Sashe 84
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasancewar nazo babu tsarki sai yau nake fatan samu lokacin da zamuyi sahur saina duba, naji wani nishaɗi ganin ya ɗauke harda tsallena a bayi, wanka nayo da brush na fito, cikin tsokana Meenal tace, “Gandiya halan yau kin musulunta ne? Naga wanka da asubar fari”. Murmushi nai mata ina zama domin busar da kaina da hand drayer ɗin dana gani saman mirror ɗakin, nace, “Oh da kafira kike kallona?”. Dariya sukayi ita da Amaturrahman dake ƙoƙarin shiga yin brush itama, tace, “Ai kima godema ALLAH ke kina zuwa yana ɗaukewa, ita tana shigowa yana zuwa”. Cikin ɗan zaro idanu na kalli Meenal ɗin, sai kuma na langaɓe kai nace, “Kai harfa kin bani tausayi babie”. Filo ta ɗauka ta jehomin ɗaya ta jefama Amaturrahman. Da gudu Amaturrahman ta shige bayi tana dariya, nikuma na cafe wanda ta tillomin. “ALLAH karkiji wasa meenal tausayi kika bani” nai maganar da ɗan mata gwalo. Ƙwafa tayi da faɗin, “Wlhy duk zan rama, ke saurama ƙiris na raman ai, zaki gane kurankine”. Murmushi nai mata bance komaiba na cigaba da busar da kaina.
Bayan munyi sahur salla mukai muka sake kwanciya barci, mune bamu tashiba sai sha ɗaya, shima tadamu akazo akayi. shiri mukai a gaggauce na tafiya massallaci, nidai Kasa daurewa nai na tambayi Amaturrahman Auntyn da Ummu tace tanada makaranta gidansu kuma na kusa da inda zamu sauka?.
“Lah Bily ai yanzu bazakiga Umm-Anum ba, sun shiga ittifaqi, kinga gidansu nan, duk Ramdhan idan mukazo bama ganinsu muma sai ranar sallah”. Da mamaki nace, “Basu da yara?”. Tace, “Sunada yara biyu mana, mace da namiji, namijin ya girmemu da kusan shekara biyar, sunansa Anwar, sai macen Anum, tare suke shiga ittifaqi. Tunkan na gansu naji sun matuƙar burgeni har ina zumuɗin ganin nasu mai ban mamaki, dan tunda Ummu taban labarin matar a taƙaice saita kasa barin zuciyata. Yanda na iso da ƙuncin zuciya a yanzu sai ba hakaba, fes nakejin raina cike da nishaɗi da farin ciki da shauƙin ganina a ƙasa mai tsarki, santin da banyi a daren jiyaba sai gashi a yau inayinsa, dan har muka isa massallaci bakina bai hutaba, Safah kam bata gajiya damin bayanin komai dalla-dalla. Lokacin dana ganni gaban ɗakin ka'aba sai kawai nakejina tamkar wata sabuwar Bilkisu ce tsaye ba wadda tazo da ƙunci ba, hawaye masu ɗumi na ziraromin bisa kumatu, abinda ban taɓa tunaniba koda a mafarki, wani nauyin zuciya da ƙunci da damuwar da natsinci kaina a gaba ɗaya cikin shekarunan sai naji tamkar an yayesu an zubar tare da ruwan wankan dana samu tsarki ɗazun da asuba. UBANGIJI mai rahama, UBANGIJI mai ni'ima.
Muna zaune a wajen mutanen kirki, larabawan usul masu ƙyawawan zuciyoyi, bamu rasa komaiba, ibada muke babu wasa dansu Amaturrahman sun horu sosai, sannan sunada ilimin addini suna kuma aiki dashi, Umm-Aban koda yaushe cikin kulawa take damu sosai, nasamu sauyi iri-iri da ha
ske a rayuwata a cikin kwanakinan goma da mukai na Umrah, babu abinda mukeyi banda ibada, duk wata shiririta mun ajiyeta gefe, a kullum safiya bayan sahur muna waya da gimbiya, hakama su Ummie duk saina kirasu, Boss kam ko filashin bai taɓa haɗamu ba, sannan dukkan numbers ɗin ƴan gidanmu bana ganinsu a wayata yanzun, bansan yaya akai hakan ta kasanceba tunda nidai ban gogeba.
