Sashe 54
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Magana yaje sukai da Doctor, ko kallon ɗakin da aka kwantar da Shahudah baiyiba yay ficewarsa daga asibitin, daga nan gidan Alhaji baba ya nufa.
Kiraye-kirayen sallar isha'i da akeyine ya sakashi shiga massallaci, saida aka idar ya shiga gidan. Shima Alhaji baban shigowarsa kenan babu jimawa, Jawaad ya zauna ya gaishesa, amsawa Alhaji baba yay idonsa akan jikam nasa. fuskar Alhaji a ɗaure baba yace, “Daga ina?”. Batare da Jawaad ya kallesaba yace, “Gida”. “Ɗazun kumafa da akaita nemanka a wajen ɗaurin aure?”. “Aiki naje”. Alhaji baba yace, “Humm aiki? Kenan bakasan miya faru a wajen ɗaurin aureba ma?”. Kan Jawaad a ƙasa dan yaƙi yarda su haɗa ido da kakan nasa yace, “Na sani, ninema na canja list ɗin ai”. Idanu Alhaji baba ya ɗago daga littafin addu'oin dake hannunsa ya kafe Jawaad ɗin da kallo, cikin sake ɗaure fuska yace, “Ai nasan bazai wuce kaiɗinbane daman, miyasa kai hakan?”. Kallonsa Jawaad ya ɗago yayi sai kuma ya ɗauke kansa yana wani ɓata fuska, dama yasan ko kowa bai gano shi bane da wuri Alhaji baba sai ya gane.
Alhaji baba yay ƙwafa yana maida kansa ga littafin da faɗin, “A hatsabibancinka dana sani hakan ƙaramin abune a gareka Jawaad, amma ince tun randa mukaje gidan Alhaji Ali akan maganarnan ya tabbatar mana da ɗansa zai aurama yarinyarnan kace ka haƙura?”. “Hakane baba, kamar yanda na faɗa a gabanku na haƙura na barmasa da gasken na haƙuran, sai dai kuma dalilin daya biyo bayane yasa na canja shawara”. Ran Alhaji baba ya fara ɓaci, dan haka cikin zafi yace, “Kasan zan iya saɓa maka ko Muhammad? Har wane irin banzan dalili ka riƙe da bazakazo ka sanar minba kafin ka yanke masa hukunci? Banason wannan shegen taurin kan nakafa kaima ka sani”. Sosai idanun Jawaad suka sake kaɗawa sukai jajur, jijiyar kansa dukta fito ruɗu-ruɗu, yasan duk sanda zaiyi abu saiya zo ya sanarma Alhaji baba, dan a halin yanzu shine kawai ke iya nuna masa ɓacin rai idan ya aikata ba dai-daiba kuma ya tsawatar masa akan ya kiyaye gaba, to amma akan wannan shi kansa baisan miyasa zuciyar
sa taƙi aminta da ya nema sharar kowaba akan batun har sai bayan ya aiwatar..........
“Ina maka magana ka tafi tunani”. Jawaad da maganar Alhaji baba ta maido hayyacinsa yay ajiyar zuciya, cikin sanyin murya yace, “Nayi laifi kayi haƙuri, amma zuwa nan gaba kaɗan zaka fahimci hakan danai shine dai-dai baba......”
“Dai-dai ɗin ƙaniyarka, ka sakar musu yarinya ta auri wanda suka zaɓa mata, shikuma wancan habibun halan shima kaine ka kawosu shi da Azeemar? Tunda kasan har cikin ranka bakason maida yarinyarnan miyasa ka amincemin zaka maidatan?”.
“Baba nifa bani na kawosuba, su Uncle Nasir pretending kawai suke akan maganar suma, dan sunsan wacece Azeema, tunda da saninsu aka ƙulla aurama shi Qaseem ɗin ita, sannan sakin yarinyar zai zama babban kuskurene, akwai wani abu da suke ɓoyewa akan yarinyar, ka bani damar bincikosa sanan, na yarda inhar nine banda gaskiya ka ɗauki kowane hukunci”. Shiru Alhaji baba yay yana kallon Jawaad da nazarin kalamansa a ƙwaƙwalwa, kusan mintuna biyu suna a haka shiru kafin Alhaji baba ya ɗauke kansa daga kallon Jawaad ɗin ya maida ga littafinsa, “Ka dainamin ɓoye-ɓoye, ka fito fili kasanar min abinda ke faruwa?”. Ajiyar zuciya Jay ya sauke da faɗin, “Duk abinda zan faɗa a yanzun zai iya zama kuskuren abinda yake a zahirin gaskiya ne, nima a yanzu bakomai na saniba baba, sai dai insha ALLAH zan binciko duk abinda yake a binne nanda ƙanƙanin lokaci insha ALLAHU”. Tsagwaron gaskiya Alhaji baba ya hango a kalaman Jawaad, hakan yasa bai sake cewa komaiba.
