Sashe 8
Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan ya fita daga sashen su kitchen ya nufa a lokacin Azmee harta kusa kammala aikin breakfast,yayi mamakin ganinta ita kadae tana ta faman aiki,
 Tana ganinshi ta ajiye aikin da takeyi ta ƙaraso gaban shi tare da gaishe shi cikin girmamawa tace"barka da safiya Abba,antashi lpy?jiya sai muka ji abun farin ciki,Hajiya azeema ke sanar dani wai ashe su sehrish ƴa'ƴan Abusufyan ne,Wlh nayi farin ciki sosai,dama na jima ina ganin kamanninta da Shi,'.
Fukarshi asake yace"wllh Alhmdllh,mun Samu ƙaruwar ƴan uku,ni dai ince jiya banganki ba,ae naso ace agabanki akayi komai,kema kiji wannan abun al'ajabin da kuma tashin hankalin,labarin dae babu daɗin ji,Amma ta wani 6angaren kuma mun gode ma Allah da ya bayyana mana yaran nan amatsayin jinin mu,munyi farin ciki sosai,har Walima ma nake so asake shirya mana saboda yaran nan,'
Murmushi azmee tayi tare da cewa"Yaushe kenan?ko yau zamu fara shiryawa ne"?
 Girgiza kai Abba yayi alamar a'a sannan yace"Wannan walimar ta musammance,gagarumin shagali za'ayi,akwai buƙatar kwanciyar hankali kafin lokacin,amma zanyi shawara da Abusufyan,idan har muka tsara komai,zan sanar maki,don ku shirya tarbar baƙi,zamu sa aƙaro wadanda zasu tayaki aiki.....'
 Tunkan yakai ƙarshen maganar azmee tace"a'a Abba,zan iya ni kaɗai,basai an ƙaro masu aiki ba'
 "Okey,ba damuwa naga kina ta wahala ke kadae,wai nikam ina yarinyar nan take ne?wata ƴar fara kanwarsu laila?naga kamar atare kuke aikin girki da ita ko ta koma gida ne"?
 Azmee tace"a'a bata koma ba,bata jin daɗin jikinta ne,shine nace mata ta huta kawai,in taji sauƙi taci gaba da tayani,saboda yarinyar akwai son aiki,'
Jinjina kai Abba yayi tare da cewa"Allah ya bata lpy,bari zanyi ma Kanal yousouf magana ya dubata...'
 Cikin sauri azmee tace"A'a....ae na bata magani dama ciwon ciki ne,insha Allah zata warke,'
  "Okey,' ya ambaci hakan tare da fucewa ya wuce cikin main palour dinsu,
 Zama yayi saman sofa yana murmushi,bakomai yake tunawa ba face yadda yaga abusufyan tare da ƴan ukunsa,aranshi yace"Allah sarki,rayuwa kenan komai mai wucewa ne in bawa yasa haƙuri aransa,junaid tun yana jinjiri rabonshi da mahaifiyarshi,sai gashi jiya rungume da ita yana bacci,ƴan ukun abusufyan tun suna ciki rabonsu da ubansu, tun kafin cikinsu ya bayyana ma,sun sha wahalar rayuwa amma sai gashi komai na rayuwarsu ya canza yanzu tamkar basu ta6a shiga wani ƙuncin rayuwa ba,sannu a hankali zasu manta da duk wata uƙuba da suka sha arayuwarsu,Yau dae gasu can rungume da mahaifinsu suna bacci,Allah sarki,
A ƙarshe kuma yace"Oh,ni kuma gani nan babu mai rungumata,abusufyan nacen rungume da ƴa'ƴan shi,junaid ma na can manne da mommynsu,gaskiya nayi kewarsu sosai......'
