← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 168

Sashe 30

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

aba maigarin da zasuyi sa'anni da Jawaad, dan abokinsane na amana, dukkan sirrin gidan gonarsa yana hannun Abbati, shike kula da komai, Abbati dukda yayi karatu har matakin degree na biyu yana zaune ne anan ƙauyen tare da iyayensa, iyakarsa yaje birni wajen aiki ya dawo garinsu ya kwanta, matarsa ɗaya da ƴaƴa huɗu, yayi ɗan gininsa na zamani saboda ƙauyen yanzu yanada dukkan cigaban da ake hangensa a birnin, kuma mafi yawansu sunada aƙidar son zaman gida sai dai waɗanda aiki ya tilastama komawa birnin akan dole, dan a dalilin Abdul-aziz mahaifin Jawaad ƙauyen yanada manyan ƴan boko matasa masu jini a jika dake taka rawar gani sosai a sassan ƙasar.
     Suna tafe suna hirarsu cikin nishaɗi, inda Abbati keta kiran sauran abokansu dake gida ta waya yana sanar musu Jawaad yazo. Jawaad ya fige wayar yana hararar Abbati, “Malam ya isheka haka, sai gayyatomin ƴan iskannan kake salon kuzo ku addabeni da surutu mara ma'ana”. Abbati ya kwashe da dariya, “Oh ashe kana tsoron surutun namu? Ai indai kaga munbar maka surutu kuwa sai kayi abinda mukeso, ka dubemu daga mai yara uku sai masu huɗu amma kai ka zauna ruwan ido Jay, ai kosu Jabeer da kuke tare a birni  sunada iyalansu, wai kodai da kurwanka Shahudah ta tafine bani labari kafin su Isa su zo”.
     Kafin Jay yay magana sukaji ance, “Ai gamu mun iso”. Daƙƙuwa Jay ya watsama abokan nasa huɗu da suka iso wajen yanzu-yanzu, waɗanda suma duk sunyi karatu kowa da abin yinsa, kuma suna bada gudunmawa a gidan gonarsa suma. “Duk kunci ƙaniyarku zomayen banza, uwarwa ya gayyatoku nan?”.
      Dariya suka sanya baki ɗaya, Labaran ya dunƙule hannu ya bigi damtsen hannun Jawaad yana faɗin, “Bar wani mazurai gaye, munfika ƙarfi fa inma hayaƙin kakeji, dan mu kullum matanmu ƙara mana sukeyi” duka shima Jawaad ya kai masa, Labaran yay saurin duƙewa. “Ɗan iska da ka tsaya naima fuskarka damage sai naga ƙarfin da Asiyan ke baka, mara mutunci”. Dariya suka sanya su dukansu, Aminu yace, “Mudai mun gaji da ganinka haka ALLAH kuwa”. “Gaskiyane Aminu, ya kamata ka duba Jay” cewar isa. “Hakane kam lokaci baya jira fa, kullum girma muke ƙarawa ƙuruciyarmu na guduwa” cewar Salisu dake dafe da kafaɗar Jawaad. Murmushi kawai Jawaad yayi, yasan halin abokan nasa, tunkan yay auren farkoma haka sukaita addabarsa, sai da akai bikinsa da shahudane suka sama masa lafiya, yanzunma ko waya yake dasu faɗansu kenan, shi kansa ba auren bane bayaso, gidan jiya yake tsoron komawa........ Adam ya katse masa tunani da cewar, “Idan kuma a birnin babu wadda tai maka ka duba a garin nan mana, auren nan shine cikar martabar mutum”. Abbati yace, “Maganarku nakan hanya ƴan uwa, ko ɓato maka rai akai daga waje kana shigowa gida kaga iyalanka sai kaji ka huce, musamman idan kayi dace da macen datasan yanda zata tattali dukkanin farin cikinka, koda gajiyarka ka kwaso kanada inda za'a nuna tausayinka a sauke maka ita da kulawa”. Jawaad ya shafa kansa yana sauke numfashi da girgiza kai, “Kudai baku da magana saita aure dai jarababbu, ko hutawa bakwayi, karku damu zanyi, kumin addu'a kudai. a tare suka shiga masa addu'ar kuwa kafin su fara bashi hannu suna gaisuwa.
       Jawaad nason abokansa na ƙauyensu, dan suna bashi nishaɗi da faɗa masa gaskiya komai ɗacinta, shiyyasa ko kansa ɗaukar zafi yay a wajen aiki tuni yake ƙoƙarin ware weekend ɗin da zai shigo, dan yasan zai samu nutsuwa sosai..............✍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[12/31/2020, 9:31 PM] Abubakar Saleh Kurami: Aminatu Alhassan:
Typing📲

ƘWAI cikin ƘAYA!!

