← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 168

Sashe 92

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 3 min read

kasance a gareta ba”. Ajiyar zuciyar Dad da Mom suka sauke lokaci guda, Doctor ya cigaba da faɗin, “Sai dai wani ƙari ya fito a bakin mahaifar, a hankali kuma zai rinƙa girma inhar ba'ai mata aiki ba, zaita girmane cikinta na girma kamar mai ciki, idan tsautsayi yasa ya fashe kuma sai ta ringa zubar da ruwa mai wari”. Idanu a waje cike da tsoro su Dad suke kalon Doctor, cikin rawar baki Dad yace, “Likita amma ai kace ana cirewa?”. “ƙwarai Alhaji ana cirewa, sai dai itamafa cirewar nada nata haɗarin, dan zaku iya rasata a dalilin cirewar, idan kuma an dace za'a cire lafiya ta tashi”. Kuka Mom ta fashe dashi iya ƙarfinta, shi kansa Dad dauriya kawai yakeyi, amma kallo ɗaya zakai masa ka fahimci tsagwaron tashin hankalinsa. Murya a sanyaye yace, “Wannan itace kaɗai mafitar Doctor?”. Doctor yace, “Eh to akwai wata mafitar bayan wannan”. Cikin rawar jiki Mom tace, “Wacece Doctor faɗa mana ita dan ALLAH”. “Hajiya mafitar ƙarshe itace shan magani, zamu iya bata maganin da zata shashi a sati sau ɗaya, ya kama a wata guda sau huɗu kenan, sai dai yanada matuƙar tsada, sannan zata cigaba da shansane har illa masha ALLAH, amfanin shansa anan bazai bar wannan ƙarin ya cigaba da girmaba, sannan bazata sake samun cikiba sai abinda ALLAH ya ƙaddara wannan ikonsane da rahamarsa idan yaso, nidai iya hasashena na faɗa sanin gaibu kuma sai ALLAH”.

________________________________

Knocking ƙofa da akeyine ya saka Jawaad farkawa, guntun tsaki yaja yana buɗe idanunsa akan agogon ɗakin nasa, ƙarfe goma harda mintuna sha bakwai, ya ɗan lumshe idanu ya sake buɗewa kafin ya tashi zaune da ƙyar. Lallai yasha barci sosai ashe. Sauka yay daga gadon ya nufi toilet, fuska ya wanko ya kuskure baki ya fito, jallabiyar da yaje masallaci ya ɗauka ya zira.

A falo suka haɗu da Bilkisu wadda itama bugun ƙofarne ya tasheta, nbatare da ita tama gansaba ta buɗe ƙofar. Nabeelah ce ɗauke da basket.

Murmushi nai mata ina matsawa na bata hanya ta shigo tana ƴar dariya damin shaƙiyanci. “Ta wajena naga duk kinyi wani laushi, ko Yayanmu ya angwanc..........”

Jin tayi shiru tare da jan biriki bata ƙarasaba ya sani maida ƙofar na rufe na juyo. zaune yake saman kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yay bala'in ɗaure fuska da tsatstsareta da idanunsa masu ban tsoro ga marajin magana. Ba itaba hatta ni saida na tsume, dan a bazata na gansa tunda sanda na wuce ban ganshi a wajenba.

Yaƙi cewa komai kuma yaƙi daina kallonta, a hankali takai ƙasa ta durƙusa kamar wata munafuka, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Yayanmu ina kwana”. Bai amsa mataba, sai sake ɗaure fuska da yay yace, “Ƙarasa abinda kika fara”..................✍

ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.

SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;

ƊAURIN ƁOYE

ALƘAWARIN ALLAH.

HAFSAT RANO tazo muku da;

SAUYIN ƘADDARA

ƊAURIN GORO

MAMU GEE tazo muku da;

BURI ƊAYA

ƘAUNAR MU.

MISS XOXO tazo muku da;

KAIMIN HALACCI

IGIYAR ZATO.

BILYN ABDULL tazo muku da;

WUTSIYAR RAƘUMI...

GUDU DA WAIWAYE....

abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.

Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899

sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823

Hafsat Kabir Umar GTB.

Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300

Sai kunzo😍😍😍😘.

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.

.

.

Domin samun littafin Ƙwai cikin ƙaya daga farkon ko taɓa Link ɗin da ke ƙasa.

👇👇👇👇

.

https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Typing📲

ƘWAI cikin ƘAYA!!

Bilyn Abdull ce🤙🏻

BOOK TWO
Chapter 92 · 0% Book details