Sashe 18
Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Wuraren ƙarfe biyu daidai na dare,wata irin guguwar iska,ta shigo ta cikin windown ɗakin su Sehrish mai matuƙar tsoratarwa da kuma razanarwa baƙi wulik mai tafe da wani irin sauti,wanda ya ciccika kunnuwansu,a firgice hosana ta farka tare da fasa wata irin razananniyar ƙara,wanda yayi silar tashin Sehrish,ita kanta ta tsorata da ganin guguwar iskar nan,ta tattare wuri guda yadda kasan kwarangwal din mutun haka shape ɗinta ya koma bayan ta sauka a dakin nasu,ga yayi ajikinta,
 Ƙanƙame Sehrish hosana tayi sosai tana cewa"Wayyo Allahna,mun shigo uku,ina daddynmu yake,menene wannan abun,'
 Babu abunda Sehrish ke ambato face"innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,yayin da ta ƙura idanunta akan guguwar nan data saukar masu acikin ɗakinsu,
 jikinsu sae faman kerma yake yi gaba ɗayansu,hakoransu sae faman rawar ɗari suke yi kaf kaf kaf,saboda wani irin sanyi daya ziyarce su,
 ganin guguwar ta tsaya agefen gadonsu,kamar su take kallo don harda ƴan idanu gare ta hakan yasa suka ƙara fashewa da kuka suna faɗin"Wayyo Allah mun shiga uku!"
A firgice jahad ta farka,jin ihun da su hosana keyi,adai dai lokacin hosana na cewa"wlh hada Æ´an idanu ke gare ta,mun shiga uku,"
 Zuba masu ido jahad tayi tana kallonsu ganin yadda suka kware baki suna kuka,Ga bargo a hannunsu,sun rurruƙe,
 A hankali ta mayar da idanunta kan abunda suke kallo,guguwar nan ta gani tsaye da suffar kwarangwal tayi masu ƙuru da ido,
 "Jahad kina ganin abunda muke gani kuwa"?Sehrish ce tayi mata maganar,
 Jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Nagani,mutun ne wannan ba guguwar gaske ba,koma waye yazo ne don ya tsoratar damu ne kawai babu abunda zai iyayi mana,"
 Hankali atashe hosana da sehrish suke kallon jahad,jin abunda tace,babu alamun jin tsoro atattare da ita,hankalinta kwance tayi maganar,ganin haka yasa suma suka dakatar da kukan da sukeyi,
  "Wama ya sani,ko ya sayyadi ne yazo da suffar guguwar nan don yazo yaga yadda muka koma," jahad ce tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,
Baki asake suke kallonta,sehrish tace"Anya jahad ba macanzarki akayi mana ba?na fara kokwanto anya kece?taya zaki ga wannan tashin hankalin amma ki nuna baki damu ba?guguwa face tayi suffar kwarangwal kuma hada Æ´an idanu kuru tana kallonmu ki kalla dakyau,"
 Tsoki jahad taja tare da cewa"Nice mana,nifa Allah kaɗai nake tsoro,dashi na dogara,wannan koma menene yazo wlh ni dariya ma halittar take bani,ji idon fa yadda yake jujjuyawa kamar an ɗorashi,' fashewa da dariya jahad ta kuma yi,Kafin ta kalli su hosana tace"abunda za'ae yanzu muja bargo mu lullu6e,mu rabu da ita,idan ta gaji da tsayuwa ta tafi,koda yake ba ƙafafu gareta ba,fiffike zatayi ta tashi,'
Ta ƙarasa maganar cike da nishaɗi,jan bargon nasu tayi,cikin sauri suka gyara kwanciyarsu ta lullu6esu da bargon,saboda tsabar tsoro Bargon da suka lullu6a dashi sae faman kerma yake yi,
 "Jahad dagaske,baki ji tsoron wannan abun ba"?kasa-kasa Sehrish ta tambaye ta,
