Sashe 106
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
arya nakeyi, kagani ko tamkar kai, Anuwar wlhy bari kaji yay bagana muryarku iri ɗaya ne shima. Anuwar da ya kasa bama Anum amsa ya wani rinƙa fisgar numfashi da ƙyar yana sake matse kansa cikin hannayensa yana jujjuyashi. “Anum kaina zai fashe, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, wash ALLAH kaina......”
Yanda yay maganar tamkar numfashinsa zai ɗauke baki ɗayane ya kuma tadamana hankali mukai kansa mu duka. Duk yanda nake zumuɗin son ganin yanayin dazasu shiga idan sun haɗu da juna sai hankalina ya tashi.
Ƙarar da Anum ta ƙwalla ce ta maido Jawaad da shima yake riