanshi abun ya ɗaure mashi kai,bai ta6a sanin wannan zancen ba,Mommy kuwa wani irin kallo take binta dashi,
"Daƙyar na samu Sgr ya fara tanka mun in na gaishe shi,Ba ƙaramin daɗi nake ji ba idan na kai mashi abinci yaci,ni kaɗai nayita haukan soyayyata don shi baisan ma inayi ba,A kwana a tashi Ya koma U.s A ranar kamar nayi hauka,bayan tafiyarshi na soma tunanin Me ya kawoni gidan?Me nake jira da ban aiwatar da mummunan ƙudurin daya kawoni ba,Saboda jin daɗin da nake ciki,Na manta cewa ɗaukar fansa ta kawoni gidan,Komai na more rayuwa ina samu,Inci me kyau in sha me kyau in kwana a me kyau,ga Albashin da Abba ke bani harya zarce na wani likitan,ko lokacin bani albashina baiyi ba,Yana yawan dunƙulo kuɗi ya damƙa mun,Yace ga wannan in ina buƙatar wani abu,Insa driver yakaini kasuwa inyi siyayya,Wani irin daɗi nake ji,koba shi ba da yawan lokutta Yusuf Yana bani kuɗi hakanan kyauta yace mun ga wannan Inyi amfani dasu,Ganin irin ƙaunar da suke nuna mun saina fara tunanin kodai in janye batun ɗaukar fansar nan tawa,Tabbas a lokacin na fara tunanin yin tuba in koma Ga Allah,Amma sai Dangina suka taso ni gaba,Musamman Hamma Ghali barazana Ya soma yi mun akan kodai na aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ko kuma zai ɗauki mataki akaina,na tsorata sosai,Saboda mugune shi,nasan shi sarai,kuma shine Shugaban ƙungiyarmu ta matsafa,komai nake Yi acikin gidan nan akan idonshi nake yi,Duk da bamu atare amma Yana da madubin tsafinshi wanda yake kallon duk wani motsina,Ba don naso ba haka naci gaba da bin umarninshi,A lokacin Haroon na soma ƙoƙarin janyowa Jikina,Na nuna mashi cewa ku ba jininshi bane,Ya daina shige maku,Fansa muka zo ɗauka acikinku,Amma sai ya kangaremun,Yace shi bazai yarda a haɗa baki dashi ba,Wurin cutar daku ba,Saboda Abba yana sonshi,kuma Yanayi mashi duk abunda Yake so,Don haka inma naci gaba dayi mashi magana zai tona mun asiri ne,Jin wannan magana ta haroon Yasa na fara tunanin ta yadda zan juye mashi tunaninshi,Don na lura ɗabi'unsa da halayyarsa ba irin ta dangina bace,Duk da dama ina kokwanto akanshi,Banda tabbacin wanene mahaifinshi,Ganin yana nema yafi ƙarfina sai na sanar ma Hamma ghali abunda Haroon Yace,aikuwa tun daga wannan Lokacin da mukayi waya dashi,Ya sanar dani cewa In kawar dakaina akanshi zanga me zai biyo baya,tofa aikoda yace haka,cikin ƴan kwanaki ƙalilan Haroon ya canza,Ya zama mugun ƙarfi da yaji,Wata muguntar ma ba saina sanar dashi ba,dakanshi yake yi,Ga bin mata da bin maza,Shaye shaye duk wani aiki na shaiɗanci Haroon ya iyashi,nikaina banji daɗin Sauyawar Haroon ba,Iya Cuta dai Mun cutar dashi,Duk da bani bace silar jefa shi cikin halin da yake ciki ba,Amma ni mahaifiyarshi ce,dani akayi amfani wurin Canza mashi tunaninshi,su kuma Su twins Rashin kunyar da suke yi mun ne Yasa nayi masu turen shaiɗanin Aljanu ajikinsu,Waɗanda ke sanyasu suna Neman junansu wanda in har basuyi ba,Aljanun nan ke jibgarsu da bulala,........."sosai Azmee ta fashe da kuka,
Gaba É—aya jikinsu yayi sanyi,wasu ma gaza cigaba da tsayuwa suka yi dole suka zauna,
"About Junaid!Ke da Haroon Waye ya shirya Mutuwarshi"?Sgr ne yayi mata tambayar,
Daƙyar ta tsagaita da Yin kukan ta soma kora mashi bayani,
 "Haroon ne Ya shirya mutuwar Junaid,A lokacin Kun fusata shi sosai,dama a ƙule yake daku,saboda bambancin da kuke nuna mashi don ba ahankalinshi yake duk abubuwan da yakeyi ba,Duk da ni naso In kashe Junaid,ko dan in fanshe haushin kisan Mijina da akayi,Nasha Sanya Haroon ya kashe Junaid,Amma sai ya ce mun bazai Iya kashe shi ba,Junaid yana sonshi sosai,Kuma bai aikata mashi laifin da zai kasheshi ba,Har ce mun yakeyi zai iya kashe kowa acikin gidan nan koda kuwa Abbane,Amma banda Junaid,Ni gaskiya aranar bansan maiya ƙona mashi rai ba,Har ya bada Umarnin akashe mashi Junaid,
