← Book details Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 91 OF 212

Sashe 91

Abban Sojoji Takun Karshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Yayi nisa acikin baccinshi yaji an ambaci sunanshi da ƙarfin gaske da wata irin murya mai matuƙar razanarwa,tashin hankali,A firgice junaid ya ware idanuwanshi shi kaɗae asaman gadonshi,Gabanshi ne ya faɗi rass!sakamakon Mutun daya gani tsaye agaban mirror ɗinshi sanye da baƙar jallabiya mai hula,a wani irin firgice junaid ya miƙe zaune tare da toshe kunnanshi ya fasa ƙara mai sautin gaske yana ambaton sunan Daddynsu maimaikon sunan Allah,
   Sosai ya shiga ja da baya,Hankalin shi a matuƙar tashe la66ansa na kerma ya shiga faɗin"Daddy!Mommy!Ya Rafayet!ya Omar!kuzo ku taimake ni!nashiga uku!dodo acikin ɗakina!Kashe ni zaiyi,'
   Ƙwayar idonshi tamkar zata faɗo waje saboda tsabar tsoro,
   Mutumin dake tsaye agaban madubin,wasu irin zaƙwa zaƙwan Akaifune a hannunshi,tsininsu tamkar na wuƙa,Ga uban gashi ajikin fatar hannunshi,juyowa yayi junaid na ganin fuskarshi ya rikirkice ya ruɗe,uban gashi ne ta ko'ina asaman fuskarshi,Ga wasu irin dogayen haƙora dake gareshi har sun sauko daga bakinshi,Idanuwanshi kuwa wa'iya zubilla,
  Gadan gadan ya tunkari junaid,A wani irin Sukwane,junaid ya wuntsilo daga saman gadon har yana tuntu6e wurin ƙoƙarin fitowa daga cikin bedroom ɗinshi,fisgar ƙopar yayi dama a buɗe ya barta,da gudun gaske ya fito tare da nufar bedroom ɗin Sgr yana kuka,Sai dai kafin ya ƙarasa wurin part din nashi,Sai ga wannan Mutumin ya bayyana,A gigice junaid ya fasa ƙara ya canza hanya ya nufi part ɗin marshal Omar,Nan ma kafin ya isa,Sai ga mutun ya ƙara bayyana,A galabaice ya sauko daga downstairs,bawan Allah Ya rasa wurin wa zashi,gashi duk ihun da yake yi yana kuka babu mai jin shi,
  *Junaid*!
Muryar jahad ce ta katse shi,da sauri ya juya wurin da sautin ya fito,a tsaye take tana kallonshi da gudun gaske ya nufeta tare da faɗawa jikinta ya ƙankameta yana faɗin"dodo!dodo!"
  