"Abba!" karaf kiran ya sauka a kunnanshi a ɗan firgice ya juya don yaga wanene,bakowa bane face Junaid yana tsaye hannunshi ruƙe da waist ɗinshi,har yanzu shaddar jiya ce ajikinshi,fuskar nan tashi cike da annuri sai faman zabga murmushi yake yi yadda kasan wanda akayi mashi albishir da gidan Aljana,
 Wani irin farin ciki ne ya lullu6e abbansu,yunkurawa yayi zai miƙe tunkan ya ƙarasa miƙewar junaid ya watsa da gudu kai tsaye ya faɗa jikinshi sosai ya rungume shi yana faɗin"I really miss u Abba,'
 "Nima junaid nayi kewarka sosai,jiya da tunaninka na kwana araina,'yayi maganar yana ɗan bubbuga bayanshi,
  raba jikinsu sukayi dana juna,ganin abbansu na kallon bayanshi yasa shi cewa"Abba mommy ko?
 murmushi yayi tare da cewa"Ashe ka gane,ta ina ne?ko ba tare kuka zo ba?
 ɗan ta6e baki junaid yayi nan fa hankalin abbansu ya tashi,.
Jiki asanyaye yace"Junaid bazata zo ba ko?Allah yasa dae ba Australlia ta koma ba,dama tunda na ganka kai kadae gabana ya fadi,don nasan halinta,'
 Fashewa da dariya junaid yayi ganin yadda Abban nasu ya tashi hankalinshi don baiga mommynsu ba,
 ɗaure fuskarshi yayi"oh ka ɗauki abun wasa ko?ba zaka faɗamun ina take ba,'
Yana cikin maganar ya jiyo takun takalminta,baisan lokacin daya janye junaid gefe ɗaya ba,Zuba mata ido yayi yana kallonta fuskarshi ɗauke da murmushi,tsayawa tayi tana ƙare mashi kallo,ba ƙaramin kyau tayi ba saboda kwalliyar da junaid yayi mata,da kanshi ya shafa mata janbaki ya gyara mata jagirar idonta,duk da haskenta sai da yashafa mata hoda,wai don Abbansu ya ganta da kyau,kuma shi da kanshi ya za6a mata rigar da zata sanya,jallabiya ce brown colour mai kyan gaske tayi rolling mayafi akanta,kamar wata balarabiya,tayi haske sosai kamar wata fatalwa,ga tsayi dake gareta kamar Sgr,
  Komawa junaid yayi saman sofa yana kallonsu,jira yake yaga mai zasu yi,sun wani ƙura ma juna ido,sae murmushi yake saki,
Cigaba da tafiya tayi harta ƙaraso kusa dashi suna fuskantar juna,
 Waro ido waje junaid yayi tare da cewa"Anshiga uku,Abba kaga yadda ka koma agaban mommy,wai dama ahaka kukayi aure Wayyo Allahna'
 maganar junaid tasa suka fashe da dariya gaba ɗayansu,shi abunda ya bashi mamaki tsawonta agaban abban nasu,sae yaga abban nasu ya koma mashi guntu,
 Sun jima suna sakar ma juna murmushi kafin daga bisani suka rungume juna sosai,kamar zasu zama daya,ba ƙaramin kewar juna sukayi ba,duk da akwanakin can baya yana kai mata ziyara Australlia,daga bayane ya daina zuwa saboda abubuwa da sukayi mashi yawa,
 Kasa rabuwa sukayi da junansu,junaid kuwa ya tasa su gaba yana kallonsu kamar wanda ya samu television,
 Adai dai lokacin twins suka shigo cikin falon,sakamakon Yunwa data ciwo su,karaf idanunsu suka sauka akan Mommynsu dake rungume da Abbansu,har suna haɗa baki wurin Cewa"Mommy!"
Cikin sauri suka raba jikinsu dana juna,wurga idanunta tayi akansu jahan da ayaan dake tsaye suna kallonta fuskar kowannansu É—auke da farin ciki,
 Da gudun gaske suka ƙarasa inda take gaba ɗaya suka faɗa jikinta,haɗasu tayi duka ta rungume ajikinta,tuni taji hawaye sun cicciko a idanunta,tayi kewar ƴa'ƴanta sosai,muryoyinsu tamkar zasu yi kuka suka haɗa baki wurin cewa"we really missed u mom!ashe zamu sake ganinki acikin gidanmu,'suka ƙarasa maganar ayayin da suke raba jikinsu da nata,
 Hawaye tagani a idanunsu,cikin sauri ta sanya hannunta tana share masu hawayen muryarta na rawa saboda kukan daya zo mata daƙyar ta iya cewa"i missed u too my twins,nasan ban kyauta maku..... '
 Jahan ya katseta"Mommy abubuwa da yawa sun faru,wanda da ace kina tare damu na tabbatar cewar bazasu faru ba,mun yi rashinki akusa damu mommy,munyi kewarki......'