a ƙa'ida Miyagun dake yi mana aiki,basa Yanke hukunci in ba sun sanar dani ba,Dole sai in ni na basu umarni kaitsaye suke aiwatar da abu,Haroon ya basu Umarni su kashe Junaid su kuma Sun kirani a waya sun sanar dani cewa Haroon Ya basu Umarnin su kashe Junaid,Shin da sanina koba da sani na ba,"!nan take nace masu karsu kuskura su kashe shi,Su san yarda za'ae su ɗauke Junaid daga cikin motar sannan su ƙonata yarda kowa zaiyi tunanin ya mutu,Nayi hakanne saboda banaso Haroon yaji cewa Na hana su bi umarninshi don zai canja wata hanyarne,sannan Kuma Don Junaid Ya zame mun makamin da zan Yaƙe ku dashi,
Ƙarin bayani,
Lokacin da Jahad ta fita daga cikin motar ta tsallaka zata siya masu ice cream,Junaid Ya dinga ƙwala mata kira,Ta dinga juyowa tana kallonshi Yana yi mata bye bye,bayan mai ice cream ɗin ya sallami mutanan dake gabanshi,Yace ma Jahad madam guda nawa za'a baki,Ta juya ta bashi Amsa,A cikin wannan Lokacin kafin Jahad ta lalubo kuɗi acikin jakarta ta miƙa mashi,adai dai lokacin,waɗannan miyagun suka buɗe motar,kafin Junaid ya ankara suka shaƙa mashi cocaine a hancinshi gaba ɗaya ya fita hayyacinshi,janyoshi su kayi daga cikin motar da hanzari suka fitar dashi,wanda ya ɗauki Junaid a kafaɗarshi ya juya dashi ta baya inda suka ajiye motarsu ya tura shi aciki,Shi kuma ɗayan Ya jefa bomb acikin motar,Yana barin wurin,Gingimarin Motar nan Ta shararo da gudu,Dama already sun kira wayarshi yana akan layi suna sanar dashi cewa Babu Yaron acikin motar,Atsiyace Yabi takan motar Junaid Ya rugurguzata,Yana sauka ya antaya da gudun gaske,Nan take Bomb ɗin cikin motar Ya fashe,Dama sun ɗibar mashi adadin mintunan da zai tashi,To masu karatu Kunji yadda akai Junaid Ya tsira,Baya acikin motar lokacin da suka take motar,Ko lokacin da Jahad ke ihu tana kuka,Duk a kunnanshi bawan Allah,Yana acikin motarsu sun rufe shi,Sam baya acikin hayyacinshi sai faman shafa glass ɗin motar yake yi yana kallonta,A haka har suka tashi motar da gudu suka bar wurin bayan sun dauki vedion motar naci da wuta wanda suka tura ma haroon,
Yadda akai Sgr yasan game da abubuwan daya fadi ma haroon kuwa,dama tun farko,ya dawo Nigeria ne da niyyar yin bincike,don Mommynsa tasha fadi masa cewa akwae abubuwan dake faruwa ba daidai ba acikin gidan,kuma ta sanar dashi ita bata yarda da azmee ba,wannan dalilinne yasa yazo da shirinshi,a 6oye ya fara yin bincikenshi ba tare da kowa ya sani ba,ana haka kuma Mommynsu ta kirashi ta sanar dashi game da makudan kudin dasu twins suka bukata awurinta,ta tabbatar mashi akwae abunda yake faruwa dasu wanda suka 6oye don a yadda suka bukaci kudin sam hankalinsu ba'a kwance yake ba,gashi itama ta bukaci sai sun shirya tsakaninta da Junaid wanda tana ganin hakan ba mai yuwuwa bane cikin sauki,amman sai gashi sun aikata hakan duk don ta basu kudin,hakan yasa mata zarginsu,jin hakan yasa Sgr yin amfani da Surveillance Cameras wadanda yasa a wasu bangarori na gidan ba tare da kowa ya sani ba don bai barsu a bayyane ba wasu har a cikin chandeliers(fitilun sama) na parlon gidan aka sa,ta nan yake ganin duk abunda ke faruwa har lokacin dasu twins din suka kaima haroon kudin wanda daga baya yabi ya daukesu,koda ace asirin Azmee bai tonu ba ta hanyar ya Mu'allim ba,Sgr na gab da ganota,atakaice ma kusan ya gane bata da gaskia shiyasa ko lokacin da Abu ta sanar dashi dalilin ciwon Sehrish da kuma inda tasan Azmee yayi murmushin takaici,haka lokacin da Marshal Omar ke lallaba haroon akan ya sanar dasu wanda ke bashi umarni yace Sgr yasan komae,wannan kenan.