Yau take salla, sosai massalacin ke cike, bayan an idar da sallah sai na dingajin juwa, duk yanda naso dannewa hakan ya gagara, bandai sanarma su Amaturrahman ba dan karsu tada hankalinsu, miƙewa nai da nufin na ɗan samu waje inda babu yawan mutane na huta ko zanji nutsuwa sai kawai hajijiya ta kwasheni. Sama-sama na jiyo wata nutsatstsiyar muryar ta ambaci “Yah ALLAH”. Sai jina nai a jikinta. Cikin ɗan larabcin da nakeji kaɗan-kaɗan na tsinci tanama wani wanda bansan ko waneneba magana akan ya bata ruwan zam-zam dake hannunsa. Gabana yay wata masifar faɗuwa jin muryar data amsa mata, murya irin wadda wajan mutum ɗaya na santa, muryar dake sakani bugun zuciya, muryar dake saka jinina gudu cikin jijiyoyi, da ƙyar nai ƙoƙarin ɗaga idanuna dake neman rufewa na sauke a kansa dai-dai ya miƙo ƙaramar goran ruwa wa matar da har yanzu nike a jikinta.............✍
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Kwai Cikin Ƙaya!!
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
BARKA DA JUMA'A
Page 37
..................Sosai su Amaturrahman ke santin gidan Jawaad na A.Y Street, badan yafi kowane gidaba, bakuma dan an cikasa da ƙawa ba, ginine dai tamkar kowanne gini da kowa yasani, sai dai yanda akai tsarin gyaran sai ya kuma fiddo da ƙyawun gidan fiye da yanda yake a da, (masu karatu karku manta wannan shine gidan da aka haifa Jawaad, a cikinsa iyayensa suka rayu, dan shine gidannan da turawannan suka bama Abba Abdul-aziz, shine kuma sanadin wannan arziƙi daya tsolema mutane ido). Sai da suka shiga ko'ina da ina dan babu komai cikinsa sai ƙamshin sabon fenti.
Suna tsaka da dubawa Jay ya iso gidan, zaune yake a bayan motar sai Sadiq sabon drivern sa dake tuƙi cikin nutsuwa, dan shima dai baida matsala, amma hakan bai hana Jay tuna Gimba ba a kowacce daƙiƙa ta rayuwarsa, yasan gimba bazai mantu a zuciyarsa ba, dan yawuce duk tunanin mai hasashe a zuciyar tasa. Yauma kamar kullum yana cikin gayunsa da ƙyamshi, sai dai ya ɗan rame, hakan yasakashi yin wani fayau dashi, (bamu saniba azumin da aka shane kokuma ɗokin amaryarne. lol😂).
waya yakeyi, hakan yasa har Sadiq ya fito ya buɗe masa bai fitoba, sai da yaja kusan mintuna huɗu sannan ya fito bayan ya ajiye wayar, Safah data dage sai anzo da ita da gudu tayo kansa, fuskarsa ɗauke da murmushi harta iso garesa, hannunsa ta kama tana gaishesa. Shidai kallonta yake kawai, dan sosai ƙiriniyarta ke bashi mamaki, ko gajiya batayi, girma take amma abun tamkar ƙaruwar mata yakeyi. (Hhhhh tunda Jinin Munaya na yawo a jikin Safah ai kaga abinda yafi hakama, sarki Sameer ne zai baka labari dalla-dalla😂🤐). Cikin ɗoki tace, “Yayanmu gidanka kaida aunty B ya haɗu sosai, nima harna zaɓi ɗakina dan kasanfa nan zan dawo. Murmushi yay mata mai sanyi ya jinjina mata kai amma baice komaiba.