Bugun ƙafarshi da akayi ne yasa shi yin firgit ya farga daga baccin da yake yi,Duk zufa tabi ta jiƙa jikinshi sharkaf,kukan da yake yi acikin mafarkin har azahiri yake yinshi hannunshi rungume da pillow,
  Biji biji ya fara gani acikin eyes ɗinshi kafin idon nashi su washe,
  A hankali ya ambaci sunanta"Aunty Azmee,"yayi maganar tare da tashi daga zaune yana kallonta,
   "Meya faru dakai ne junaid?tunda nashigo nagan ka kana ta koke koke cikin bacci,"ajiyar zuciya ya sauke tare dakai idonshi kan wall clock ƙarfe 9 na safe,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,Ko sallar asuba baiyi ba,
  Cike da damuwa yace"Aunty Azmee wani mummunan mafarki nayi wallahi,Na tsorata sosai,Amma dana farka na ganki sae hankalina ya kwanta,Allah na gode maka da ya kasance ba gaske bane,da yanzu shikenan Na rasa rayuwata,"
   Zama azmee tayi daga gefen gadon mashi,cike da kulawa tace"Junaid!Anya kayi addu'a kafin ka kwanta bacci?
  girgiza mata kai yayi alamar a'a
"Ni nasani ae,tun lokacin baya nake fama dakai akan yin addu'ar bacci before ka kwanta,amma kaƙi jin maganata,"
  Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Aunty azmee,wlh inaso nima na dinga yin addu'ar,amma bansan meyasa ba,karatu baya zama cikin brain ɗina,bazan 6oye maki ba,ban iya komai ba,ko a karatun sallah iya surori biyarne akaina dasu nake yin sallah,amma bayansu wlh ban iya wani abu ba,komai na karanta bai zama acikin kaina,"
  Tsananin tausayinshi ne ya kama azmee,har cikin ranta ta damu da halin da junaid yake ciki,tana jinshi tamkar ɗan cikinta,
   "Junaid ita addu'a,zaka iyayinta da ko wani irin Yare,Allah yana ji kuma zai amsa maka ne,Inaso ka dage da yin addu'a,nima kuma zan tayaka in sha Allah,"
  Ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba,
"In sha Allah Aunty Azmee zan dage da addu'a,nagode sosai da irin kulawar da kike bani,"
  Murmushi azmee ta saki tare da cewa"kada ka manta fa,nifa na shayar dakai,Na so ka sosai junaid,tun lokacin da kana jinjirinka,ban mantawa Abban ku ya ke kawomin kai,
yini kake a wurina,lokacin yayyanka na zuwa aiki wasu kuma ba su kammala secondary ba,mu kaÉ—ai muke kasancewa acikin gidan,Inyi maka wanka,in shafe maka jikinka da mai in gyara maka sumar kan ka,sannan in canza maka kaya,idan na kammala yi maka wannan,sai in shayar da kai,har bacci ya É—auke mu saman gado,Kasan me"?
  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"a'a sai kin faɗa,"
  Taci gaba da cewa"idan na farka naga babu kai a kusa dani kamar in zauce...."
  "Saboda me"?Yayi tambayar da ɗan mamaki a fuskarshi,
   "Saboda na tsani araba ni dakai,Su fawan da zarar sun dawo daga school,har ɗakina suke zuwa su ɗauke ka,"
  Fashewa yayi da dariya sosai har dimples ɗinshi suka lotsa,Bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ni bansan meyasa kowa ke sona ba,Ina da farin jini sosai,ko yau muka haɗu da mutun cikin ƴan mintina sai ki ji yace ina burgeshi,"yayi maganar with proud,
  Murmushi Azmee ta saki,kafin tace"Because of ur Glamorous personality,kana da kyakkyawar zuciya,shiyasa ka ke sace zuciyar mutane cikin ƙankanin lokaci,"
..cike da zolaya yace"Shiyasa jahad ta zauce akan sona,"yayi maganar yana dafe saitin heart dinshi,
  Dariya azmee tayi tare da miƙewa tsaye tana cewa"Ga breakfast can yana jiran ka a dining,Jahad ba ta nan balle ta kawo maka a ɗakinka
  Dafe saitin zuciyarshi ya kuma yi hankali a ɗan tashe yace"Aunty Azmee kina nufin cewa,Juliet dina bata nan?yanzu saida Uncle Abusufyan ya tafin mu da ita ko"?a shagwa6e ya ƙarasa maganar yana ɗan bubbuga ƙafarshi,har cikin ranshi baiso tafiyar jahad ba,Yaci burin su fita shan ice cream yau,
  Fucewa Azmee tayi daga cikin ɗaƙin tana dariya,
  Saukowa yayi daga saman gadon jiki asanyaye ya wuce cikin toilet,