Azmee taci gaba da bayani "Tunkafin Afkuwar wannan Lamarin,Akwai sihiri ajikin Junaid,Wanda mukayi mashi turenshi,a duk daren duniya,dunƙulen jini na fita daga hancinshi batare da sanin kowa ba,Saboda bai sanar daku ba,bayan Faruwar Accident ɗin nan ni nasa aka killace mun Junaid,kuma na hana kowa Ya cutar mun dashi,Lokacin da kuka sanar cewa Junaid Anyi kidnapping dinshi,Nayi mamaki sosai,Yarda kuka tsara hakan bayan a iya saninku mutuwa Yayi,Sai kuma nayi tunanin cewa Kun 6oye mutuwar Junaid ne saboda mahaifinku gudun kada ku rasa shi,bakowa ya fara Zargina ba,Sae Sehrish da ta tsinci zoben Junaid a cikin wardrobe ɗina,tundaga nan ta fara sanya mun ido,ni kuma nayi kokarin rikitar da ita har ta fara ƴan gane gane..............."
Tunkan takai ƙarshen Maganar,Omar ya katse ta da cewa"Yanzu ina Junaid Yake,"?yayi tambayar tamkar baisan inda yake ba,
Shuru Azmee Ta É—anyi kafin tace"daga bayan nan Nasa an kaishi gidan Hajiya saratu,ÆŠiyar wan mahaifina wadda ke acikin garin nan,"..
 "Innalallahi wa'inna ilahirraji'un!!" Amrish ce ta ambaci hakan tare da ɗaura hannunta asaman kanta,Tana kuka,
Hankalin kowa Ya koma kanta,Muryarta na kerma ta nuna Azmee da hannunta tana faɗin"Dama ke kikasa aka kaishi gidanmu dan baƙin zalunci?Wacece ke?Ni bansan meya haɗani da ku ba,Wlh duk na tsani kaina,In har abunda nake zargi ya tabbata,wlh saina kashe kaina,"sosai ta fashe da kuka
Tunda Azmee taji hakan nan ta gane cewa wani abu ya faru acan gidan,tabbas Junaid Ya ku6uta daga wurinsu,.
