Sashe 99
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
shaƙar da yaymin cikin rahamar UBANGIJI na samu damar lalubar bed side drawer da naji a kusa da hannuna, kofin da boss yasha ruwa ban fiddaba yana a kai na jiyo, ALLAH ya bani sa'a fisgosa na ɗaga hannuna dake rawa da ƙyar na maka masa a gefen kunnensa. A take ya sakarmin wuya yana huci na shigar zafi..... Kafin ya dawo hayyacinsa na caka masa sauran kofin dake riƙe a hannun nawa, sai dai bansa a inane ba dan a kwai duhu a ɗakin har yanzun. ƙara ya saki yana sake kaimin wawura sai dai na zille harma na dire a gadon. Cafkoni yay cikin zafin nama ya maidoni baya kan gadon har saida nai ƙara dan azaba nima. Na gallama hannunsa cizo tare da halbinsa da ƙafa cikin salon trianing ɗin da muka samu duk da ba ganinsa nake ba. kokawa ce ta kaure a tsakanina da shi dukda yafi ƙarfina nesa ba kusaba. Amma kasancewar akwai taimakon UBANGIJI da kuma kowa yasan mata ALLAH kan bamu ƙarfi a irin wannan yanayin koda ace bazamu iya ƙwatar kanmuba kuwa. Kokawa muke bil haƙƙi da gaskiya dukda nice keshan wahala ban yarda ya kaini ƙasa ba. Cikin sa'a na kama ɗan yatsan hannunsa da yake neman sake kaiwa wuyana na murɗesa da azabar ƙarfi nai baya dashi. Jikake ƙaraƙassss ƙasss ƙasss ƙashin na bada sauti. Wahalalliyar ƙarar daya saki yay baya ta bani damar jan hannuna baya nima, sai na saɓulo da zoben dake jikin yatsan.
A take Ɗakin ya ɗauki sautin wata murya mai ban tsoro da saka firgici, aka shiga faman faɗin, “Barmata shine kuskure mafi girma, ka karɓa maza ka fita karka tsaya akwai matsala!!”.
Wani irin ɗagowa yay a zabure ya fisgoni muka tafi ƙasa tare ya murɗe hannuna da zoben ke a ciki zai ƙwace. Hakan yasa na shiga ambaton,
حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ.
Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel.
(ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro).
اَللَّهُمَّ اكْفِنِيهِمْ بِمَا شِئْتَ.
Allahummak finihim bima shi'ita.
(Ya ALLAH! Ka isar mini su da abin da Ka so).
اَللَّهُمَّ لاَ سَهْلَ إِلاَّ مَا جَعَلْتَهُ سَهْلاً وَأَنْتَ تَجْعَلُ الْحَزْنَ إِذَا شِئْتَ سَهْلاً.
Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahlan, wa anta taj'alu-l-hzana idha shi'ta sahlan.
(Ya ALLAH! Babu wani abu mai sauki sai abin da Ka sanya shi ya zama mai sauki, kuma Kai kana sanya tsanani idan Ka so ya zama sauki).
Ƙarar da aka ƙwallah ta sakashi Hankaɗani kaina ya daki gadon, ya fita da gudu, na fasa wani irin gigitaccen ihu jikina na ɗaukar wani irin rawa, a take komai yay min ɗifff.......
Fasa ƙarar Bilkisu tai dai-dai da ƙarasowar Jay jikin ƙofar falon zai buɗe dan isowarsa gidan kenan bayan yakai Ɓaleru ya ajiye a wani ɓoyayyen waje. cikin zafin nama ya faɗa falon batare da ya rufe ƙofar ba. Ledar dake hannunsa ma sakinta yay a falon. A gigice ya danna makunnar fitilar ɗakin ta kawo haske. Ya daka wani uban tsalle sai gashi gaban Bilkisu data sume. Da ƙarfi ya ƙwala kiran sunanta jikinsa na rawa dan har yanzu yana tattare da fushin ɓaleru ne, yay saurin maidata ya kwantar jin kamar gudun mutum ta bayan Windown ɗakin. Fita yay da gudu yana ƙwalama maigadi kira cikin matsanancin hargagi akan ya rufe masa gate. sosai maigadi dahar ya shiga ɗakinsa zai kwanta ya fito a gigice shima jin wannan mafaraucin kira, baƙaramin tashin hankali ya shigaba ganin yanda Jawaad yake nufosa tamkar mahaukacin zakin dake a yunwace. Ɗaukesa Jay yay da mahaukacin mari, “Waye ya shigomin gida? Ka gayamin wa kabama damar ya shigomin gida!!?”.
