Sashe 95
Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Gab da sallar magrib,Wayarta dake ajiye saman gadonsu ta shiga ringing,a lokacin tana acikin toilet,Jahad ce kawai acikin bedroom ɗin nasu,tayi zaman cin tuwo saman gadon,ta ƙura ido tana kallon k-drama acikin system dinsu,Hannu tasa tare da daukar wayar Sehrish,ta duba mai kiran nata,Sunan Aunty azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,picking tayi tare da manna wayar a kunnanta,
 "Assalamu alaikum,mommy azeema"
On the other hand azeema tace"Daughter,kin ga saƙo na"?_
Murmushi jahad tayi kafin tace"Aunty azeema yanzu baki gane muryoyin mu?Jahad fa ce ba rishi ba,"
 Hajiya azeema tace"wlh naso in ɗauki muryarki,Ashe second daughter ce,To ya kike"?
 "Lafiya lou Alhamdulillah ina lafiya,"
 "Madallah,Amaryar junaid,"
Cike da jin kunya jahad tace"Aunty azeema waya faÉ—i zancen nan,"
  Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"oh kin manta matsayina a wurin daddynku ne?Ae shi da kanshi ya sanar dani,kuma naji daɗi wlh,Junaid zai samu kamilar mace wadda zata kula da rayuwarshi,"_
kayataccen murmushi jahad ta saki,ba ƙaramin daɗin maganar taji ba,
  "Ina fata zaki kula mana da bugun zuciyar mu?
 Dariya jahad tayi tana faɗin"in sha Allah,zan kula maku dashi,"
 Hajiya azeema tace"Yawwa My daughter,but akwai abunda nakeso na tattauna tare dake game da junaid!amma ki bari zan kira wayarki,ko zuwa anjima ne,"
 "To Aunty Allah yakaimu anjiman lafiya,"
 "Ameen daughter,ina sehrish ɗin take ne?inaso nayi magana da ita ne,"
 Jahad na ƙoƙarin bude baki tayi magana,sai ga sehrish ta fito daga toilet din,jikinta sanye da bathrobe,wankan marece tayi,dama duk in tana period,kusan sau uku take yin wanka,'
  Ganin wayarta a hannun jahad yasa ta tunkarota tana tambayarta wanene ya kirata,
 Mika mata wayar jahad tayi"kar6i nan,Mommy azeema ce keson magana dake"
 Jiki na rawa ta kar6i wayar,da sauri ta koma gaban mirror,ta zauna saman kujerar,sannan tayi mata sallama,
 "Daughter,ya ake ciki ne?ina fata kinga saƙona ko"?
..Sehrish tace"nagani,junaid ya kawomin su,nagode sosai,"
 "Yawwa,Zaki ga turarurruka aciki,Tun yanzu zaki fara amfani dasu,akwai wasu sirrika atattare dasu,sannan akwai mayuka na gyaran fata,dana gyaran gashi,Original ne,Cikin one week,kina fara amfani dasu zaki ga sauyi a jikinki,Sannan akwai sauran kayan da ba yanzu zakiyi amfani dasu ba,suna da haɗarin gaske,su kansu turarurrukan nan,Shu'umaine na gaske,Fisgar mutun sukeyi kamar magnet,ƙarfi ne dasu,duk in zaki shafasu ki bari sai in zaki part ɗinsa,idan ba haka ba gaskiya za'a iya samun matsala,"
 Natsuwa sehrish tayi tana sauraronta,sun jima suna waya kafin daga bisani su kayi sallama,
  Kasa yin amfani da turaren tayi,tsoranshi ma take ji,tunda taji ance fisgar mutun yake yi,kada ta jama kanta bala'e tana zaman zamanta lafiya,
  bata shafa turaren ba,Amma ta fara amfani da mayukan gyaran jikin,
 Shaf shaf ta shirya cikin Doguwar riga ta material black colour,mai zanen manyan flowers a jikinshi launin ash,rigar tabi shape ɗin jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba gaban mirror ta koma ta zauna,powder ta murza a fuskarta,Sannan ta shafa man baki,la66anta sae salƙi sukeyi,
  Bata yafa komai akanta ba,Iya sumar kanta ce data sauko har gadon bayanta,high hills ta zura a ƙafarta,
Kama hanyar fita daga É—akin tayi da sauri jahad tace"Ina zuwa?