Gyaran murya Ya Mu'allim yayi,hankalinsu ya dawo kanshi,Anan Yake labarta masu duk abunda ya faru kamar yarda Amrish ta sanar dashi,Har zuwa kaishi asibiti da su kayi,
Yana kai ƙarshen maganar,Azeemi tace"Naji daɗi da Junaid ya dawo hannunku,Amrish ke bakowa bace face ɗiyar saratu matar ƙanina Ya Sayyadi,Da saratu dani ƴa'ƴan wa da kanine,Don haka ke jininmu ce gaba da baya,babu yarda zakiyi haka Allah Ya ƙaddaro maki,Ki gode ma Allah da baki ɗaukko irin mugayen ɗabi'un mahaifinki da mahaifiyarki ba wanda hakan ne ma yasa ba'a bayyana maki mahaifin naki ba,"
Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,Kallon Sgr kawai take yi,Shi kanshi abun ya ɗaure mashi kai,bai ta6a sanin wannan zancen ba,Mommy kuwa wani irin kallo take binta dashi,
"Daƙyar na samu Sgr ya fara tanka mun in na gaishe shi,Ba ƙaramin daɗi nake ji ba idan na kai mashi abinci yaci,ni kaɗai nayita haukan soyayyata don shi baisan ma inayi ba,A kwana a tashi Ya koma U.s A ranar kamar nayi hauka,bayan tafiyarshi na soma tunanin Me ya kawoni gidan?Me nake jira da ban aiwatar da mummunan ƙudurin daya kawoni ba,Saboda jin daɗin da nake ciki,Na manta cewa ɗaukar fansa ta kawoni gidan,Komai na more rayuwa ina samu,Inci me kyau in sha me kyau in kwana a me kyau,ga Albashin da Abba ke bani harya zarce na wani likitan,ko lokacin bani albashina baiyi ba,Yana yawan dunƙulo kuɗi ya damƙa mun,Yace ga wannan in ina buƙatar wani abu,Insa driver yakaini kasuwa inyi siyayya,Wani irin daɗi nake ji,koba shi ba da yawan lokutta Yusuf Yana bani kuɗi hakanan kyauta yace mun ga wannan Inyi amfani dasu,Ganin irin ƙaunar da suke nuna mun saina fara tunanin kodai in janye batun ɗaukar fansar nan tawa,Tabbas a lokacin na fara tunanin yin tuba in koma Ga Allah,Amma sai Dangina suka taso ni gaba,Musamman Hamma Ghali barazana Ya soma yi mun akan kodai na aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ko kuma zai ɗauki mataki akaina,na tsorata sosai,Saboda mugune shi,nasan shi sarai,kuma shine Shugaban ƙungiyarmu ta matsafa,komai nake Yi acikin gidan nan akan idonshi nake yi,Duk da bamu atare amma Yana da madubin tsafinshi wanda yake kallon duk wani motsina,Ba don naso ba haka naci gaba da bin umarninshi,A lokacin Haroon na soma ƙoƙarin janyowa Jikina,Na nuna mashi cewa ku ba jininshi bane,Ya daina shige maku,Fansa muka zo ɗauka acikinku,Amma sai ya kangaremun,Yace shi bazai yarda a haɗa baki dashi ba,Wurin cutar daku ba,Saboda Abba yana sonshi,kuma Yanayi mashi duk abunda Yake so,Don haka inma naci gaba dayi mashi magana zai tona mun asiri ne,Jin wannan magana ta haroon Yasa na fara tunanin ta yadda zan juye mashi tunaninshi,Don na lura ɗabi'unsa da halayyarsa ba irin ta dangina bace,Duk da dama ina kokwanto akanshi,Banda tabbacin wanene mahaifinshi,Ganin yana nema yafi ƙarfina sai na sanar ma Hamma ghali abunda Haroon Yace,aikuwa tun daga wannan Lokacin da mukayi waya dashi,Ya sanar dani cewa In kawar dakaina akanshi zanga me zai biyo baya,tofa aikoda yace haka,cikin ƴan kwanaki ƙalilan Haroon ya canza,Ya zama mugun ƙarfi da yaji,Wata muguntar ma ba saina sanar dashi ba,dakanshi yake yi,Ga bin mata da bin maza,Shaye shaye duk wani aiki na shaiɗanci Haroon ya iyashi,nikaina banji daɗin Sauyawar Haroon ba,Iya Cuta dai Mun cutar dashi,Duk da bani bace silar jefa shi cikin halin da yake ciki ba,Amma ni mahaifiyarshi ce,dani akayi amfani wurin Canza mashi tunaninshi,su kuma Su twins Rashin kunyar da suke yi mun ne Yasa nayi masu turen shaiɗanin Aljanu ajikinsu,Waɗanda ke sanyasu suna Neman junansu wanda in har basuyi ba,Aljanun nan ke jibgarsu da bulala,........."sosai Azmee ta fashe da kuka,