*Boss Bature*

  ❤🤍❤

*Marshal Omar*

Fitowar shi kenan daga cikin toilet,Waist dinshi É—aure da towel hannunshi kuma na ruke da wani short yana goge ruwan dake É—iÉ—É—igowa daga jikinshi,
  "Ya Omar"muryar hosana yaji acikin kunnanshi,da sauri ya juya don yaga ko itace,Kwance ya sameta saman gadonshi ko kayan baccinta bata cire ba,
  Cike da mamaki yace"Kee!me kike yi acikin bedroom ɗina"?
   "Ya Omar nifa zuwa nayi kawai don na gaishe ka"tayi maganar a ɗan shagawa6e,
   "Haka ya dace kizo gaishe dani?ko sallama babu,kawai sai dai na fito daga toilet na same ki a kwance saman gadona,"Yayi maganar fuskarshi aɗan daure,
  Murguɗa mashi baki tayi tare da cewa"Ae ɗakin Mijina ne"
  Harara ya watsa mata"waye mijin naki?Allah ya kiyaye in auri mai ɗan kai irin naki,"
  Gwalo tayi mashi tare da cewa"Oho dai,a haka ka gani kuma kake so,"_
  ƙiris ya rage ya fashe da dariya,amma sai yayi saurin kawar da dariyar don kada taga kamar ma wasa yake yi mata,
   "Get out from my bedroom!"a ɗan tsawace yayi maganar tare da nuna mata hanyar fita daga bedroom ɗin,
  Maƙe mashi kafaɗa tayi,"Wlh ba inda zani ya Omar,Kazo ka ɗauke ni,ka fitar dani idan ba ka son gani na,"
  girgiza kai kawai yayi tare da ƙarasawa gaban mirror dinshi,
   "Kaya fa zansa,pls ki fita daga waje idan na kammala saiki dawo,kin ji My baby"
   "Ae wlh ba inda zani je,Ae ba wani abu bane don ka sanya kaya agabana,tunda aure zamuyi,"
  Shiru yayi bai kara tanka mata ba,
Jin yayi banza da ita yasa ta kuma cewa"Ya Omar"shiru yaƙi amsa mata kiran nata,
  Ci gaba da magana tayi"Wai ya Omar,idan munyi aure,to taya zamu haihu muma"?
  Banza yayi bai tanka mata ba,
Bata damu da hakan ba,sai ma ci gaba da maganar tayi,
  "Ya Omar,kana ganin nima zan iya haihuwa?Kuma ma Taya za'ae na samu cikin"?
  Hauka maganinka Allah,ya furta hakan acikin Zuciyarshi,
   "Ji ya Omar ina magana ka wani share ni,idan baka faɗamun ba,to taya zan sani,"?
  Ƙin tanka mata yayi,a hasale tace"Shikenan tunda ba zaka bani Amsa ba,wlh idan Daddy ya dawo zanje in tambayeshi ne,don ni bazan bari ayi abun kunya ba,Ayi mun aure bansan komai ba,
  A ƙule ya juyo tare da kallonta yace"Ke,Tashi ki fuce mun daga ɗaki"
  Maƙe mashi kafaɗa ta kuma yi"anƙi a fita Ya omar,"
  Abun ya ɗaure mashi kai,ita ko shakkarshi bata ji,neman ma abunda zata yi mashi ya bugeta take yi don tasan cewa bazai iya ta6a lafiyar jikinta ba,
  "Idan kanaso in fita cikin lalama,to ka fara faɗamun taya zan samu ciki idan munyi aure"
  "Shine abunda kikeson sani"?yayi tambayar yana kallonta hadi da dage mata gira,ɗaga mashi kai tayi alamar eh,
Aikuwa Nan take ya sanya hannunshi ya zame towel É—in daya É—aure qugunshi dashi,
  Tashin hankali! A gigice Hosana ta fasa wata irin razananniyar ƙara,Kafin kace me kamar walkiya haka tabar ɗakin da gudu tana kuka,ta firgita sosai
  Mayar da towel ɗin yayi ya ɗaure waist ɗin sosai,sai faman tiƙar dariya yake yi,har da dafe cikinshi,
  "Maganinki kenan,nasan daga yau ba zaki sake yi mun irin wannan question ɗin ba,Yarinya sai kace mai iskokai,Ni bansan ya zan ƙare da ita ba,A haka dai nakeso,kuma zan kula da abuna"ya ƙarasa zancen zucin fuskarshi ɗauke da murmushi ya wuce wurin wardrobe ɗinshi,sai daga baya ya dinga tunanin kada hosana fa taje ta faɗa ma wani abunda ta gani tunda ba hankali gareta ba,Tuna wannan yasa yayi saurin ɗauko jallabiya ya zura ajikinshi,da sauri ya sauko downstairs yana nemanta,
Chapter 91 · 0% Book details