Sosai mamaki ya kama Jay lokacin da suka shiga ciki shi da Safah yay arba da Munubiya, shi tunaninsa Gimbiyace da kanta, itama ɗindai kallon mamaki take masan sai dai ita bamusan kona minene ba. Su Amaturrahman ne suka katse tunaninsa da gaisuwar da suke masa, ya amsa musu da kulawa kafin shima ya gaida Munubiya cikin girmamawa. Kasa haƙuri yay dai yace, “Ummu da kanki? Su Amaturrahman ma aisun isa basai ke kinzoba”. Munubiya tai murmushinta mai kama dana Munaya, kafin ta bashi amsa Safah tace, “Lah Yayanmu bafa Ummu bace, wannan Mami ce sweetheart ɗin Ummu”. Cikin rashin fahimta yake kallon Safah amma baice komaiba. Amaturrahman tace, “Yayanmu ai Ummu ƴan biyune, Mami itace hassanarta”. Ɗan waro idanu Jay yayi waje sai kuma ya shafa kansa, “Sorry Mami ai wlhy ni duk ɗaukata Ummu ce, bansan ita ƴan biyu baneba nasan dai tanada yaya mace”. “Karka damu ƙanina, Gida yay ƙyau masha ALLAH, ALLAH yasa rai akaimawa, ALLAH yasa a cika manashi taf da ƴaƴa ko jikoki zance”. Cikin murna su Safah suka shiga faɗin, “Amin”. Shidai a saman laɓɓa ya amsa nasa amin ɗin.
Kasa jurewa Mami Munubiya tai ta koma gefe tai kiran Munaya, tana ɗagawa tace, “Sweetheart kingako mina gani ga angon nan?”. Daga can murmushi gimbiya Munaya tai tana gyara kanta a kafaɗar takawa, tace, “Nasan ina kika dosa sweetheart, tun randa na fara ganinsa nima naga abinda kika gani, wannan ne dalilin tura matarsa can ta ɗan zauna, sai dai bamu da tabbas, amma muna fatan ALLAH yasa ta kasance hakanne”. “Kai to amin kuwa, al'amarin akwai ruɗarwa, amma gaskiya bana tantamar alaƙa a tsakaninsa da Umm-Anum Sweetheart, nifa da farko na zata Anuwar ne wlhy, sai da nai masa kallon nutsuwa na fahimci yafi Anuwar cikar zati, Anuwar kuma ya fisa haske, hatta da maganarsu kumafa babu banbanci, bara sai dai mun dawo ma tattauna”. Daga haka Mami Munubiya ta yanke wayar ta koma ciki dan baƙin da suke jira har sun iso.
Sai da suka gama zagaye gidan tsaf kafin su basu hotunan kayan ɗakin da zasu dace da tsarin gidan akan su zaɓa. Shi dai Jawaad bai saka musu bakiba, Mami dai ta tambayesa kalar da yafi so, ya sanar musu, daga haka ya cigaba da danne-dannen waya Safah na gefensa tana zuba masa surutu, shidai nasa saurarenta dayin murmushi, sai jefi-jefi yake bata amsar wani abun koyay mata tamba
ya.
Kusan awa guda suka kammala komai dangane da zaɓin kayan, a take Mami ta kira Ummu ta sanar mata kuɗin da suka cajesu. Kafin kuwa subar gidan har ƙuɗaɗensu sun shiga accaunt. daga haka suka bar gidan akan sai zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu zasu dawo suga yanda kamfanin suka shirya gidan. Jay yaymusu rakkiya har mota yanama Mami godiya, sai da suka wuce sannan shima ya shiga mota suka bar gidan.
Bayan munyi sahur salla mukai muka sake kwanciya barci, mune bamu tashiba sai sha ɗaya, shima tadamu akazo akayi. shiri mukai a gaggauce na tafiya massallaci, nidai Kasa daurewa nai na tambayi Amaturrahman Auntyn da Ummu tace tanada makaranta gidansu kuma na kusa da inda zamu sauka?.
“Lah Bily ai yanzu bazakiga Umm-Anum ba, sun shiga ittifaqi, kinga gidansu nan, duk Ramdhan idan mukazo bama ganinsu muma sai ranar sallah”. Da mamaki nace, “Basu da yara?”. Tace, “Sunada yara biyu mana, mace da namiji, namijin ya girmemu da kusan shekara biyar, sunansa Anwar, sai macen Anum, tare suke shiga ittifaqi. Tunkan na gansu naji sun matuƙar burgeni har ina zumuɗin ganin nasu mai ban mamaki, dan tunda Ummu taban labarin matar a taƙaice saita kasa barin zuciyata. Yanda na iso da ƙuncin zuciya a yanzu sai ba hakaba, fes nakejin raina cike da nishaɗi da farin ciki da shauƙin ganina a ƙasa mai tsarki, santin da banyi a daren jiyaba sai gashi a yau inayinsa, dan har muka isa massallaci bakina bai hutaba, Safah kam bata gajiya damin bayanin komai dalla-dalla. Lokacin dana ganni gaban ɗakin ka'aba sai kawai nakejina tamkar wata sabuwar Bilkisu ce tsaye ba wadda tazo da ƙunci ba, hawaye masu ɗumi na ziraromin bisa kumatu, abinda ban taɓa tunaniba koda a mafarki, wani nauyin zuciya da ƙunci da damuwar da natsinci kaina a gaba ɗaya cikin shekarunan sai naji tamkar an yayesu an zubar tare da ruwan wankan dana samu tsarki ɗazun da asuba. UBANGIJI mai rahama, UBANGIJI mai ni'ima.