 "Mommy..amma dae ba zaki sake komawa ba ko"?acewar ayaan
Jinjina mashi kai tayi alamar eh sannan tace"nadawo kenan bazan sake komawa ba,I will be with u,for the rest of my life....."
 Murmushi kawai Abbansu ke saki yana kallon uwa da ƴa'ƴanta,abubuwan farin ciki dae sai faruwa sukeyi acikin gidan,
 "Mommy,kinga junaid ko ya girma sosai,yayi kukan rashinki sosai lokacin da baki nan,amma yanzu nasan cewar zaki bashi kulawa,dan Allah mommy ki bashi kyakkyawar kulawa saboda yafi kowa buƙatarki,'ayaan ne yayi maganar yana kallon junaid dake zaune yana ta faman murmushi,
Itama kallon nashi tayi tare da cewa"Insha Allah ayaan,daga yanzu junaid zai canza gaba É—aya,zan bashi kyakkyawar kulawa,bama shi kadae ba hada ku gaba dayanku,Amma banga fawan ba dasu Irfan,and kanal yousouf ko duk suna ciki ne"?
 Jahan yace"basu tashi daga bacci ba,bari naje na kira maki fawan ɗin,'
Dakatar dashi tayi da cewa"A'a kada ka tashe shi daga bacci,nasan daga ya farka yaji labarin zuwa na zaizo ne,but where is Alexander?
 Atare suka haɗa baki wurin cewa"Mommy wanene Alexander kuma"?
 Dariya Abbansu yayi tare da cewa"tana nufin Babban yayanku,ae sunan data raɗa mashi kenan ko kun manta,'
 "Ae mun saba da kiranshi da babban yaya,mun manta da wannan sunan,shima yana a bedroom ɗinshi,duk bacci sukeyi saboda jiya bamu samu isasshen bacci ba,
 Abba ne yayi mata nuni da 3 seater din dake gefensu yace"bismillahi,ki zauna mana ko baki gaji da tsayuwa bane,ko da yake na tuna fa Soja ce matar tawa,'yayi maganar cikin zolaya,
 Murmushi kawai tayi tare da samun wuri ta zauna,shima abban nasu ya zauna daga gefenta,wuri su ayaan suka samu saman 2 seater suka zauna,
Cike da kulawa tace"Amma meya hanaku samun bacci da wuri ne?naji kunce baku samu isasshen bacci ba ko wani abu ya faru ne'?
  Ayaan yace"abun farin cikine ya faru jiya agidan nan mommy,nasan kin kwaso gajiyar tafiya,idan kika huta nasan cewa Abba zai baki labari anjima,"
 Da sauri junaid yace"meya faru ne?dan Allah ayaan ka faɗa mana yanzu kawai,Mommy fa tun jiya tazo ƙasar nan,muna acan tare da ita agidanta ma muka kwana,bata sanar ma kowa ba,sae abban mu,'
 Baki sake jahan yace"Wai dagaske?mommy abun ƴar haka ce,wato shine mu ba'a sanar mana da zuwan naki ba,junaid kawai kika sanar mawa,no wonder shiyasa jiya ban ganka ba,abun ya tsayamun araina,ba don abunda ya faru ba na bayyanar ƴa'ƴan uncle ɗinmu daba abunda zai hana mu nemeka a wannan lokacin,duk wannan abun shiya ɗauke mana hankalinmu....."tunkan ya ƙarasa maganar Junaid yace"Ƴa'ƴan uncle?wani uncle ɗin kenan"?aɗan rude yayi maganar,
 Miƙewa Ayaan yayi tare da ruƙo hannun junaid yabar wurin tare dashi,sai da suka samu wurin da bakowa sannan yace"kai kasan meya faru jiya"?