 Murya na kerma jahad tace"yanzu haka ma kuka nake yi,wlh atsorace nake,ƙarfin hali kawai nayi,saboda na ta6a jin wani malami yace idan ka nuna kana jin tsoran Aljani shine yake cin nasara akan mutun,shi har faɗama yake yi da aljanu shine nima na jaraba yin irin nashi,'
 Duk da halin da Sehrish ke ciki sai da ta fashe da dariya tana kumshe baki,
 "Jahad kinja mana bala'e,koma meye yanzu kin ƙara fusata shi da kalamanki,bansan me zai biyo baya ba,"acewar sehrish,
 Jahad tace"Addu'a zamuyi kawai,insha Allah ba abunda zasu iya yi mana,'
 Muryar hosana suka jiyo abayansu tana cewa"Sehrish dan Allah kuyimun addu'a,ko fatiha bazan iya karantawa ba a halin da nake ciki a yanzu,ga fitsari ya matse ni,'muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,
 Jahad tace"ki tashi ki shiga toilet mana!kinsan Allah kada kiyi mana fitsarin kwance,'
 Fashewa da kuka hosana tayi tana cewa"taya zaki ce in shiga toilet bayan wannan halittar na nan ta ƙura mana ƴan idanunta,Allah ba inda zanje,sai dae ki tashi ki rakani ko kuma inyi shi a wando,'
 Har haɗa baki sukeyi wurin cewa"Wai wa zai raka ki"?
 "Ke ko sehrish daya daga cikinku ta rakani,"
 "Tab,wlh nidai ba inda zanje,sai dai ko Sehrish," jahad nakai ƙarshen maganarta sehrish tace"Ke baki je ba sai ni kike tunanin cewa zan rakata,Ae wlh sai dae tayi shi a wando,ba inda zanje,"
 Ganin basu ɗauki maganarta serious ba yasa ta ƙara fashewa da wani kukan mai sauti,
   "Dawo tsakiyarmu ki kwanta,zanyi maki addu'ar ɗaukewar fitsari,ae na iya,Oumma ta ta6a koya mana,"fashewa da dariya sehrish tayi tana cewa"kai jahad,ni ban ta6a jin wata addu'a ta ɗauke fitsari ba,'
 Tashi hosana tayi tare da komawa tsakiyarsu ta kwanta,tana jiran Jahad tayi mata addu'a kamar yadda tace'
 "Rufe idanunki"jahad ta fadi hakan fuskarta ƙumshe da dariya,runtse ido hosana tayi tare da cewa"Na rufe,"
 Tofa mata addu'a jahad ta shiga yi a fuskarta,ita kanta me addu'ar batasan me take fadi ba,sae faman motsi take da baki,intayi sosai saita tofa ma hosana a fuskarta,
 A ƙule hosana tace"waini sai tofa mun miyau kike a fuskata,kuma ni banji kina addu'ar ba,'
 "Ita addu'ar a sirrance akeyinta,ba a bayyanata,kiyi shiru kawai zanci gaba da karanta maki har a samu fitsarin ya ɗauke,
 Shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,yayin da jahad taci gaba da karanta mata addu'ar,duk sehrish na sauraronsu,
 Abu kamar wasa,bacci ya ɗauki hosana,
 "Kamar tayi bacci"?sehrish ta tambaya,
 Jahad tace"eh,tayi bacci yanzu saura mu ya rage muyi bacci,'
 Sehrish tace"taya zamu iya bacci da waccen halittar a ɗakinmu?inta cutar damu fa"?
 Jahad tace"Insha Allah ba abunda zata iya yi mana,muyi addu'a kawai mu kwanta,mu ɗauka kamar mafarki ma mukeyi,"
 Kamar yadda jahad tace haka suka haɗa baki suna karanta addu'oi,bayan sun kammala kuma suka shiga karanta ayoyin alkur'ani mai girma atare,cikin lokaci ƙankani bacci ya ɗaukesu,
 Yin baccinsu keda wuya wannan guguwar ta disashe daga wurin ta 6ace 6aat.
Tashin hankali,kowaye yazo masu da wannan suffar?