"Zanje part É—in babban yaya ne,Inaso na gyara mashi ne,"
Murmushi jahad ta saki tare da mayar da idonta kan system É—in gabanta,
"Kinyi kyau sosai,kada fa ki zautar mana da babban yayanmu a rasa gane kanshi,"
dariya sehrish tayi batare da tace komai ba,ta fuce daga dakin,
Babu kowa a falon,da alama duk sun tafi yin sallar magriba ne,tana cikin tafiya,kwatsam taji an ruƙo sumar kanta ta baya,a firgice ta juya don taga wanene,Gabanta ne ya faɗi rass!ganin Haroon kamar wani maye haka ya kama dogon gashin kanta,yakai shi izuwa saitin hancinsa yana shinshinar ƙamshinshi,
A wani irin tsorace sehrish ta buge hannunshi,sam batasan cewa zata hadu dashi ba,da batayi kuskuren fitowa daga dakinsu ba,batare da ta sanya mayafi ba,
Fuskarta a daure tace"Dan Allah menene haka"?
Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"Shauƙi,"
Harara ta watsa mashi,aranta tace"Mai hali bai ta6a canzawa dama saida raina ya bani cewa karyane tuban da yace mun yayi,"
Guntun tsoki taja,da hanzari ta juya zata wuce saman stairs din,aikuwa da sauri ya sha gabanta ƙiris ya rage ƙirjinta ya daki nashi,hakan ba ƙaramin daga mata hankali yayi ba,
"Ka bani wuri na wuce,banason wannan rashin wayon naka,Bakasan cewa ni matar aure bace,"
Ta6e bakinshi yayi tare da cewa"And then so what idan ke matar aure ce?Nafa son komai,auren yarjejeniya ne,mutumin nan fa da kika kwallafa rai akanshi ba sonki yake yi ba,Ni ne mosayinki,inason ki sosai,kuma ashirye nake dana aureki da zarar ya sake ki...."
Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,tuni idanuwanta suka cicciko da kwalla,ta tsani taji ance mata haka,
Ranta a matuƙar 6ace tace"Wlh koda ace mazan duniya sun ƙare duka kaf babu su,kai kaɗae ne ka rage sai dabbobi a cikinta,to na ƙwammace in auri Biri da in aure ka,"
Waro ido waje yayi yana kallonta a hasale yace"Ke!ni kike gayawa wannan maganar?baki da hankali ne?ki rasa dawa zaki haÉ—ani sai biri,kina nufin cewa biri yafi ni mahimmanci a wurinki"?
"Ƙwara shi dabbane,kaifa mutunne mai hali irin na dabbo...."_
Bata ƙarasa maganar ba,a fusace haroon ya sanya tafin hannunshi ya ɗauke ta da mari,Sae dai kafin ya janye hannunshi daga saman kuncin ta,yaji shima an dauke shi da wani irin zazzaffan mari,Kuma kafin yayi wani yunƙuri yaji tafukan hannaye again har biyu asaman fuskarshi,Tashin hankalin
Wasu irin baƙaƙen taurari ya gani acikin idanuwanshi,tsabar raɗaɗin da ya ji ne yasa shi sakin ihu,yana tangal tangal zai fadi,gaba daya duk yabi ya susuce,har fitsari sae da ya saki a wondonshi,saboda tsabar raɗaɗin daya ji,
A galabaice yace"Na shiga uku!Meke faruwa dani ne!dan Allah ataimakamin duhu cikin idanuwana,"
Shessheƙar kuka kawai sehrish keyi hannunta dafe da kuncinta,mutum biyu ne suka mari haroon,shigowarsu kenan Suka ganshi ya sharara mata mari,aikuwa da gudu Abusufyan ya ƙaraso ya kwashe shi da mari,Marshal Omar kuwa,Hannu biyu yasa ya ɗauke shi da Mari ta baya,hakan yasa yaji duuuuum acikin kunnanshi,babu wani sauti kwata kwata,kamar ya kurmance,
Ruko hannunta Marshal yayi"kiyi haƙuri kinji,dan Allah ki daina kuka," side hug yayi mata yana dan bubbuga bayanta,Abusufyan kuwa sam ya kasa magana sai faman huci yakeyi,ranshi yayi mugun 6aci,