Miƙewa Jay yay ya nufi bedroom ɗin kakan nasa yay kwanciyarsa.
Alhaji baba ya bisa da kallo har saida ya shige, tabbas ya fahimci akwai abinda Jawaad ke ɓoyewa, kuma da alama yanada alaƙa da Uncles ɗin nasa, bazai matsa masaba akan sai yaji komai a yau, dan yasan idan yana fushi takura masa akan abu sake busar masa da zuciya yake, sai dai yasan duk abinda Jawaad ya dage a kansa to lallai akwai abinda ya hango a cikinsa, shi kansa akwai mafarkan da yake a kwanakinnan suna damunsa, ya kuma rasa ina suka dosa?, abin mamakin shine kullum mafarkin maimaita kansa yakeyi, kayi mafarki sau ɗaya sannan ka sake maimaitashi gobe, har tsahon wasu kwanani dolene kasaka masa alamar tambaya koda kaso tureshi a ranka. Tsahon lokaci yana zaune a falon yana tunani bai shiga ɗakinba sai kusan sha ɗaya, lokacin tuni Jawaad yay barcima shi. Shirin barcin yay shima ya hau gadon, idanu ya tairama Jawaad dake barci fuska a ɗaure alamun cikin ɓacin rai yay barcin, Alhaji baba ya sauke numfashi tare da shafa kan jikan nasa, a ƙasan ransa yanajin tausayinsa, gefe kuma yana jin matuƙar tsoron irin hatsabibancin Jawaad da rashin tsoro, yana tsoron kar wani yay amfani da wannan halayyar tasa ya cutar dashi wataran. Da waɗanan tunane-tunanen fal ransa yay barci shima.
★★★★★★
Bayan tafiyar Jawaad Maman Amina ta dawo ɗakin, macece ita mai yawan ibada dama, bata wasa da ibada ko kaɗan, dan haka koda ta dawo saita ɗauro alwala takoma gefen bilkisu ta zauna a kujera dan ganin wata irin zufa da Bilkisu keyi mara dalili, gashi sai mutsu-mutsu take kamar wadda aka saka cikin wuta, Batool kuwa tana gadon mara lafiya ɗaya daya rage a ɗakin tai kwanciyarta itama. Addu'oi maman Amina taita tofama bilkisu dan zufar ta bata mamaki da tsoro, gashi akwai fanka a ɗakin tana aiki kuma, bakuma wani uban zafi akeba a garin balle ace, da alama dai mafarki Bilkisun keyi. Ahankali-ahankali gumin ya fara tsanewa daga goshin bilkisu, ta koma sauke numfashi ahankali saɓanin da datake yinsa da sauri-sauri, takuma nutsu waje ɗaya. Tajima tana mata addu'ar har kusan ƙarfe ɗaya kafin ta miƙe ta shimfiɗa abin salla ta fara nafilfilinta data saba a zaune saboda ƙafarta bata jimirin tsaiwa.
Wani irin sukur-sukur maman Amina keji a ɗakin, tun tana ɗaukar motse-motsen da takejin a wasa hartakai ta fara waige-waige, tabbas tanaji a ranta akwai wani abu a ɗakin da itama bata iya hasasowa ba, tashi tai ta ɗakko jikkarta datazo asibitin da ita ta ciro Qur'anin da tazo da shi, karatu ta fara cikin suratul baƙara, sai motsin da takeji ya ƙara ƙarfi, ɗa
ga kan da zatai sai idanunta yaci karo da wata irin halitta mai kama da ƙadangare yana fitowa daga ƙarƙashin gadon da bilkisu ke kwance, sai dai kuma shi wannan farine fat tamkar babu jini jikinsa, sannan ƙaton gaske kamar kada ta cikin ruwa, jikinsa sai wata iriyar muguwar walƙiya yake tamkar ruwan dake kwance cikin teku, dukda zuciyarta ta girgiza da kallon wannan halitta mai ban tsoro dake nufota sai bakinta bai daina karanto ayoyin alƙur'anin ba kasancewarta jaruma mai dakakkiyar zuciya, tsayawa yay cak a tsakkiyar ɗakin batare da ya ƙaraso gareta ba, ya shiga goga kansa a ƙasan ɗakin kamar wanda ake duka, kafin kuma ya juya bindinsa har gab da ita ya fuskanci ƙofar fita, da gudu ya fice tamkar an masa umarni. Cigaba tai da karatunta har lokacin ta gaza ɗauke idanunta daga ƙofar. Sam Batool batasan wainar da ake toyawaba, barci take kashirɓan, bily ce dai bazamuce ga halin da take cikiba. Sautin karatun alkur'anin da Mmn Amina keyine ya tada Batool, itama samun kanta tai da shiga bayi tayo alwala, ta idar kenan ta miƙe tana gyara ɗan kwalinta zata fito taga wani ƙaton maciji jajur dashi yana silalawa ta Window toilet ɗin zai fita, ƙara ta ƙwalla tare da fitowa a guje jikinta na masifar rawa. Tazo ta ƙanƙame maman Amina dake cigaba da karatu dukda hankalinta yayi masifar tashi da ƙarar Batool ɗin, tanaji a ranta itama wani gamon tai a bayin................✍