Maigadi daya gama ruɗewa da marin da yasha yace, “Wlhy oga babu wanda ya shigo gidannan tunda ka fita, narantse maka babu wanda ya shig........” bai gama saurarensaba ya bar wajen, ta bayan Windows ɗinsu ya nufa kasancewar akwai wuta ko ina da haske. Take masa baya mai gadi yay da sauri shima dan bai fahimci abinda ke faruwa ba. Jay yaja wani mahaukacin birki yana kallon tsanin dake tsaye jikin katanga alamar koma wanene tanan ya shigo, kuma tanan ya fita. Naushi ya kaima bango da azabar ƙarfi yana faɗin, “Noooo!!”. Da sauri maigadi dake cikin tsoro ya riƙe masa hannu, “Oga dan ALLAH karka jima kanka ciwo”. Fisge hannunsa yayi dayin wani Uban tsalle ya ɗane katangar cikin ƙwarewar training da su
ka samu batare da ya kalli inda tsanin ya keba. Dirarsa can baya kawai maigadin yaji. “Na shiga uku ni gambo, mike faruwa a gidan wai?” mai gadi ya faɗa hankali tashe.
Babu abinda Jay ya gani sai sayin takalmi kawai da wani tsanin a baya, wajen siririyar hanyace data fita ɗoɗar har babban titi, hanyar tana taimakawa ƴan anguwarne wajen fita titi basai sunbi ta titin layinba dake da nisa da babban titi, ya dafe kansa dake wani irin masifar sara masa. Halin daya bar bilkisu a cikine ya faɗo masa a rai. Ya fiddo wayarsa a aljihu ya shiga haske-haske harya zagaya ta ƙofar gate yay knocking. Koda aka buɗe baiko kalli maigadi dake neman ƙarin bayani ba ya nufi cikin gidan.
Yanda ya barta haka ya Koma ya sameta babu alamar numfashi tattare da ita. Tsugunnawa yay gabanta ya Rungumota da ƙarfi cikin ƙirjinsa jikinsa na wani irin tsuma na tsananin ɓacin rai, “Ubanwaye ya shigomin gida? Miyay miki?”. Yay maganar cikin raunin murya da ɗaci, jijiyoyin kansa na miƙewa ruɗu-ruɗu, zafafan hawayene ke kwarara a cikin zuciyarsa, a zahiri kam babu ko ɗigonsu sai idonsa daya kaɗa yay jazur. Ɗagata yay gaba ɗayanta ya ɗaura a kujerar dake ɗakin guda ɗaya ƴar doguwa, sai da ya gama bin ɗakin da kallo tsaf, ɗigon jini har a kan gadon ya gani, sai fasashen glass aƙasa zuwa gadon dake a yamutse alamar ansha dabbe a kansa. Kauda kansa yay yana rumtse ido da danne abinda ke yinƙuro masa tamkar zai faso ƙirjinsa ya fito mai alaƙa da Masifaffen kishi, sauran ruwan daya bari dake yashe a ƙasa ya ɗauka, a hannu ya zuba ya shafa mata a fuska. A take ta kawo wani nannauyan numfashi tare da miƙewa zumbur cikin zafin nama tana faɗin, “Saina kasheka, bazan barkaba yau, kasheka zanyi wlhy......” Saurin riƙe hannunta da take ƙoƙarin kaiwa wuyansa yayi da ƙarfi ya mannata jikinsa yana faɗin, “Kwantar da hankalinki ki nutsu nine”.