Gaba É—aya jikinsu yayi sanyi,wasu ma gaza cigaba da tsayuwa suka yi dole suka zauna,
"About Junaid!Ke da Haroon Waye ya shirya Mutuwarshi"?Sgr ne yayi mata tambayar,
Daƙyar ta tsagaita da Yin kukan ta soma kora mashi bayani,
 "Haroon ne Ya shirya mutuwar Junaid,A lokacin Kun fusata shi sosai,dama a ƙule yake daku,saboda bambancin da kuke nuna mashi don ba ahankalinshi yake duk abubuwan da yakeyi ba,Duk da ni naso In kashe Junaid,ko dan in fanshe haushin kisan Mijina da akayi,Nasha Sanya Haroon ya kashe Junaid,Amma sai ya ce mun bazai Iya kashe shi ba,Junaid yana sonshi sosai,Kuma bai aikata mashi laifin da zai kasheshi ba,Har ce mun yakeyi zai iya kashe kowa acikin gidan nan koda kuwa Abbane,Amma banda Junaid,Ni gaskiya aranar bansan maiya ƙona mashi rai ba,Har ya bada Umarnin akashe mashi Junaid,
a ƙa'ida Miyagun dake yi mana aiki,basa Yanke hukunci in ba sun sanar dani ba,Dole sai in ni na basu umarni kaitsaye suke aiwatar da abu,Haroon ya basu Umarni su kashe Junaid su kuma Sun kirani a waya sun sanar dani cewa Haroon Ya basu Umarnin su kashe Junaid,Shin da sanina koba da sani na ba,"!nan take nace masu karsu kuskura su kashe shi,Su san yarda za'ae su ɗauke Junaid daga cikin motar sannan su ƙonata yarda kowa zaiyi tunanin ya mutu,Nayi hakanne saboda banaso Haroon yaji cewa Na hana su bi umarninshi don zai canja wata hanyarne,sannan Kuma Don Junaid Ya zame mun makamin da zan Yaƙe ku dashi,
Ƙarin bayani,
Lokacin da Jahad ta fita daga cikin motar ta tsallaka zata siya masu ice cream,Junaid Ya dinga ƙwala mata kira,Ta dinga juyowa tana kallonshi Yana yi mata bye bye,bayan mai ice cream ɗin ya sallami mutanan dake gabanshi,Yace ma Jahad madam guda nawa za'a baki,Ta juya ta bashi Amsa,A cikin wannan Lokacin kafin Jahad ta lalubo kuɗi acikin jakarta ta miƙa mashi,adai dai lokacin,waɗannan miyagun suka buɗe motar,kafin Junaid ya ankara suka shaƙa mashi cocaine a hancinshi gaba ɗaya ya fita hayyacinshi,janyoshi su kayi daga cikin motar da hanzari suka fitar dashi,wanda ya ɗauki Junaid a kafaɗarshi ya juya dashi ta baya inda suka ajiye motarsu ya tura shi aciki,Shi kuma ɗayan Ya jefa bomb acikin motar,Yana barin wurin,Gingimarin Motar nan Ta shararo da gudu,Dama already sun kira wayarshi yana akan layi suna sanar dashi cewa Babu Yaron acikin motar,Atsiyace Yabi takan motar Junaid Ya rugurguzata,Yana sauka ya antaya da gudun gaske,Nan take Bomb ɗin cikin motar Ya fashe,Dama sun ɗibar mashi adadin mintunan da zai tashi,To masu karatu Kunji yadda akai Junaid Ya tsira,Baya acikin motar lokacin da suka take motar,Ko lokacin da Jahad ke ihu tana kuka,Duk a kunnanshi bawan Allah,Yana acikin motarsu sun rufe shi,Sam baya acikin hayyacinshi sai faman shafa glass ɗin motar yake yi yana kallonta,A haka har suka tashi motar da gudu suka bar wurin bayan sun dauki vedion motar naci da wuta wanda suka tura ma haroon,