Sannu sannu bata hana zuwa saidai a daɗe ba'a zoba. to aljanin daya canja takarda ya bayyana😂, sai muje zuwa domin jin dalilin Jawaad na canjawar da kuma tayaya ya canja ɗin, da alama kuma ya fara bankaɗo wani sirrine da zai bamu hasken sanin ina muka dosa🚴🏼. ALLAH ya daidaita sahun Jawaad akan lokaci😂, bara na fece nidai kafin ya karyani🚴🏼🚴🏼🚴🏼.
Barkanmu da dawowa, ina fatan kunsha weekend lafiya?.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
*ALIMA Episode 1 Latest Hausa Novel*
.
_Surayya Abdulkadir_
.
*Daukar nauyi Aminci Radio kano*
.
Kun dannan Subscribe sannan ku dannan kararrawar sanarwar ta yadda za'a rinƙa sanar da ku da zarar mun ɗora sabon shiri.
.
```For More videos Subscribe to Kurami Tv```
.
👇👇👇
Hi://youtu.be/YlswgJpasVE
_Please share_
[12/9/2020, 5:17 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Bilyn Abdull 📚:
Page 24
Godiya ta musamman ga UMMINRASHIDA CARE FOUNDATION, saƙo ya iso gareni, ina muku fatan alkairin nima, tare da godiyan bangirma da jinjina, alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke. Nagode da wannan girmamawa taku a gareni, duk da har yazu dai bilyn Abdull rarrafe takeyi, Inai muku so irin trillions ɗinnan😍😍😘😘👍🏻
Kiraye-kirayen sallar isha'i da akeyine ya sakashi shiga massallaci, saida aka idar ya shiga gidan. Shima Alhaji baban shigowarsa kenan babu jimawa, Jawaad ya zauna ya gaishesa, amsawa Alhaji baba yay idonsa akan jikam nasa. fuskar Alhaji a ɗaure baba yace, “Daga ina?”. Batare da Jawaad ya kallesaba yace, “Gida”. “Ɗazun kumafa da akaita nemanka a wajen ɗaurin aure?”. “Aiki naje”. Alhaji baba yace, “Humm aiki? Kenan bakasan miya faru a wajen ɗaurin aureba ma?”. Kan Jawaad a ƙasa dan yaƙi yarda su haɗa ido da kakan nasa yace, “Na sani, ninema na canja list ɗin ai”. Idanu Alhaji baba ya ɗago daga littafin addu'oin dake hannunsa ya kafe Jawaad ɗin da kallo, cikin sake ɗaure fuska yace, “Ai nasan bazai wuce kaiɗinbane daman, miyasa kai hakan?”. Kallonsa Jawaad ya ɗago yayi sai kuma ya ɗauke kansa yana wani ɓata fuska, dama yasan ko kowa bai gano shi bane da wuri Alhaji baba sai ya gane.
Alhaji baba yay ƙwafa yana maida kansa ga littafin da faɗin, “A hatsabibancinka dana sani hakan ƙaramin abune a gareka Jawaad, amma ince tun randa mukaje gidan Alhaji Ali akan maganarnan ya tabbatar mana da ɗansa zai aurama yarinyarnan kace ka haƙura?”. “Hakane baba, kamar yanda na faɗa a gabanku na haƙura na barmasa da gasken na haƙuran, sai dai kuma dalilin daya biyo bayane yasa na canja shawara”. Ran Alhaji baba ya fara ɓaci, dan haka cikin zafi yace, “Kasan zan iya saɓa maka ko Muhammad? Har wane irin banzan dalili ka riƙe da bazakazo ka sanar minba kafin ka yanke masa hukunci? Banason wannan shegen taurin kan nakafa kaima ka sani”. Sosai idanun Jawaad suka sake kaɗawa sukai jajur, jijiyar kansa dukta fito ruɗu-ruɗu, yasan duk sanda zaiyi abu saiya zo ya sanarma Alhaji baba, dan a halin yanzu shine kawai ke iya nuna masa ɓacin rai idan ya aikata ba dai-daiba kuma ya tsawatar masa akan ya kiyaye gaba, to amma akan wannan shi kansa baisan miyasa zuciyar
sa taƙi aminta da ya nema sharar kowaba akan batun har sai bayan ya aiwatar..........
