← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 168

Sashe 57

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

da nawa, tabbas nine na canja takardar da akaba Imam da tawa a lokacin da yake ƙoƙarin shiga massallaci.. Bayan duk an kawomin bayanai akan shirin da sukai na cutar da yarinyar saina shiga nazarin neman hanyar daya dace na hana faruwar mummunan ƙudirinsu, a kaf hanyar danake gani zata zama yarinyar za'a sake cutarwa, dan haka daga ƙarshe sai na yanke shawarar bin hanyar da suma sukabi, wato ta ƙarƙashin ƙasa. Imam idan har baka mantaba bayan isowarka massallaci wani yazo ya sameka akan batun wani aure, har ya roƙi afuwa akan rashin kawowa da wuri, kaikuma ka amshi uzirinsa tare da bashi takardar list ɗin sunayen waɗanda za'a ɗaurama aure a ranar kace ya rubuta sunayen waɗanda yazo dasu a gurin, to ba kowa bane face ni, da wannan damar nai amfani na canja takardarma baki ɗaya bayan na kwafe sunayen dake can nakuma canja namu a yanda naso”.
          Salati manyan suka sanya da wannan al'amari, yayinda Cikin ƙaraji Qaseem yace, “ Momy!!!, mikuke nufi da hakan da kukayi to? Minai muku da zafi haka kuka zaɓi zalintata ni da Bilkisu?!, to wlhy, na rantse da ALLAH, ku kwana da sanin...........” da sauri Momy ta rufe masa baki, sauran ƙarfinsa da wanda ɓacinrai ya kawo masa yanzu ya tattara ya hankaɗe Momy gefe ta faɗi. Jawaad ne yay saurin miƙewa yana faɗin, “Qaseem minene haka? Baka da hankaline?”.
         “Eh bani dashi kaikuma? Idan kai haƙuri kaima ina tafe kanka,  garama kayi gaggawar sakarmin mata kafin kanema numfashinka a ƙirji ka rasa”.
      Wani banzan kallo Jawaad yay masa, kafin ya bashi amsa Shahudah ta katsesu da jehoma duk wanda ke falon tambaya cike da rashin kunya. “Kai broth kamaji munafukan da suka ƙulla maka naka makircin, nikuma saiku faɗamin wanene Habib yake koma wane oho muku, kaikuma Bb kai gaggawar sakin waccan ƴar iskar yarinyar tamaje ta auri Uban Qaseem a yanzu wannan bai dameniba dan kaina kawai na sani, gwarama kowa yasan abinda zanyi sai yafi naka ɗaga hankalin kowa dake gidanan wlhy”.
        Jin komai ya warware Imam da tawagarsa suka miƙe domin tafiya, a ganinsu wannan matsalace ta cikin gida, sukam tunda sun fita gara su kama gabansu. Godiya su Alhaji baba sukai musu sannan suka fice.
         A take falon ya kaure da hayaniya har babu maijin maganar ɗan uwansa, Jawaad na shirin ficewarsa Shahudah dake kuka tana zubama mutane rashin kunya tai saurin riƙoshi, “Wlhy bazaka fitaba saika saki tsinanniyarnan bb”. Bai tanka mataba, sannan kuma bai juyoba, sai ƙoƙarin fisgar jikinsa da yay zai fice abinsa. Ƙara Shahudah ta ƙwalla wadda ta dawo da duk hankalin ƴan falon kansu, sosai ran Jawaad ke tafasa, ji yake badan wani daliliba da sai yayma Hudah dukan mutuwa yau, saida kuma shi a tsarinsa babu bugun mace. Alhaji babane yace, “Jawaad dawo ka zauna”. Umarnin Alhaji baba yabi, ya juyo tare da zubama Shahudah wani mugun kallo daya sakata sakar masa riga ta durƙushe a wajen tana kuka, kota kanta baibi ba ya koma inda ya taso ya zauna. Ran Alhaji baba a ɓace yace, “Wanene Habib ɗin to dakasa ya aurar musu yarinya?”.
        Shima Jawaad ɗin ran nasa a ɓace yake, amma dai sai ya danne cikin ladabtaccen harshe ya bama kakan nasa amsa, “Alhaji baba shine wanda suka biya ya auri yarinyar”.
     Kuka Momy ta saka mai ƙarfima kuwa tana zagin Jawaad da ja masa ALLAH ya isa.
        Cikin rawar baki Uncle Nasir ke faɗin, “Yanzu nan Jawaad ɗan fir'auna ka aurama Shahudahr?.........”
      Uncle Sadiq yace, “Wane irin sunane haka kuma Yayah?”. Kasa magana Uncle Nasir.
       Dad kam ai hawaye kawai yakeyi kashirɓan, saboda wani irin ruɗani da wautarsa akan sakarma Momy ragamar gidansa yake hangowa. Falon yay tsit kowa na jiran ƙarin bayani daga garesu, yayinda Shahudah dake jikin Momy keta ribzar kuka. Qaseem kansa kawai ya dafe saboda tafasar da zuciyarsa ke masa da matsananciyar ƙuna.
          Kowa dai ya fahimci su Mom sune suka gina ramin mugunta wa marainiyar ALLAH daga ƙarshe ya rufta dasu batare dasun fargaba, Alhaji baba ya katse shirun da faɗin, “Bin ƙwaƙwƙwafin komai a yanda yake baida amfani, tunda su bamusan manufarsu ba, a ganina yanzu mafita kawai ya dace mu nema kamardai....”
     Qaseem ya