Ƙamshin turarensa da naji ya sakani fashewa da kuka na ƙanƙamesa, “Boss shine, wlhy shine ke bibiyata tun a gidan Dad wai sai yamin fyaɗe, ya ɗau alwashin saiya ketamin mutuncina, yace nice cikar burinsa, saiya yimin yanda yayma su Amina, na shiga y......” ɗagota yay da sauri jikinsa na kakkarwa ya manne bakinsa da nata, sam baya buƙatar ji, bayason yaji komai a yanzu, zuciyarsa zata iya tarwatsewa idan ta cigaba da faɗa bazai iya ɗauka ba, yanada kishi mai tsanani akan dukkan abunda ya kasance nasa. hawayen da tun ɗazun yake fatan yinsu sunƙi suka shiga silalo masa a kumatu yanzun, yanda yake matan kawai zai baka tabbacin ba'a hayyacinsa yake ba. Yaja kusan mintuna biyar yana kissing ɗinta, tun tana ƙoƙarin son ƙwacewa harta nutsu ta miƙa wuya, dan ta kula da fushi yake sumbatarta. hawayensu ne masu ɗumi ke sauka bisa fuskokin juna. Saida yaga tayi laƙwasa sannan ya zare bakinsa cikin nata da sake rungumeta yana haɗiyar zuciya tamkar numfashinsa zaibar ƙirjinsa. Yanda ƙirjinsa ke sama da ƙasa sosai ya firgita Bilkisu, sai dai tai luf a jikinsa tana kuka dan dukkan abinda ya faru a waɗancan ranakun a yanzu tsaf suke dawo mata tamkar yanzune komai ke faruwa. Ɗaukarta yay gaba ɗayanta ya nufa ɗakinsa da ita, kai tsaye bayi ya zarce. Tanason tai magana sai dai babu fuska, dan haka ta nutsu shiru tanata share hawaye da sauke ajiyar zuciya. Ruwa ya haɗa mai ɗumi sosai ya nuna mata alamar tai wanka ya fice.
Binsa nai da kallo harya fice sannan na maida idona ga hannuna dake a rumtse, zobene mai azabar ƙyau da ɗaukar ido dana samu zamewa hannun tsinannen nan. Na maida hannun na rumtse ina cigaba da zubar da hawayen, mamaki nake a raina miyasa wancan zuwan da yaymin a gidan Dad ban taɓa tunawabama balle na sanarma wani? Nida sam bani da mantuwa amma gashi wannan ban taɓa tunawaba sai yau? Ko yaya akai hakan ta faru?. Da wannan zoben rumtse cikin hannuna nai wankan, da gasa jikina kawai nayi da ruwan daya haɗamin kafin nai amfani da sosonsa sama-sama dan wani irin ƙyanƙyami da takaicin raɓar jikina da la'anannen can yayi nakeji.
Jay Ɗakinta ya sake komawa. Bai taɓa komaiba bayan kayan barci daya ɗauka mata ya kashe fitar ya rufo ɗakin. Ledar daya yasar a fali ya ɗauka ya koma ɗakinsa.
ina kammala
A take Ɗakin ya ɗauki sautin wata murya mai ban tsoro da saka firgici, aka shiga faman faɗin, “Barmata shine kuskure mafi girma, ka karɓa maza ka fita karka tsaya akwai matsala!!”.
Wani irin ɗagowa yay a zabure ya fisgoni muka tafi ƙasa tare ya murɗe hannuna da zoben ke a ciki zai ƙwace. Hakan yasa na shiga ambaton,
حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ.
Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel.
(ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro).
اَللَّهُمَّ اكْفِنِيهِمْ بِمَا شِئْتَ.
Allahummak finihim bima shi'ita.
(Ya ALLAH! Ka isar mini su da abin da Ka so).
اَللَّهُمَّ لاَ سَهْلَ إِلاَّ مَا جَعَلْتَهُ سَهْلاً وَأَنْتَ تَجْعَلُ الْحَزْنَ إِذَا شِئْتَ سَهْلاً.
Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahlan, wa anta taj'alu-l-hzana idha shi'ta sahlan.
(Ya ALLAH! Babu wani abu mai sauki sai abin da Ka sanya shi ya zama mai sauki, kuma Kai kana sanya tsanani idan Ka so ya zama sauki).