"Banaso Sgr ya shigo yaji wannan aika aikar da haroon yayi,don wlh sai ya É—anÉ—ana kuÉ—arshi,Sehrish ki wuce bedroom É—inku,ki barni dashi,zaici ubanshi ne,"
.. Cikin shessheƙar kuka tace"Part din babban yaya zanje in gyara mashi"
Tayi maganar tare da wuce wa upstairs da sauri tana ci gaba da yin kukan,
"Uncle,dan Allah ka shiga daga ciki,Ni zanji dashi,"
Jinjina kai kawai Abusufyan yayi tare da juyawa yabar falon,
Kwakkwaran damƙa Marshal yayi ma wuyan rigar haroon dake a zube ƙasa yana birgima,ɗaɗɗago dashi yayi ya jashi,har izuwa ɗakin da suke hukunta mai laifi,lallai haroon ya ta6o ma kanshi,
Lokacin da sehrish ta faɗa cikin palourn shi,Saman sofa ta zauna tana cigaba da yin kukan,taji zafin marin da haroon yayi mata sosai,abun ya tsaya mata aranta,tsanarshi ta ƙara ninkuwa acikin zuciyarta,ta jima a zaune batare da ta motsa ba,har aka kira sallar isha'e,sae bayan da aka kammala sallar sannan ta miƙe ta wuce cikin bedroom ɗinshi,toilet ta fara shiga ta gyara mashi,kafin ta dawo bedroom ɗin nashi tana gyarawa,har lokacin bata daina yin shessheƙar kukan ba,
Bayan ta kammala gyara mashi part ɗin nasa,kasa tafiya tayi saboda a ƙagare take daya dawo,saboda tayi mashi maganar zuwansu kano,Addu'arta Allah yasa yabarta taje,
 Safa da marwa ta shiga yi acikin bedroom ɗin nashi,gajiya tafara yi da yin yawon,wuri ta samu daga gefen gadon ta zauna,gyangyaɗi ta fara yi a ƙarshe bacci ya kwasheta,bata ƙara sanin meke wakana ba,
*SGR*
 "Assalamu alaikum,mommy azeema"
On the other hand azeema tace"Daughter,kin ga saƙo na"?_
Murmushi jahad tayi kafin tace"Aunty azeema yanzu baki gane muryoyin mu?Jahad fa ce ba rishi ba,"
 Hajiya azeema tace"wlh naso in ɗauki muryarki,Ashe second daughter ce,To ya kike"?
 "Lafiya lou Alhamdulillah ina lafiya,"
 "Madallah,Amaryar junaid,"
Cike da jin kunya jahad tace"Aunty azeema waya faÉ—i zancen nan,"
  Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"oh kin manta matsayina a wurin daddynku ne?Ae shi da kanshi ya sanar dani,kuma naji daɗi wlh,Junaid zai samu kamilar mace wadda zata kula da rayuwarshi,"_
kayataccen murmushi jahad ta saki,ba ƙaramin daɗin maganar taji ba,
  "Ina fata zaki kula mana da bugun zuciyar mu?
 Dariya jahad tayi tana faɗin"in sha Allah,zan kula maku dashi,"
 Hajiya azeema tace"Yawwa My daughter,but akwai abunda nakeso na tattauna tare dake game da junaid!amma ki bari zan kira wayarki,ko zuwa anjima ne,"
 "To Aunty Allah yakaimu anjiman lafiya,"
 "Ameen daughter,ina sehrish ɗin take ne?inaso nayi magana da ita ne,"
 Jahad na ƙoƙarin bude baki tayi magana,sai ga sehrish ta fito daga toilet din,jikinta sanye da bathrobe,wankan marece tayi,dama duk in tana period,kusan sau uku take yin wanka,'
  Ganin wayarta a hannun jahad yasa ta tunkarota tana tambayarta wanene ya kirata,
 Mika mata wayar jahad tayi"kar6i nan,Mommy azeema ce keson magana dake"
 Jiki na rawa ta kar6i wayar,da sauri ta koma gaban mirror,ta zauna saman kujerar,sannan tayi mata sallama,
 "Daughter,ya ake ciki ne?ina fata kinga saƙona ko"?