 Cike da zumuɗi junaid yace"taya za'ae in sani,ni da bana agida,don Allah ka sanar dani har naƙosa naji,'
Ayaan yace"hmmmmm,labari da É—umi É—uminsa,ko kasan cewa yarinyar nan Sehrish É—iyar uncle É—inmu ce Abusufyan?
 Gaban junaid ne ya faɗi rasss!saboda yadda maganar ta dira a kunnanshi,can kuma ya ɗan ɗaure fuskarshi yace"pls Ya ayaan dan Allah ka daina jamun rai,ni dae ka faɗimun gaskiyar abunda ya faru,'
 Ayaan yace"kai nifa bada wasa nake maka ba,na ta6a maka wasa irin wannan ne!Sehrish ɗiyar uncle ɗinmu ce abusufyan,
 Tur6une fuska junaid yayi tare da ɗan bubbuga ƙafarshi rai a6ace yace"yaushe uncle ya ta6a aure da har zai haifi ƴa'ƴa,kuma ma ƴar tashi ka rasa wadda zaka ce sae sehrish,kaji tsoran Allah ya Ayaan,babu kyau ƙarya,'
 Rai a6ace Ayaan ya dunguri goshin junaid tare da cewa"Shashasha,ana ƙoƙarin a fahimtar dakai amma kaƙi yadda,don ubanka kaje ɗakin nasu ka leƙa,zaka ga abun mamaki,'
 Turo baki junaid yayi tare da juyawa ya nufi hanyar xuwa ɗakin sehrish yana cewa"mai ƙarya dae ɗan wuta,'
 Murmushi ayaan yayi yana kallon bayanshi,yasan cewa muddin junaid yaga Sehrish da ƴan uwanta sai ya haukace masu,farat ɗaya bazaiyi tunanin ƴan uku bane,sae ranshi ya fara bashi cewar Aljanune,
 Tana ganinshi ta ajiye aikin da takeyi ta ƙaraso gaban shi tare da gaishe shi cikin girmamawa tace"barka da safiya Abba,antashi lpy?jiya sai muka ji abun farin ciki,Hajiya azeema ke sanar dani wai ashe su sehrish ƴa'ƴan Abusufyan ne,Wlh nayi farin ciki sosai,dama na jima ina ganin kamanninta da Shi,'.
Fukarshi asake yace"wllh Alhmdllh,mun Samu ƙaruwar ƴan uku,ni dai ince jiya banganki ba,ae naso ace agabanki akayi komai,kema kiji wannan abun al'ajabin da kuma tashin hankalin,labarin dae babu daɗin ji,Amma ta wani 6angaren kuma mun gode ma Allah da ya bayyana mana yaran nan amatsayin jinin mu,munyi farin ciki sosai,har Walima ma nake so asake shirya mana saboda yaran nan,'
Murmushi azmee tayi tare da cewa"Yaushe kenan?ko yau zamu fara shiryawa ne"?
 Girgiza kai Abba yayi alamar a'a sannan yace"Wannan walimar ta musammance,gagarumin shagali za'ayi,akwai buƙatar kwanciyar hankali kafin lokacin,amma zanyi shawara da Abusufyan,idan har muka tsara komai,zan sanar maki,don ku shirya tarbar baƙi,zamu sa aƙaro wadanda zasu tayaki aiki.....'
 Tunkan yakai ƙarshen maganar azmee tace"a'a Abba,zan iya ni kaɗai,basai an ƙaro masu aiki ba'
 "Okey,ba damuwa naga kina ta wahala ke kadae,wai nikam ina yarinyar nan take ne?wata ƴar fara kanwarsu laila?naga kamar atare kuke aikin girki da ita ko ta koma gida ne"?