Ƙarar da aka ƙwallah ta sakashi Hankaɗani kaina ya daki gadon, ya fita da gudu, na fasa wani irin gigitaccen ihu jikina na ɗaukar wani irin rawa, a take komai yay min ɗifff.......
Fasa ƙarar Bilkisu tai dai-dai da ƙarasowar Jay jikin ƙofar falon zai buɗe dan isowarsa gidan kenan bayan yakai Ɓaleru ya ajiye a wani ɓoyayyen waje. cikin zafin nama ya faɗa falon batare da ya rufe ƙofar ba. Ledar dake hannunsa ma sakinta yay a falon. A gigice ya danna makunnar fitilar ɗakin ta kawo haske. Ya daka wani uban tsalle sai gashi gaban Bilkisu data sume. Da ƙarfi ya ƙwala kiran sunanta jikinsa na rawa dan har yanzu yana tattare da fushin ɓaleru ne, yay saurin maidata ya kwantar jin kamar gudun mutum ta bayan Windown ɗakin. Fita yay da gudu yana ƙwalama maigadi kira cikin matsanancin hargagi akan ya rufe masa gate. sosai maigadi dahar ya shiga ɗakinsa zai kwanta ya fito a gigice shima jin wannan mafaraucin kira, baƙaramin tashin hankali ya shigaba ganin yanda Jawaad yake nufosa tamkar mahaukacin zakin dake a yunwace. Ɗaukesa Jay yay da mahaukacin mari, “Waye ya shigomin gida? Ka gayamin wa kabama damar ya shigomin gida!!?”.
Maigadi daya gama ruɗewa da marin da yasha yace, “Wlhy oga babu wanda ya shigo gidannan tunda ka fita, narantse maka babu wanda ya shig........” bai gama saurarensaba ya bar wajen, ta bayan Windows ɗinsu ya nufa kasancewar akwai wuta ko ina da haske. Take masa baya mai gadi yay da sauri shima dan bai fahimci abinda ke faruwa ba. Jay yaja wani mahaukacin birki yana kallon tsanin dake tsaye jikin katanga alamar koma wanene tanan ya shigo, kuma tanan ya fita. Naushi ya kaima bango da azabar ƙarfi yana faɗin, “Noooo!!”. Da sauri maigadi dake cikin tsoro ya riƙe masa hannu, “Oga dan ALLAH karka jima kanka ciwo”. Fisge hannunsa yayi dayin wani Uban tsalle ya ɗane katangar cikin ƙwarewar training da su
ka samu batare da ya kalli inda tsanin ya keba. Dirarsa can baya kawai maigadin yaji. “Na shiga uku ni gambo, mike faruwa a gidan wai?” mai gadi ya faɗa hankali tashe.
Babu abinda Jay ya gani sai sayin takalmi kawai da wani tsanin a baya, wajen siririyar hanyace data fita ɗoɗar har babban titi, hanyar tana taimakawa ƴan anguwarne wajen fita titi basai sunbi ta titin layinba dake da nisa da babban titi, ya dafe kansa dake wani irin masifar sara masa. Halin daya bar bilkisu a cikine ya faɗo masa a rai. Ya fiddo wayarsa a aljihu ya shiga haske-haske harya zagaya ta ƙofar gate yay knocking. Koda aka buɗe baiko kalli maigadi dake neman ƙarin bayani ba ya nufi cikin gidan.