Bilyn Abdull ce🤙🏻

BOOK TWO

Page 15

To yau page ɗin ƙwai cikin ƙaya na ƙuɗine, duk wanda ya karanta ina roƙonsa dan girman ALLAH ya biya da addu'ar ALLAH ya kawo mana iyakar tashin hankalin dake damun wasu yankuna namu na arewaci, dan ALLAH ina roƙon har ƴaƴanmu ku saka suyi wannan addu'ar a dukkanin sallolinsu biyar na wannan yinin, domin addu'ar yara abuce mai muhimmanci a garemu mubar sakaci da ita, idan baki aureba ki roƙa mana jama'ar gidanku suyi da kanninki, duk da munsan anayi dama, sai dai ina fatan wannan ta zama ta musamman domin ALLAH, dan ALLAH kar'a manta, kar'a manta, kar'a manta.

Ya rabbi ka kawo mana ƙarshen waɗanan tashin hankali, ya ALLAH ka ruɓanya rahamarka da rangwame a garemu, ya Rabbi ka yafe mana kurakuranmu, ya Rabbi kaimana maganin abinda bazamu iyaba harma da wanda zamu iya ɗin, ya rabbi ka taimaki bayinka dake cikin gararin rayuwa da hali na buƙatar agaji, ya rabbi ka kawoma muhallansu zaman lafiya, kasaka kwanciyar hankali a zukatansu suma su sami cigaba da rayuwa a yankunansu kamar kowa, ya rabbi ka kawoma ƙasarmu zaman lafiya baki ɗaya da dukkanin duniyar musulunci, ya rabbi ka bamu ikon cinye jarabawa kasa ta zama rahama a garemu duniya da lahira🙏🏻😭.

Idan kasan bazaka biyaba karka karanta, bayin ALLAH na buƙatar tallafin addu'oinmu, dan girman ALLAH karmu wofantar da lamarinsu saboda mu muna barci a gidajenmu da iyalanmu bayan munci mun ƙoshi, ba'a zahiri kawai nakeson ayiba har abaɗi ma ita mukafi buƙata😭.
Masu 6am sunyi winning, wannan shine zaizama lokacin posting ɗinmu kafin na daina fushi da kamfanin masu yellow'n tambari 🙄🙄🙄.

................Daga ni har shi kallonsa mukai. Nidai na sauke idanuna da hannuna a hankali ina haɗiyar yawu da ƙyar. Kamal yace, “Haba malam ya haka?” Jawaad bai tanka masaba, sai wayar daya daddana alamar wani abun yayi a ciki ya miƙa masa. A ƙufule Kamal ya amsa yana faɗin, “Wanan rainin wayone ai, ya zakazo ka shiga abinda bai shafeka ba?”.
Ban jira amsar da boss zai bashiba nabar wajen nidai, saboda wata muguwar harara daya makamin dan ya cire madubin idonsa.
Jawaad ya maida kallonsa ga kamal yace, “Karka damu ka kira Number dana saka maka zaka sameta”. Kamal yay ɗan shiru alamar nazari, sai kuma yay saurin taɓa hannun Jawaad dake shirin barin wajen, Jay ya juyo yana kallonsa, sai dai baice komaiba. “Sorry, dan ALLAH ko ƙanwarka ce dai?” wani munafukin murmushi Jawaad yayi tare da ɗagema kamal gira ɗaya sannan ya wani juya kansa da lumshe ido yabar wajen. Sam Kamal bai fahimci komai daga yaren na Jawaad ba, sai dai kuma ya haƙura akan zai nema waje ya zauna harsu tashi tafiya ya bisu a baya, dan shifa yaga matar aure.
Tsaye yazo ya sameni ina waya da Zuhrah, baiko kalleni ba yaja kujerar da ya fara zama ɗazun ya sake zaunawa yana maida glasess ɗinsa a ido kamar ma ya manta dani, nima ɗin dai ƙasa-ƙasa nake satar kallonsa yanda nasan bazai fahimtaba ina wayata, a ƙasan raina inata tunanin komi ya cema Kamal? Number wa kuma ya saka masa a waya? Dan nidai nasan baisan tawaba. Zuwan ɗaya daga ma'aikatan wajen ne ya sakani janye idona a kansa, umarnin kwashe kayan wajen ya basa tare da sake kawo wasu, dai-dai lokacin da muka ƙarisa wayar, sai da yabar wajen ne cikin dauriya nace masa, “Ina kwana sir”.
Shiru bai tanka minba, saima ya kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa ya ɗauke kansa, duk a tsorace nake, gani nake zaimin faɗa akan ganina da Kamal, amma har aka sake kawo abinda ya saka ɗin baice dani komaiba.
Ni kuma har lokacin ina tsaye duk da ƙafafuna sun gaji haka na fuske abina, shiko ya buɗe sabon Popcorn ɗin da aka kawo ya hau ci yanayi yana danna waya, baifi ɗiba uku ba wata mata mai sanye da hijjab har ƙasa da niƙaf ta iso wajen, sallama tai mana, na amsa mata, shiko bangama ya motsaba har sai da taja kujerar gefensa ta zauna, sai da ta ɗage niƙaf ɗin tana gaishesa sannan na fahimci wadda muke jirace.
Batare da ya amsa mata gaisuwarta ba yace, “Kinsan irin ɓata mana lokacin da kikai?” haƙuri ta bashi. Kallona yay ya ɗauke kansa batare da yace komaiba, hakan ya sakani gyara kujera nima na zauna.

Munja
Chapter 30 · 0% Book details