Abunda ya faru bayan fitar abbansu daga bedroom ɗinshi,kai tsaye ya wuce upstairs part ɗin Marshal Omar,jikinshi duk asanyaye haƙika junaid ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,da alama sakin fuskar da yake yi mashi ne yana wasa dashi kamar tsaranshi,hakanne yasa raini ya fara shiga tsakaninsu,
Da sallama abakinsa ya shiga bedroom É—in Marshal,samunshi yayi a kwance yana sharar bacci,bedside lamps É—insa ne suka haskaka wurin bed É—insa,
Shiga ciki abbansu yayi tare da hayewa saman gadon,ya jingina bayanshi a jikin headboard ɗin gadan,Ranshi duk a jagule yama kasa kwanciyar saboda yasan cewa koya kwanta bazai iya runtsawa ba,ba ƙaramin ƙuntata yayi ba,junaid ya fusata shi sosai,
 Kwakkwaran juyi marshal yayi zai gyara kwanciyarshi,karaf idanunshi suka sauka akan Abban nasu,cike da mamaki ya ambaci sunanshi"Abba!"
 fuskarshi ɗauke da damuwa yakai idanunshi akan fuskar Marshal yace"Omar,dama ba bacci kakeyi ba ne?"yayi maganar ayayin da yake ƙoƙarin 6oye damuwarshi,
 Yunƙurawa Omar yayi tare da tashi daga zaune yana fuskantar abban nasu yace"Abba!meya faru naganka anan?kuma fuskarka da alamun damuwa attare dakai,"?
 shiru abbansu yayi na wani lokaci yana deciding akan ya faɗa ma Omar halin da yake ciki ko kuwa ya ƙyale zancem kawai,
 "Omar,ashe junaid bai da wayau har yanzu yaro ne shi"?
 aɗan ruɗe omar yace"me junaid ya aikata,"?
 "Hmmm,ya hanani sakat Omar,ƙiri ƙiri junaid ya shige mun ɗakina,yana can rungume da mommynsa,nayi nayi dashi ya tashi in kwanta amma ya ƙiya,wai har ni yake ce ma Yau kwanan sa ne!"?
Murmushi marshal Omar yayi jin shiriritar junaid,wato yau da Abbansu yake kishi,
  "Abba,just calm down ur mind,ka bani 5 minutes yanzu zan dawo,just wait,"
 Ya ƙarasa maganar tare da miƙewa ya kama hanyar fucewa daga bedroom ɗin,
 Zugudum abbansu yayi yana jiran dawowar Marshal,
 Ƙanƙame Sehrish hosana tayi sosai tana cewa"Wayyo Allahna,mun shigo uku,ina daddynmu yake,menene wannan abun,'
 Babu abunda Sehrish ke ambato face"innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,yayin da ta ƙura idanunta akan guguwar nan data saukar masu acikin ɗakinsu,
 jikinsu sae faman kerma yake yi gaba ɗayansu,hakoransu sae faman rawar ɗari suke yi kaf kaf kaf,saboda wani irin sanyi daya ziyarce su,
 ganin guguwar ta tsaya agefen gadonsu,kamar su take kallo don harda ƴan idanu gare ta hakan yasa suka ƙara fashewa da kuka suna faɗin"Wayyo Allah mun shiga uku!"