..Sehrish tace"nagani,junaid ya kawomin su,nagode sosai,"
 "Yawwa,Zaki ga turarurruka aciki,Tun yanzu zaki fara amfani dasu,akwai wasu sirrika atattare dasu,sannan akwai mayuka na gyaran fata,dana gyaran gashi,Original ne,Cikin one week,kina fara amfani dasu zaki ga sauyi a jikinki,Sannan akwai sauran kayan da ba yanzu zakiyi amfani dasu ba,suna da haɗarin gaske,su kansu turarurrukan nan,Shu'umaine na gaske,Fisgar mutun sukeyi kamar magnet,ƙarfi ne dasu,duk in zaki shafasu ki bari sai in zaki part ɗinsa,idan ba haka ba gaskiya za'a iya samun matsala,"
 Natsuwa sehrish tayi tana sauraronta,sun jima suna waya kafin daga bisani su kayi sallama,
  Kasa yin amfani da turaren tayi,tsoranshi ma take ji,tunda taji ance fisgar mutun yake yi,kada ta jama kanta bala'e tana zaman zamanta lafiya,
  bata shafa turaren ba,Amma ta fara amfani da mayukan gyaran jikin,
 Shaf shaf ta shirya cikin Doguwar riga ta material black colour,mai zanen manyan flowers a jikinshi launin ash,rigar tabi shape ɗin jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba gaban mirror ta koma ta zauna,powder ta murza a fuskarta,Sannan ta shafa man baki,la66anta sae salƙi sukeyi,
  Bata yafa komai akanta ba,Iya sumar kanta ce data sauko har gadon bayanta,high hills ta zura a ƙafarta,
Kama hanyar fita daga É—akin tayi da sauri jahad tace"Ina zuwa?
"Zanje part É—in babban yaya ne,Inaso na gyara mashi ne,"
Murmushi jahad ta saki tare da mayar da idonta kan system É—in gabanta,
"Kinyi kyau sosai,kada fa ki zautar mana da babban yayanmu a rasa gane kanshi,"
dariya sehrish tayi batare da tace komai ba,ta fuce daga dakin,
Babu kowa a falon,da alama duk sun tafi yin sallar magriba ne,tana cikin tafiya,kwatsam taji an ruƙo sumar kanta ta baya,a firgice ta juya don taga wanene,Gabanta ne ya faɗi rass!ganin Haroon kamar wani maye haka ya kama dogon gashin kanta,yakai shi izuwa saitin hancinsa yana shinshinar ƙamshinshi,
A wani irin tsorace sehrish ta buge hannunshi,sam batasan cewa zata hadu dashi ba,da batayi kuskuren fitowa daga dakinsu ba,batare da ta sanya mayafi ba,
Fuskarta a daure tace"Dan Allah menene haka"?
Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"Shauƙi,"
Harara ta watsa mashi,aranta tace"Mai hali bai ta6a canzawa dama saida raina ya bani cewa karyane tuban da yace mun yayi,"
Guntun tsoki taja,da hanzari ta juya zata wuce saman stairs din,aikuwa da sauri ya sha gabanta ƙiris ya rage ƙirjinta ya daki nashi,hakan ba ƙaramin daga mata hankali yayi ba,
"Ka bani wuri na wuce,banason wannan rashin wayon naka,Bakasan cewa ni matar aure bace,"
Ta6e bakinshi yayi tare da cewa"And then so what idan ke matar aure ce?Nafa son komai,auren yarjejeniya ne,mutumin nan fa da kika kwallafa rai akanshi ba sonki yake yi ba,Ni ne mosayinki,inason ki sosai,kuma ashirye nake dana aureki da zarar ya sake ki...."
Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,tuni idanuwanta suka cicciko da kwalla,ta tsani taji ance mata haka,
Ranta a matuƙar 6ace tace"Wlh koda ace mazan duniya sun ƙare duka kaf babu su,kai kaɗae ne ka rage sai dabbobi a cikinta,to na ƙwammace in auri Biri da in aure ka,"
Waro ido waje yayi yana kallonta a hasale yace"Ke!ni kike gayawa wannan maganar?baki da hankali ne?ki rasa dawa zaki haÉ—ani sai biri,kina nufin cewa biri yafi ni mahimmanci a wurinki"?
"Ƙwara shi dabbane,kaifa mutunne mai hali irin na dabbo...."_
Bata ƙarasa maganar ba,a fusace haroon ya sanya tafin hannunshi ya ɗauke ta da mari,Sae dai kafin ya janye hannunshi daga saman kuncin ta,yaji shima an dauke shi da wani irin zazzaffan mari,Kuma kafin yayi wani yunƙuri yaji tafukan hannaye again har biyu asaman fuskarshi,Tashin hankalin
Wasu irin baƙaƙen taurari ya gani acikin idanuwanshi,tsabar raɗaɗin da ya ji ne yasa shi sakin ihu,yana tangal tangal zai fadi,gaba daya duk yabi ya susuce,har fitsari sae da ya saki a wondonshi,saboda tsabar raɗaɗin daya ji,
A galabaice yace"Na shiga uku!Meke faruwa dani ne!dan Allah ataimakamin duhu cikin idanuwana,"
Shessheƙar kuka kawai sehrish keyi hannunta dafe da kuncinta,mutum biyu ne suka mari haroon,shigowarsu kenan Suka ganshi ya sharara mata mari,aikuwa da gudu Abusufyan ya ƙaraso ya kwashe shi da mari,Marshal Omar kuwa,Hannu biyu yasa ya ɗauke shi da Mari ta baya,hakan yasa yaji duuuuum acikin kunnanshi,babu wani sauti kwata kwata,kamar ya kurmance,
Ruko hannunta Marshal yayi"kiyi haƙuri kinji,dan Allah ki daina kuka," side hug yayi mata yana dan bubbuga bayanta,Abusufyan kuwa sam ya kasa magana sai faman huci yakeyi,ranshi yayi mugun 6aci,
"Banaso Sgr ya shigo yaji wannan aika aikar da haroon yayi,don wlh sai ya É—anÉ—ana kuÉ—arshi,Sehrish ki wuce bedroom É—inku,ki barni dashi,zaici ubanshi ne,"
.. Cikin shessheƙar kuka tace"Part din babban yaya zanje in gyara mashi"
Tayi maganar tare da wuce wa upstairs da sauri tana ci gaba da yin kukan,
"Uncle,dan Allah ka shiga daga ciki,Ni zanji dashi,"
Jinjina kai kawai Abusufyan yayi tare da juyawa yabar falon,
Kwakkwaran damƙa Marshal yayi ma wuyan rigar haroon dake a zube ƙasa yana birgima,ɗaɗɗago dashi yayi ya jashi,har izuwa ɗakin da suke hukunta mai laifi,lallai haroon ya ta6o ma kanshi,
Lokacin da sehrish ta faɗa cikin palourn shi,Saman sofa ta zauna tana cigaba da yin kukan,taji zafin marin da haroon yayi mata sosai,abun ya tsaya mata aranta,tsanarshi ta ƙara ninkuwa acikin zuciyarta,ta jima a zaune batare da ta motsa ba,har aka kira sallar isha'e,sae bayan da aka kammala sallar sannan ta miƙe ta wuce cikin bedroom ɗinshi,toilet ta fara shiga ta gyara mashi,kafin ta dawo bedroom ɗin nashi tana gyarawa,har lokacin bata daina yin shessheƙar kukan ba,
Bayan ta kammala gyara mashi part ɗin nasa,kasa tafiya tayi saboda a ƙagare take daya dawo,saboda tayi mashi maganar zuwansu kano,Addu'arta Allah yasa yabarta taje,
 Safa da marwa ta shiga yi acikin bedroom ɗin nashi,gajiya tafara yi da yin yawon,wuri ta samu daga gefen gadon ta zauna,gyangyaɗi ta fara yi a ƙarshe bacci ya kwasheta,bata ƙara sanin meke wakana ba,
*SGR*