ɗago kai, cikin ɗacin rai yace, “Mafita itace wannan yaron ya sakarmin mata tunkafin rayuka suyi ɓacin da yafi na yanzu”.
     Miƙewa Jawaad yay cike da takun ƙasaita ya ƙarasa gaban Qaseem sunama juna kalon kallo tamkar wasu zakuna, baki ya taɓe yana binsa da wani banzan kallo, cikin kakkausan furuci yace, “Gurɓataccen tunani kenan Qaseem, domin kuwa wannan shine abinda bazai taɓa faruwaba koda a cikin mafarki, kayi wani tunanin amma ba wannanba” Yaƙare maganar da ɗan buga kafaɗar Qaseem ya raɓashi ya fice daga falon.

       Babu wanda ya iya yunƙurin hana Jawaad ɗin fita har Alhaji baba, dan a ganinsu garama ya tafi kar abin ya kuma ƙwaɓewa tsakaninsa da Qaseem. Asibiti Jawaad ya nufa domin ganin yaya su Bilkisu suka tashi. Saida ya tsaya ya sai abubuwa a hanya dukda yasan za'a kai abinci daga gidan Ummah, mintuna kaɗan ya shigo asibitin, da Nabeelah yaci karo ta fito sayama Ummah kati, ta amshi kayan hannunsa tana masa sannu da zuwa da gaishesa. Bai amsaba saboda waya yakeyi, hannu kawai ya ɗaga mata yay gaba, tabi bayansa tana gulmarsa a zuciya batare daya saniba, hardasu kwaikwayon tafiyarsa.
          A ƙofar ɗakin ya tsaya yayma Nabeelah nuni akan ta shiga domin sanar dasu. Da “to” ta amsa, shikuma ya cigaba da wayarsa a nutse, baifi minti biyu da shigartaba tafito tace ya shigo.............✍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.