“Ina maka magana ka tafi tunani”. Jawaad da maganar Alhaji baba ta maido hayyacinsa yay ajiyar zuciya, cikin sanyin murya yace, “Nayi laifi kayi haƙuri, amma zuwa nan gaba kaɗan zaka fahimci hakan danai shine dai-dai baba......”
“Dai-dai ɗin ƙaniyarka, ka sakar musu yarinya ta auri wanda suka zaɓa mata, shikuma wancan habibun halan shima kaine ka kawosu shi da Azeemar? Tunda kasan har cikin ranka bakason maida yarinyarnan miyasa ka amincemin zaka maidatan?”.
“Baba nifa bani na kawosuba, su Uncle Nasir pretending kawai suke akan maganar suma, dan sunsan wacece Azeema, tunda da saninsu aka ƙulla aurama shi Qaseem ɗin ita, sannan sakin yarinyar zai zama babban kuskurene, akwai wani abu da suke ɓoyewa akan yarinyar, ka bani damar bincikosa sanan, na yarda inhar nine banda gaskiya ka ɗauki kowane hukunci”. Shiru Alhaji baba yay yana kallon Jawaad da nazarin kalamansa a ƙwaƙwalwa, kusan mintuna biyu suna a haka shiru kafin Alhaji baba ya ɗauke kansa daga kallon Jawaad ɗin ya maida ga littafinsa, “Ka dainamin ɓoye-ɓoye, ka fito fili kasanar min abinda ke faruwa?”. Ajiyar zuciya Jay ya sauke da faɗin, “Duk abinda zan faɗa a yanzun zai iya zama kuskuren abinda yake a zahirin gaskiya ne, nima a yanzu bakomai na saniba baba, sai dai insha ALLAH zan binciko duk abinda yake a binne nanda ƙanƙanin lokaci insha ALLAHU”. Tsagwaron gaskiya Alhaji baba ya hango a kalaman Jawaad, hakan yasa bai sake cewa komaiba.
Miƙewa Jay yay ya nufi bedroom ɗin kakan nasa yay kwanciyarsa.
Alhaji baba ya bisa da kallo har saida ya shige, tabbas ya fahimci akwai abinda Jawaad ke ɓoyewa, kuma da alama yanada alaƙa da Uncles ɗin nasa, bazai matsa masaba akan sai yaji komai a yau, dan yasan idan yana fushi takura masa akan abu sake busar masa da zuciya yake, sai dai yasan duk abinda Jawaad ya dage a kansa to lallai akwai abinda ya hango a cikinsa, shi kansa akwai mafarkan da yake a kwanakinnan suna damunsa, ya kuma rasa ina suka dosa?, abin mamakin shine kullum mafarkin maimaita kansa yakeyi, kayi mafarki sau ɗaya sannan ka sake maimaitashi gobe, har tsahon wasu kwanani dolene kasaka masa alamar tambaya koda kaso tureshi a ranka. Tsahon lokaci yana zaune a falon yana tunani bai shiga ɗakinba sai kusan sha ɗaya, lokacin tuni Jawaad yay barcima shi. Shirin barcin yay shima ya hau gadon, idanu ya tairama Jawaad dake barci fuska a ɗaure alamun cikin ɓacin rai yay barcin, Alhaji baba ya sauke numfashi tare da shafa kan jikan nasa, a ƙasan ransa yanajin tausayinsa, gefe kuma yana jin matuƙar tsoron irin hatsabibancin Jawaad da rashin tsoro, yana tsoron kar wani yay amfani da wannan halayyar tasa ya cutar dashi wataran. Da waɗanan tunane-tunanen fal ransa yay barci shima.