Muna zaune a wajen mutanen kirki, larabawan usul masu ƙyawawan zuciyoyi, bamu rasa komaiba, ibada muke babu wasa dansu Amaturrahman sun horu sosai, sannan sunada ilimin addini suna kuma aiki dashi, Umm-Aban koda yaushe cikin kulawa take damu sosai, nasamu sauyi iri-iri da ha
ske a rayuwata a cikin kwanakinan goma da mukai na Umrah, babu abinda mukeyi banda ibada, duk wata shiririta mun ajiyeta gefe, a kullum safiya bayan sahur muna waya da gimbiya, hakama su Ummie duk saina kirasu, Boss kam ko filashin bai taɓa haɗamu ba, sannan dukkan numbers ɗin ƴan gidanmu bana ganinsu a wayata yanzun, bansan yaya akai hakan ta kasanceba tunda nidai ban gogeba.
Yau take salla, sosai massalacin ke cike, bayan an idar da sallah sai na dingajin juwa, duk yanda naso dannewa hakan ya gagara, bandai sanarma su Amaturrahman ba dan karsu tada hankalinsu, miƙewa nai da nufin na ɗan samu waje inda babu yawan mutane na huta ko zanji nutsuwa sai kawai hajijiya ta kwasheni. Sama-sama na jiyo wata nutsatstsiyar muryar ta ambaci “Yah ALLAH”. Sai jina nai a jikinta. Cikin ɗan larabcin da nakeji kaɗan-kaɗan na tsinci tanama wani wanda bansan ko waneneba magana akan ya bata ruwan zam-zam dake hannunsa. Gabana yay wata masifar faɗuwa jin muryar data amsa mata, murya irin wadda wajan mutum ɗaya na santa, muryar dake sakani bugun zuciya, muryar dake saka jinina gudu cikin jijiyoyi, da ƙyar nai ƙoƙarin ɗaga idanuna dake neman rufewa na sauke a kansa dai-dai ya miƙo ƙaramar goran ruwa wa matar da har yanzu nike a jikinta.............✍
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Kwai Cikin Ƙaya!!
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
BARKA DA JUMA'A
Page 37
..................Sosai su Amaturrahman ke santin gidan Jawaad na A.Y Street, badan yafi kowane gidaba, bakuma dan an cikasa da ƙawa ba, ginine dai tamkar kowanne gini da kowa yasani, sai dai yanda akai tsarin gyaran sai ya kuma fiddo da ƙyawun gidan fiye da yanda yake a da, (masu karatu karku manta wannan shine gidan da aka haifa Jawaad, a cikinsa iyayensa suka rayu, dan shine gidannan da turawannan suka bama Abba Abdul-aziz, shine kuma sanadin wannan arziƙi daya tsolema mutane ido). Sai da suka shiga ko'ina da ina dan babu komai cikinsa sai ƙamshin sabon fenti.
Suna tsaka da dubawa Jay ya iso gidan, zaune yake a bayan motar sai Sadiq sabon drivern sa dake tuƙi cikin nutsuwa, dan shima dai baida matsala, amma hakan bai hana Jay tuna Gimba ba a kowacce daƙiƙa ta rayuwarsa, yasan gimba bazai mantu a zuciyarsa ba, dan yawuce duk tunanin mai hasashe a zuciyar tasa. Yauma kamar kullum yana cikin gayunsa da ƙyamshi, sai dai ya ɗan rame, hakan yasakashi yin wani fayau dashi, (bamu saniba azumin da aka shane kokuma ɗokin amaryarne. lol😂).