[12/10/2020, 1:53 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 25

.............Na daɗe banji irin wannan matsanancin bugun zuciyarba idan na samu kusanci dashi.
     Tunda Nabeelah ta sanar da shigowarsa duk sai na nema nutsuwata na rasa, farfesun da Ummah ma ta tsareni naci sai naji ya fitarmin a rai, ƙasa-ƙasa nake kallon ƙofar ta gefen ido harya shigo da sallama, Sanye yake cikin ƙananun kayan nasa na fama, sai dai sun masa ƙyau kamar ko yaushe. Da hannu yake amsama kowa sannun da yake masa saboda waya yakeyi. Ummah ta tura masa kujerar da take zaune a kai ita kuma ta koma kusa dani a bakin gado.
            Gaba ɗaya na kasa cigaba da shan farfesun har sai da Ummah taimin magana, “Saifa kin cinye abincin nan tas dota, garama ki dage kafin nasa a riƙeminke namiki ɗura”. Murmushi nai ina satar kallon boss da ƙamshin turarensa ya addabi hancinanmu, kasancewar turaren maza yafi na mata ƙarfi duk sai ya danne namu. A bazata muka haɗa ido, saurin janye nawa nayi dan banyi tunanin kallona yakeba. Farfesun na cigaba da tsakura kaɗan-kaɗan, har yanzu inajin idanunsa na yawo a kaina ko kunyar su Ummah bayaji.
     Kusan mintuna biyar ya ɗauka kafin ya ajiye wayar yana faɗin, “Am sorry Ummana nazo ina waya”. Murmushi Ummah tai masa, tace, “Babu komai Son”. Guntun murmushi yayi yana mai risinar da kansa ya gaisheta ita da Mama, kafin ya ɗorama mama da godiya. Mama tace, “Babu komai Jawaad, ai yima kaine, Bilkisu ta cancanci ai mata abindama yafi haka dan yarinyar kirkice mai tarbiyya, mu saidai muce ALLAH ya sanya alkairi a wannan al'amari ya kuma baku zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba”.
     Gaba ɗaya ban fahimci kalaman mamaba, dan dama Nabeelah ta shigo ɗazu tana cemin amaryar yayansu, kallonsa naɗan sata sai naga ya amsa da “Amin” akan laɓɓansa. Tunanin ko da aunty Shahudah aka ɗaura masa aurene yasa naɗanji nutsuwa. Ganin ya gama gaisawa da aunty Batool nima nace, “Ina kwana sir”.
         Amsamin yay da “Lafiya, ya jikin naki?”. “Alhmdllh naji sauƙi”. Bai sake cemin komaiba ya juya sukai magana da Ummah, sai naga sun miƙe sun fita. Numfashi na sauke a hankali ina rumtse idona, dan fitar tasa yasa naji kamar an saukemin kaya. Babu abinda nake buƙata a halin yanzu kamar ƙarin bayani akan abinda ya faru jiya tsakanina da ƴan gidanmu, banga kowa a cikinsu ba kuma yau tunda na farka, sannan kuma miya faru har aunty Shahudah ta nemi jimin ciwo su aunty Aamilah kuma sukaimin wannan bugun da gashi ya kaini da kwana a asibiti?........
         Ring ɗin wayatane da Ummie ta kawo ɗazun ya katsemin tunani, Nabeelah dake kusa da wayar ta miƙomin tana ƴar dariya, “Matar Yayanmu waye kuma masarauta?”. Wayar na amsa dan karta tsinke batare dana bata amsaba, bayan mun gaisa daga can Amaturrahman ke tambayata a ɗakin da nake?. Mamaki ne ya kamani sosai, ta yaya akai sukasan banda lafiya to? Kodai jiya sunzo ana wannan rikicin da bansan tshensa ba? Tunanin ƙila Ummie ce ta sanar musu ya sakani amsa mata da cewar bara na turo a shigo dasu. Da ga haka muka ajiye wayar, Nabeelah na kalla cikin marairaicewa nace, “Sorry dear, dan ALLAH ki shigo da baƙi wai suna waje”. Cikin dariya tace, “Karki damu matar yayanmu, girmankine ai”. Kasa haƙuri nayi nace mata, “Wai nikam wannan sunan daga ina haka?”. Sosai ta kwashe da dariya tana nufar hanyar fita da faɗin, “A wannan ba hurumina bane, yayanmu zai baki bayani”.
      Aunty Batool ce tace, “Fitsararriya ALLAH yasa ya jiki dai”. “Ba amin ba” ta faɗa tana ficewa fuska a kumbure.
      Murmushi mukai ni da mama, danni taɓarar Nabeelah dariya take bani, na lura gatane kawai yay mata yawa, ga uwa ga uba ga yayu ga dangi gata auta kuma. Mintuna baifi goma ba sai ga Nabeelah ta shigo dasu Amaturrahman bakinta fal magana da ganin jama'ar kamar jinin sarauta, dan tare suke da hadimai mata uku tare da wani dattijo, sai hadimai maza suma guda biyu.
    Tun a waje Jawaad da Ummah dake zaune suna magana akan yanda za'ai da bilkisu kafin lokacin tarewar sukaga Nabeelah dasu Amaturrahman, cike da mamaki suka bisu da kallo, ganin da gaske ɗakin da bily take suka shiga yasasu tasowa suka biyo bayansu.
      A waje suka iske hadiman su duka biyar, basuce dasu komaiba suka sh
Chapter 57 · 0% Book details