 Azmee tace"a'a bata koma ba,bata jin daɗin jikinta ne,shine nace mata ta huta kawai,in taji sauƙi taci gaba da tayani,saboda yarinyar akwai son aiki,'
Jinjina kai Abba yayi tare da cewa"Allah ya bata lpy,bari zanyi ma Kanal yousouf magana ya dubata...'
 Cikin sauri azmee tace"A'a....ae na bata magani dama ciwon ciki ne,insha Allah zata warke,'
  "Okey,' ya ambaci hakan tare da fucewa ya wuce cikin main palour dinsu,
 Zama yayi saman sofa yana murmushi,bakomai yake tunawa ba face yadda yaga abusufyan tare da ƴan ukunsa,aranshi yace"Allah sarki,rayuwa kenan komai mai wucewa ne in bawa yasa haƙuri aransa,junaid tun yana jinjiri rabonshi da mahaifiyarshi,sai gashi jiya rungume da ita yana bacci,ƴan ukun abusufyan tun suna ciki rabonsu da ubansu, tun kafin cikinsu ya bayyana ma,sun sha wahalar rayuwa amma sai gashi komai na rayuwarsu ya canza yanzu tamkar basu ta6a shiga wani ƙuncin rayuwa ba,sannu a hankali zasu manta da duk wata uƙuba da suka sha arayuwarsu,Yau dae gasu can rungume da mahaifinsu suna bacci,Allah sarki,
A ƙarshe kuma yace"Oh,ni kuma gani nan babu mai rungumata,abusufyan nacen rungume da ƴa'ƴan shi,junaid ma na can manne da mommynsu,gaskiya nayi kewarsu sosai......'
"Abba!" karaf kiran ya sauka a kunnanshi a ɗan firgice ya juya don yaga wanene,bakowa bane face Junaid yana tsaye hannunshi ruƙe da waist ɗinshi,har yanzu shaddar jiya ce ajikinshi,fuskar nan tashi cike da annuri sai faman zabga murmushi yake yi yadda kasan wanda akayi mashi albishir da gidan Aljana,
 Wani irin farin ciki ne ya lullu6e abbansu,yunkurawa yayi zai miƙe tunkan ya ƙarasa miƙewar junaid ya watsa da gudu kai tsaye ya faɗa jikinshi sosai ya rungume shi yana faɗin"I really miss u Abba,'
 "Nima junaid nayi kewarka sosai,jiya da tunaninka na kwana araina,'yayi maganar yana ɗan bubbuga bayanshi,
  raba jikinsu sukayi dana juna,ganin abbansu na kallon bayanshi yasa shi cewa"Abba mommy ko?
 murmushi yayi tare da cewa"Ashe ka gane,ta ina ne?ko ba tare kuka zo ba?
 ɗan ta6e baki junaid yayi nan fa hankalin abbansu ya tashi,.
Jiki asanyaye yace"Junaid bazata zo ba ko?Allah yasa dae ba Australlia ta koma ba,dama tunda na ganka kai kadae gabana ya fadi,don nasan halinta,'
 Fashewa da dariya junaid yayi ganin yadda Abban nasu ya tashi hankalinshi don baiga mommynsu ba,
 ɗaure fuskarshi yayi"oh ka ɗauki abun wasa ko?ba zaka faɗamun ina take ba,'
Yana cikin maganar ya jiyo takun takalminta,baisan lokacin daya janye junaid gefe ɗaya ba,Zuba mata ido yayi yana kallonta fuskarshi ɗauke da murmushi,tsayawa tayi tana ƙare mashi kallo,ba ƙaramin kyau tayi ba saboda kwalliyar da junaid yayi mata,da kanshi ya shafa mata janbaki ya gyara mata jagirar idonta,duk da haskenta sai da yashafa mata hoda,wai don Abbansu ya ganta da kyau,kuma shi da kanshi ya za6a mata rigar da zata sanya,jallabiya ce brown colour mai kyan gaske tayi rolling mayafi akanta,kamar wata balarabiya,tayi haske sosai kamar wata fatalwa,ga tsayi dake gareta kamar Sgr,