★★★★★★
Bayan tafiyar Jawaad Maman Amina ta dawo ɗakin, macece ita mai yawan ibada dama, bata wasa da ibada ko kaɗan, dan haka koda ta dawo saita ɗauro alwala takoma gefen bilkisu ta zauna a kujera dan ganin wata irin zufa da Bilkisu keyi mara dalili, gashi sai mutsu-mutsu take kamar wadda aka saka cikin wuta, Batool kuwa tana gadon mara lafiya ɗaya daya rage a ɗakin tai kwanciyarta itama. Addu'oi maman Amina taita tofama bilkisu dan zufar ta bata mamaki da tsoro, gashi akwai fanka a ɗakin tana aiki kuma, bakuma wani uban zafi akeba a garin balle ace, da alama dai mafarki Bilkisun keyi. Ahankali-ahankali gumin ya fara tsanewa daga goshin bilkisu, ta koma sauke numfashi ahankali saɓanin da datake yinsa da sauri-sauri, takuma nutsu waje ɗaya. Tajima tana mata addu'ar har kusan ƙarfe ɗaya kafin ta miƙe ta shimfiɗa abin salla ta fara nafilfilinta data saba a zaune saboda ƙafarta bata jimirin tsaiwa.
Wani irin sukur-sukur maman Amina keji a ɗakin, tun tana ɗaukar motse-motsen da takejin a wasa hartakai ta fara waige-waige, tabbas tanaji a ranta akwai wani abu a ɗakin da itama bata iya hasasowa ba, tashi tai ta ɗakko jikkarta datazo asibitin da ita ta ciro Qur'anin da tazo da shi, karatu ta fara cikin suratul baƙara, sai motsin da takeji ya ƙara ƙarfi, ɗa
ga kan da zatai sai idanunta yaci karo da wata irin halitta mai kama da ƙadangare yana fitowa daga ƙarƙashin gadon da bilkisu ke kwance, sai dai kuma shi wannan farine fat tamkar babu jini jikinsa, sannan ƙaton gaske kamar kada ta cikin ruwa, jikinsa sai wata iriyar muguwar walƙiya yake tamkar ruwan dake kwance cikin teku, dukda zuciyarta ta girgiza da kallon wannan halitta mai ban tsoro dake nufota sai bakinta bai daina karanto ayoyin alƙur'anin ba kasancewarta jaruma mai dakakkiyar zuciya, tsayawa yay cak a tsakkiyar ɗakin batare da ya ƙaraso gareta ba, ya shiga goga kansa a ƙasan ɗakin kamar wanda ake duka, kafin kuma ya juya bindinsa har gab da ita ya fuskanci ƙofar fita, da gudu ya fice tamkar an masa umarni. Cigaba tai da karatunta har lokacin ta gaza ɗauke idanunta daga ƙofar. Sam Batool batasan wainar da ake toyawaba, barci take kashirɓan, bily ce dai bazamuce ga halin da take cikiba. Sautin karatun alkur'anin da Mmn Amina keyine ya tada Batool, itama samun kanta tai da shiga bayi tayo alwala, ta idar kenan ta miƙe tana gyara ɗan kwalinta zata fito taga wani ƙaton maciji jajur dashi yana silalawa ta Window toilet ɗin zai fita, ƙara ta ƙwalla tare da fitowa a guje jikinta na masifar rawa. Tazo ta ƙanƙame maman Amina dake cigaba da karatu dukda hankalinta yayi masifar tashi da ƙarar Batool ɗin, tanaji a ranta itama wani gamon tai a bayin................✍
Sannu sannu bata hana zuwa saidai a daɗe ba'a zoba. to aljanin daya canja takarda ya bayyana😂, sai muje zuwa domin jin dalilin Jawaad na canjawar da kuma tayaya ya canja ɗin, da alama kuma ya fara bankaɗo wani sirrine da zai bamu hasken sanin ina muka dosa🚴🏼. ALLAH ya daidaita sahun Jawaad akan lokaci😂, bara na fece nidai kafin ya karyani🚴🏼🚴🏼🚴🏼.
Barkanmu da dawowa, ina fatan kunsha weekend lafiya?.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
*ALIMA Episode 1 Latest Hausa Novel*
.
_Surayya Abdulkadir_
.
*Daukar nauyi Aminci Radio kano*
.
Kun dannan Subscribe sannan ku dannan kararrawar sanarwar ta yadda za'a rinƙa sanar da ku da zarar mun ɗora sabon shiri.
.
```For More videos Subscribe to Kurami Tv```
.
👇👇👇
Hi://youtu.be/YlswgJpasVE
_Please share_
[12/9/2020, 5:17 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Bilyn Abdull 📚:
Page 24
Godiya ta musamman ga UMMINRASHIDA CARE FOUNDATION, saƙo ya iso gareni, ina muku fatan alkairin nima, tare da godiyan bangirma da jinjina, alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke. Nagode da wannan girmamawa taku a gareni, duk da har yazu dai bilyn Abdull rarrafe takeyi, Inai muku so irin trillions ɗinnan😍😍😘😘👍🏻