A firgice jahad ta farka,jin ihun da su hosana keyi,adai dai lokacin hosana na cewa"wlh hada Æ´an idanu ke gare ta,mun shiga uku,"
 Zuba masu ido jahad tayi tana kallonsu ganin yadda suka kware baki suna kuka,Ga bargo a hannunsu,sun rurruƙe,
 A hankali ta mayar da idanunta kan abunda suke kallo,guguwar nan ta gani tsaye da suffar kwarangwal tayi masu ƙuru da ido,
 "Jahad kina ganin abunda muke gani kuwa"?Sehrish ce tayi mata maganar,
 Jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Nagani,mutun ne wannan ba guguwar gaske ba,koma waye yazo ne don ya tsoratar damu ne kawai babu abunda zai iyayi mana,"
 Hankali atashe hosana da sehrish suke kallon jahad,jin abunda tace,babu alamun jin tsoro atattare da ita,hankalinta kwance tayi maganar,ganin haka yasa suma suka dakatar da kukan da sukeyi,
  "Wama ya sani,ko ya sayyadi ne yazo da suffar guguwar nan don yazo yaga yadda muka koma," jahad ce tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,
Baki asake suke kallonta,sehrish tace"Anya jahad ba macanzarki akayi mana ba?na fara kokwanto anya kece?taya zaki ga wannan tashin hankalin amma ki nuna baki damu ba?guguwa face tayi suffar kwarangwal kuma hada Æ´an idanu kuru tana kallonmu ki kalla dakyau,"
 Tsoki jahad taja tare da cewa"Nice mana,nifa Allah kaɗai nake tsoro,dashi na dogara,wannan koma menene yazo wlh ni dariya ma halittar take bani,ji idon fa yadda yake jujjuyawa kamar an ɗorashi,' fashewa da dariya jahad ta kuma yi,Kafin ta kalli su hosana tace"abunda za'ae yanzu muja bargo mu lullu6e,mu rabu da ita,idan ta gaji da tsayuwa ta tafi,koda yake ba ƙafafu gareta ba,fiffike zatayi ta tashi,'
Ta ƙarasa maganar cike da nishaɗi,jan bargon nasu tayi,cikin sauri suka gyara kwanciyarsu ta lullu6esu da bargon,saboda tsabar tsoro Bargon da suka lullu6a dashi sae faman kerma yake yi,
 "Jahad dagaske,baki ji tsoron wannan abun ba"?kasa-kasa Sehrish ta tambaye ta,
 Murya na kerma jahad tace"yanzu haka ma kuka nake yi,wlh atsorace nake,ƙarfin hali kawai nayi,saboda na ta6a jin wani malami yace idan ka nuna kana jin tsoran Aljani shine yake cin nasara akan mutun,shi har faɗama yake yi da aljanu shine nima na jaraba yin irin nashi,'
 Duk da halin da Sehrish ke ciki sai da ta fashe da dariya tana kumshe baki,
 "Jahad kinja mana bala'e,koma meye yanzu kin ƙara fusata shi da kalamanki,bansan me zai biyo baya ba,"acewar sehrish,
 Jahad tace"Addu'a zamuyi kawai,insha Allah ba abunda zasu iya yi mana,'
 Muryar hosana suka jiyo abayansu tana cewa"Sehrish dan Allah kuyimun addu'a,ko fatiha bazan iya karantawa ba a halin da nake ciki a yanzu,ga fitsari ya matse ni,'muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,
 Jahad tace"ki tashi ki shiga toilet mana!kinsan Allah kada kiyi mana fitsarin kwance,'
 Fashewa da kuka hosana tayi tana cewa"taya zaki ce in shiga toilet bayan wannan halittar na nan ta ƙura mana ƴan idanunta,Allah ba inda zanje,sai dae ki tashi ki rakani ko kuma inyi shi a wando,'
 Har haɗa baki sukeyi wurin cewa"Wai wa zai raka ki"?
 "Ke ko sehrish daya daga cikinku ta rakani,"
 "Tab,wlh nidai ba inda zanje,sai dai ko Sehrish," jahad nakai ƙarshen maganarta sehrish tace"Ke baki je ba sai ni kike tunanin cewa zan rakata,Ae wlh sai dae tayi shi a wando,ba inda zanje,"
 Ganin basu ɗauki maganarta serious ba yasa ta ƙara fashewa da wani kukan mai sauti,
   "Dawo tsakiyarmu ki kwanta,zanyi maki addu'ar ɗaukewar fitsari,ae na iya,Oumma ta ta6a koya mana,"fashewa da dariya sehrish tayi tana cewa"kai jahad,ni ban ta6a jin wata addu'a ta ɗauke fitsari ba,'
 Tashi hosana tayi tare da komawa tsakiyarsu ta kwanta,tana jiran Jahad tayi mata addu'a kamar yadda tace'
 "Rufe idanunki"jahad ta fadi hakan fuskarta ƙumshe da dariya,runtse ido hosana tayi tare da cewa"Na rufe,"
 Tofa mata addu'a jahad ta shiga yi a fuskarta,ita kanta me addu'ar batasan me take fadi ba,sae faman motsi take da baki,intayi sosai saita tofa ma hosana a fuskarta,
 A ƙule hosana tace"waini sai tofa mun miyau kike a fuskata,kuma ni banji kina addu'ar ba,'
 "Ita addu'ar a sirrance akeyinta,ba a bayyanata,kiyi shiru kawai zanci gaba da karanta maki har a samu fitsarin ya ɗauke,
 Shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,yayin da jahad taci gaba da karanta mata addu'ar,duk sehrish na sauraronsu,
 Abu kamar wasa,bacci ya ɗauki hosana,
 "Kamar tayi bacci"?sehrish ta tambaya,
 Jahad tace"eh,tayi bacci yanzu saura mu ya rage muyi bacci,'
 Sehrish tace"taya zamu iya bacci da waccen halittar a ɗakinmu?inta cutar damu fa"?