  Komawa junaid yayi saman sofa yana kallonsu,jira yake yaga mai zasu yi,sun wani ƙura ma juna ido,sae murmushi yake saki,
Cigaba da tafiya tayi harta ƙaraso kusa dashi suna fuskantar juna,
 Waro ido waje junaid yayi tare da cewa"Anshiga uku,Abba kaga yadda ka koma agaban mommy,wai dama ahaka kukayi aure Wayyo Allahna'
 maganar junaid tasa suka fashe da dariya gaba ɗayansu,shi abunda ya bashi mamaki tsawonta agaban abban nasu,sae yaga abban nasu ya koma mashi guntu,
 Sun jima suna sakar ma juna murmushi kafin daga bisani suka rungume juna sosai,kamar zasu zama daya,ba ƙaramin kewar juna sukayi ba,duk da akwanakin can baya yana kai mata ziyara Australlia,daga bayane ya daina zuwa saboda abubuwa da sukayi mashi yawa,
 Kasa rabuwa sukayi da junansu,junaid kuwa ya tasa su gaba yana kallonsu kamar wanda ya samu television,
 Adai dai lokacin twins suka shigo cikin falon,sakamakon Yunwa data ciwo su,karaf idanunsu suka sauka akan Mommynsu dake rungume da Abbansu,har suna haɗa baki wurin Cewa"Mommy!"
Cikin sauri suka raba jikinsu dana juna,wurga idanunta tayi akansu jahan da ayaan dake tsaye suna kallonta fuskar kowannansu É—auke da farin ciki,
 Da gudun gaske suka ƙarasa inda take gaba ɗaya suka faɗa jikinta,haɗasu tayi duka ta rungume ajikinta,tuni taji hawaye sun cicciko a idanunta,tayi kewar ƴa'ƴanta sosai,muryoyinsu tamkar zasu yi kuka suka haɗa baki wurin cewa"we really missed u mom!ashe zamu sake ganinki acikin gidanmu,'suka ƙarasa maganar ayayin da suke raba jikinsu da nata,
 Hawaye tagani a idanunsu,cikin sauri ta sanya hannunta tana share masu hawayen muryarta na rawa saboda kukan daya zo mata daƙyar ta iya cewa"i missed u too my twins,nasan ban kyauta maku..... '
 Jahan ya katseta"Mommy abubuwa da yawa sun faru,wanda da ace kina tare damu na tabbatar cewar bazasu faru ba,mun yi rashinki akusa damu mommy,munyi kewarki......'
 "Mommy..amma dae ba zaki sake komawa ba ko"?acewar ayaan
Jinjina mashi kai tayi alamar eh sannan tace"nadawo kenan bazan sake komawa ba,I will be with u,for the rest of my life....."
 Murmushi kawai Abbansu ke saki yana kallon uwa da ƴa'ƴanta,abubuwan farin ciki dae sai faruwa sukeyi acikin gidan,
 "Mommy,kinga junaid ko ya girma sosai,yayi kukan rashinki sosai lokacin da baki nan,amma yanzu nasan cewar zaki bashi kulawa,dan Allah mommy ki bashi kyakkyawar kulawa saboda yafi kowa buƙatarki,'ayaan ne yayi maganar yana kallon junaid dake zaune yana ta faman murmushi,
Itama kallon nashi tayi tare da cewa"Insha Allah ayaan,daga yanzu junaid zai canza gaba É—aya,zan bashi kyakkyawar kulawa,bama shi kadae ba hada ku gaba dayanku,Amma banga fawan ba dasu Irfan,and kanal yousouf ko duk suna ciki ne"?
 Jahan yace"basu tashi daga bacci ba,bari naje na kira maki fawan ɗin,'
Dakatar dashi tayi da cewa"A'a kada ka tashe shi daga bacci,nasan daga ya farka yaji labarin zuwa na zaizo ne,but where is Alexander?
 Atare suka haɗa baki wurin cewa"Mommy wanene Alexander kuma"?