Yadda akai Sgr yasan game da abubuwan daya fadi ma haroon kuwa,dama tun farko,ya dawo Nigeria ne da niyyar yin bincike,don Mommynsa tasha fadi masa cewa akwae abubuwan dake faruwa ba daidai ba acikin gidan,kuma ta sanar dashi ita bata yarda da azmee ba,wannan dalilinne yasa yazo da shirinshi,a 6oye ya fara yin bincikenshi ba tare da kowa ya sani ba,ana haka kuma Mommynsu ta kirashi ta sanar dashi game da makudan kudin dasu twins suka bukata awurinta,ta tabbatar mashi akwae abunda yake faruwa dasu wanda suka 6oye don a yadda suka bukaci kudin sam hankalinsu ba'a kwance yake ba,gashi itama ta bukaci sai sun shirya tsakaninta da Junaid wanda tana ganin hakan ba mai yuwuwa bane cikin sauki,amman sai gashi sun aikata hakan duk don ta basu kudin,hakan yasa mata zarginsu,jin hakan yasa Sgr yin amfani da Surveillance Cameras wadanda yasa a wasu bangarori na gidan ba tare da kowa ya sani ba don bai barsu a bayyane ba wasu har a cikin chandeliers(fitilun sama) na parlon gidan aka sa,ta nan yake ganin duk abunda ke faruwa har lokacin dasu twins din suka kaima haroon kudin wanda daga baya yabi ya daukesu,koda ace asirin Azmee bai tonu ba ta hanyar ya Mu'allim ba,Sgr na gab da ganota,atakaice ma kusan ya gane bata da gaskia shiyasa ko lokacin da Abu ta sanar dashi dalilin ciwon Sehrish da kuma inda tasan Azmee yayi murmushin takaici,haka lokacin da Marshal Omar ke lallaba haroon akan ya sanar dasu wanda ke bashi umarni yace Sgr yasan komae,wannan kenan.
Azmee taci gaba da bayani "Tunkafin Afkuwar wannan Lamarin,Akwai sihiri ajikin Junaid,Wanda mukayi mashi turenshi,a duk daren duniya,dunƙulen jini na fita daga hancinshi batare da sanin kowa ba,Saboda bai sanar daku ba,bayan Faruwar Accident ɗin nan ni nasa aka killace mun Junaid,kuma na hana kowa Ya cutar mun dashi,Lokacin da kuka sanar cewa Junaid Anyi kidnapping dinshi,Nayi mamaki sosai,Yarda kuka tsara hakan bayan a iya saninku mutuwa Yayi,Sai kuma nayi tunanin cewa Kun 6oye mutuwar Junaid ne saboda mahaifinku gudun kada ku rasa shi,bakowa ya fara Zargina ba,Sae Sehrish da ta tsinci zoben Junaid a cikin wardrobe ɗina,tundaga nan ta fara sanya mun ido,ni kuma nayi kokarin rikitar da ita har ta fara ƴan gane gane..............."
Tunkan takai ƙarshen Maganar,Omar ya katse ta da cewa"Yanzu ina Junaid Yake,"?yayi tambayar tamkar baisan inda yake ba,
Shuru Azmee Ta É—anyi kafin tace"daga bayan nan Nasa an kaishi gidan Hajiya saratu,ÆŠiyar wan mahaifina wadda ke acikin garin nan,"..
 "Innalallahi wa'inna ilahirraji'un!!" Amrish ce ta ambaci hakan tare da ɗaura hannunta asaman kanta,Tana kuka,
Hankalin kowa Ya koma kanta,Muryarta na kerma ta nuna Azmee da hannunta tana faɗin"Dama ke kikasa aka kaishi gidanmu dan baƙin zalunci?Wacece ke?Ni bansan meya haɗani da ku ba,Wlh duk na tsani kaina,In har abunda nake zargi ya tabbata,wlh saina kashe kaina,"sosai ta fashe da kuka
Tunda Azmee taji hakan nan ta gane cewa wani abu ya faru acan gidan,tabbas Junaid Ya ku6uta daga wurinsu,.
Gyaran murya Ya Mu'allim yayi,hankalinsu ya dawo kanshi,Anan Yake labarta masu duk abunda ya faru kamar yarda Amrish ta sanar dashi,Har zuwa kaishi asibiti da su kayi,
Yana kai ƙarshen maganar,Azeemi tace"Naji daɗi da Junaid ya dawo hannunku,Amrish ke bakowa bace face ɗiyar saratu matar ƙanina Ya Sayyadi,Da saratu dani ƴa'ƴan wa da kanine,Don haka ke jininmu ce gaba da baya,babu yarda zakiyi haka Allah Ya ƙaddaro maki,Ki gode ma Allah da baki ɗaukko irin mugayen ɗabi'un mahaifinki da mahaifiyarki ba wanda hakan ne ma yasa ba'a bayyana maki mahaifin naki ba,"