 Jahad tace"Insha Allah ba abunda zata iya yi mana,muyi addu'a kawai mu kwanta,mu ɗauka kamar mafarki ma mukeyi,"
 Kamar yadda jahad tace haka suka haɗa baki suna karanta addu'oi,bayan sun kammala kuma suka shiga karanta ayoyin alkur'ani mai girma atare,cikin lokaci ƙankani bacci ya ɗaukesu,
 Yin baccinsu keda wuya wannan guguwar ta disashe daga wurin ta 6ace 6aat.
Tashin hankali,kowaye yazo masu da wannan suffar?
Abunda ya faru bayan fitar abbansu daga bedroom ɗinshi,kai tsaye ya wuce upstairs part ɗin Marshal Omar,jikinshi duk asanyaye haƙika junaid ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,da alama sakin fuskar da yake yi mashi ne yana wasa dashi kamar tsaranshi,hakanne yasa raini ya fara shiga tsakaninsu,
Da sallama abakinsa ya shiga bedroom É—in Marshal,samunshi yayi a kwance yana sharar bacci,bedside lamps É—insa ne suka haskaka wurin bed É—insa,
Shiga ciki abbansu yayi tare da hayewa saman gadon,ya jingina bayanshi a jikin headboard ɗin gadan,Ranshi duk a jagule yama kasa kwanciyar saboda yasan cewa koya kwanta bazai iya runtsawa ba,ba ƙaramin ƙuntata yayi ba,junaid ya fusata shi sosai,
 Kwakkwaran juyi marshal yayi zai gyara kwanciyarshi,karaf idanunshi suka sauka akan Abban nasu,cike da mamaki ya ambaci sunanshi"Abba!"
 fuskarshi ɗauke da damuwa yakai idanunshi akan fuskar Marshal yace"Omar,dama ba bacci kakeyi ba ne?"yayi maganar ayayin da yake ƙoƙarin 6oye damuwarshi,
 Yunƙurawa Omar yayi tare da tashi daga zaune yana fuskantar abban nasu yace"Abba!meya faru naganka anan?kuma fuskarka da alamun damuwa attare dakai,"?
 shiru abbansu yayi na wani lokaci yana deciding akan ya faɗa ma Omar halin da yake ciki ko kuwa ya ƙyale zancem kawai,
 "Omar,ashe junaid bai da wayau har yanzu yaro ne shi"?
 aɗan ruɗe omar yace"me junaid ya aikata,"?
 "Hmmm,ya hanani sakat Omar,ƙiri ƙiri junaid ya shige mun ɗakina,yana can rungume da mommynsa,nayi nayi dashi ya tashi in kwanta amma ya ƙiya,wai har ni yake ce ma Yau kwanan sa ne!"?
Murmushi marshal Omar yayi jin shiriritar junaid,wato yau da Abbansu yake kishi,
  "Abba,just calm down ur mind,ka bani 5 minutes yanzu zan dawo,just wait,"
 Ya ƙarasa maganar tare da miƙewa ya kama hanyar fucewa daga bedroom ɗin,
 Zugudum abbansu yayi yana jiran dawowar Marshal,