 Dariya Abbansu yayi tare da cewa"tana nufin Babban yayanku,ae sunan data raɗa mashi kenan ko kun manta,'
 "Ae mun saba da kiranshi da babban yaya,mun manta da wannan sunan,shima yana a bedroom ɗinshi,duk bacci sukeyi saboda jiya bamu samu isasshen bacci ba,
 Abba ne yayi mata nuni da 3 seater din dake gefensu yace"bismillahi,ki zauna mana ko baki gaji da tsayuwa bane,ko da yake na tuna fa Soja ce matar tawa,'yayi maganar cikin zolaya,
 Murmushi kawai tayi tare da samun wuri ta zauna,shima abban nasu ya zauna daga gefenta,wuri su ayaan suka samu saman 2 seater suka zauna,
Cike da kulawa tace"Amma meya hanaku samun bacci da wuri ne?naji kunce baku samu isasshen bacci ba ko wani abu ya faru ne'?
  Ayaan yace"abun farin cikine ya faru jiya agidan nan mommy,nasan kin kwaso gajiyar tafiya,idan kika huta nasan cewa Abba zai baki labari anjima,"
 Da sauri junaid yace"meya faru ne?dan Allah ayaan ka faɗa mana yanzu kawai,Mommy fa tun jiya tazo ƙasar nan,muna acan tare da ita agidanta ma muka kwana,bata sanar ma kowa ba,sae abban mu,'
 Baki sake jahan yace"Wai dagaske?mommy abun ƴar haka ce,wato shine mu ba'a sanar mana da zuwan naki ba,junaid kawai kika sanar mawa,no wonder shiyasa jiya ban ganka ba,abun ya tsayamun araina,ba don abunda ya faru ba na bayyanar ƴa'ƴan uncle ɗinmu daba abunda zai hana mu nemeka a wannan lokacin,duk wannan abun shiya ɗauke mana hankalinmu....."tunkan ya ƙarasa maganar Junaid yace"Ƴa'ƴan uncle?wani uncle ɗin kenan"?aɗan rude yayi maganar,
 Miƙewa Ayaan yayi tare da ruƙo hannun junaid yabar wurin tare dashi,sai da suka samu wurin da bakowa sannan yace"kai kasan meya faru jiya"?
 Cike da zumuɗi junaid yace"taya za'ae in sani,ni da bana agida,don Allah ka sanar dani har naƙosa naji,'
Ayaan yace"hmmmmm,labari da É—umi É—uminsa,ko kasan cewa yarinyar nan Sehrish É—iyar uncle É—inmu ce Abusufyan?
 Gaban junaid ne ya faɗi rasss!saboda yadda maganar ta dira a kunnanshi,can kuma ya ɗan ɗaure fuskarshi yace"pls Ya ayaan dan Allah ka daina jamun rai,ni dae ka faɗimun gaskiyar abunda ya faru,'
 Ayaan yace"kai nifa bada wasa nake maka ba,na ta6a maka wasa irin wannan ne!Sehrish ɗiyar uncle ɗinmu ce abusufyan,
 Tur6une fuska junaid yayi tare da ɗan bubbuga ƙafarshi rai a6ace yace"yaushe uncle ya ta6a aure da har zai haifi ƴa'ƴa,kuma ma ƴar tashi ka rasa wadda zaka ce sae sehrish,kaji tsoran Allah ya Ayaan,babu kyau ƙarya,'
 Rai a6ace Ayaan ya dunguri goshin junaid tare da cewa"Shashasha,ana ƙoƙarin a fahimtar dakai amma kaƙi yadda,don ubanka kaje ɗakin nasu ka leƙa,zaka ga abun mamaki,'
 Turo baki junaid yayi tare da juyawa ya nufi hanyar xuwa ɗakin sehrish yana cewa"mai ƙarya dae ɗan wuta,'
 Murmushi ayaan yayi yana kallon bayanshi,yasan cewa muddin junaid yaga Sehrish da ƴan uwanta sai ya haukace masu,farat ɗaya bazaiyi tunanin ƴan uku bane,sae ranshi ya fara bashi cewar Aljanune,