Yanda ya barta haka ya Koma ya sameta babu alamar numfashi tattare da ita. Tsugunnawa yay gabanta ya Rungumota da ƙarfi cikin ƙirjinsa jikinsa na wani irin tsuma na tsananin ɓacin rai, “Ubanwaye ya shigomin gida? Miyay miki?”. Yay maganar cikin raunin murya da ɗaci, jijiyoyin kansa na miƙewa ruɗu-ruɗu, zafafan hawayene ke kwarara a cikin zuciyarsa, a zahiri kam babu ko ɗigonsu sai idonsa daya kaɗa yay jazur. Ɗagata yay gaba ɗayanta ya ɗaura a kujerar dake ɗakin guda ɗaya ƴar doguwa, sai da ya gama bin ɗakin da kallo tsaf, ɗigon jini har a kan gadon ya gani, sai fasashen glass aƙasa zuwa gadon dake a yamutse alamar ansha dabbe a kansa. Kauda kansa yay yana rumtse ido da danne abinda ke yinƙuro masa tamkar zai faso ƙirjinsa ya fito mai alaƙa da Masifaffen kishi, sauran ruwan daya bari dake yashe a ƙasa ya ɗauka, a hannu ya zuba ya shafa mata a fuska. A take ta kawo wani nannauyan numfashi tare da miƙewa zumbur cikin zafin nama tana faɗin, “Saina kasheka, bazan barkaba yau, kasheka zanyi wlhy......” Saurin riƙe hannunta da take ƙoƙarin kaiwa wuyansa yayi da ƙarfi ya mannata jikinsa yana faɗin, “Kwantar da hankalinki ki nutsu nine”.
Ƙamshin turarensa da naji ya sakani fashewa da kuka na ƙanƙamesa, “Boss shine, wlhy shine ke bibiyata tun a gidan Dad wai sai yamin fyaɗe, ya ɗau alwashin saiya ketamin mutuncina, yace nice cikar burinsa, saiya yimin yanda yayma su Amina, na shiga y......” ɗagota yay da sauri jikinsa na kakkarwa ya manne bakinsa da nata, sam baya buƙatar ji, bayason yaji komai a yanzu, zuciyarsa zata iya tarwatsewa idan ta cigaba da faɗa bazai iya ɗauka ba, yanada kishi mai tsanani akan dukkan abunda ya kasance nasa. hawayen da tun ɗazun yake fatan yinsu sunƙi suka shiga silalo masa a kumatu yanzun, yanda yake matan kawai zai baka tabbacin ba'a hayyacinsa yake ba. Yaja kusan mintuna biyar yana kissing ɗinta, tun tana ƙoƙarin son ƙwacewa harta nutsu ta miƙa wuya, dan ta kula da fushi yake sumbatarta. hawayensu ne masu ɗumi ke sauka bisa fuskokin juna. Saida yaga tayi laƙwasa sannan ya zare bakinsa cikin nata da sake rungumeta yana haɗiyar zuciya tamkar numfashinsa zaibar ƙirjinsa. Yanda ƙirjinsa ke sama da ƙasa sosai ya firgita Bilkisu, sai dai tai luf a jikinsa tana kuka dan dukkan abinda ya faru a waɗancan ranakun a yanzu tsaf suke dawo mata tamkar yanzune komai ke faruwa. Ɗaukarta yay gaba ɗayanta ya nufa ɗakinsa da ita, kai tsaye bayi ya zarce. Tanason tai magana sai dai babu fuska, dan haka ta nutsu shiru tanata share hawaye da sauke ajiyar zuciya. Ruwa ya haɗa mai ɗumi sosai ya nuna mata alamar tai wanka ya fice.
Binsa nai da kallo harya fice sannan na maida idona ga hannuna dake a rumtse, zobene mai azabar ƙyau da ɗaukar ido dana samu zamewa hannun tsinannen nan. Na maida hannun na rumtse ina cigaba da zubar da hawayen, mamaki nake a raina miyasa wancan zuwan da yaymin a gidan Dad ban taɓa tunawabama balle na sanarma wani? Nida sam bani da mantuwa amma gashi wannan ban taɓa tunawaba sai yau? Ko yaya akai hakan ta faru?. Da wannan zoben rumtse cikin hannuna nai wankan, da gasa jikina kawai nayi da ruwan daya haɗamin kafin nai amfani da sosonsa sama-sama dan wani irin ƙyanƙyami da takaicin raɓar jikina da la'anannen can yayi nakeji.
Jay Ɗakinta ya sake komawa. Bai taɓa komaiba bayan kayan barci daya ɗauka mata ya kashe fitar ya rufo ɗakin. Ledar daya yasar a fali ya ɗauka ya koma ɗakinsa.
ina kammala