waya yakeyi, hakan yasa har Sadiq ya fito ya buɗe masa bai fitoba, sai da yaja kusan mintuna huɗu sannan ya fito bayan ya ajiye wayar, Safah data dage sai anzo da ita da gudu tayo kansa, fuskarsa ɗauke da murmushi harta iso garesa, hannunsa ta kama tana gaishesa. Shidai kallonta yake kawai, dan sosai ƙiriniyarta ke bashi mamaki, ko gajiya batayi, girma take amma abun tamkar ƙaruwar mata yakeyi. (Hhhhh tunda Jinin Munaya na yawo a jikin Safah ai kaga abinda yafi hakama, sarki Sameer ne zai baka labari dalla-dalla😂🤐). Cikin ɗoki tace, “Yayanmu gidanka kaida aunty B ya haɗu sosai, nima harna zaɓi ɗakina dan kasanfa nan zan dawo. Murmushi yay mata mai sanyi ya jinjina mata kai amma baice komaiba.
Sosai mamaki ya kama Jay lokacin da suka shiga ciki shi da Safah yay arba da Munubiya, shi tunaninsa Gimbiyace da kanta, itama ɗindai kallon mamaki take masan sai dai ita bamusan kona minene ba. Su Amaturrahman ne suka katse tunaninsa da gaisuwar da suke masa, ya amsa musu da kulawa kafin shima ya gaida Munubiya cikin girmamawa. Kasa haƙuri yay dai yace, “Ummu da kanki? Su Amaturrahman ma aisun isa basai ke kinzoba”. Munubiya tai murmushinta mai kama dana Munaya, kafin ta bashi amsa Safah tace, “Lah Yayanmu bafa Ummu bace, wannan Mami ce sweetheart ɗin Ummu”. Cikin rashin fahimta yake kallon Safah amma baice komaiba. Amaturrahman tace, “Yayanmu ai Ummu ƴan biyune, Mami itace hassanarta”. Ɗan waro idanu Jay yayi waje sai kuma ya shafa kansa, “Sorry Mami ai wlhy ni duk ɗaukata Ummu ce, bansan ita ƴan biyu baneba nasan dai tanada yaya mace”. “Karka damu ƙanina, Gida yay ƙyau masha ALLAH, ALLAH yasa rai akaimawa, ALLAH yasa a cika manashi taf da ƴaƴa ko jikoki zance”. Cikin murna su Safah suka shiga faɗin, “Amin”. Shidai a saman laɓɓa ya amsa nasa amin ɗin.
Kasa jurewa Mami Munubiya tai ta koma gefe tai kiran Munaya, tana ɗagawa tace, “Sweetheart kingako mina gani ga angon nan?”. Daga can murmushi gimbiya Munaya tai tana gyara kanta a kafaɗar takawa, tace, “Nasan ina kika dosa sweetheart, tun randa na fara ganinsa nima naga abinda kika gani, wannan ne dalilin tura matarsa can ta ɗan zauna, sai dai bamu da tabbas, amma muna fatan ALLAH yasa ta kasance hakanne”. “Kai to amin kuwa, al'amarin akwai ruɗarwa, amma gaskiya bana tantamar alaƙa a tsakaninsa da Umm-Anum Sweetheart, nifa da farko na zata Anuwar ne wlhy, sai da nai masa kallon nutsuwa na fahimci yafi Anuwar cikar zati, Anuwar kuma ya fisa haske, hatta da maganarsu kumafa babu banbanci, bara sai dai mun dawo ma tattauna”. Daga haka Mami Munubiya ta yanke wayar ta koma ciki dan baƙin da suke jira har sun iso.
Sai da suka gama zagaye gidan tsaf kafin su basu hotunan kayan ɗakin da zasu dace da tsarin gidan akan su zaɓa. Shi dai Jawaad bai saka musu bakiba, Mami dai ta tambayesa kalar da yafi so, ya sanar musu, daga haka ya cigaba da danne-dannen waya Safah na gefensa tana zuba masa surutu, shidai nasa saurarenta dayin murmushi, sai jefi-jefi yake bata amsar wani abun koyay mata tamba
ya.
Kusan awa guda suka kammala komai dangane da zaɓin kayan, a take Mami ta kira Ummu ta sanar mata kuɗin da suka cajesu. Kafin kuwa subar gidan har ƙuɗaɗensu sun shiga accaunt. daga haka suka bar gidan akan sai zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu zasu dawo suga yanda kamfanin suka shirya gidan. Jay yaymusu rakkiya har mota yanama Mami godiya, sai da suka wuce sannan shima ya shiga mota suka bar gidan.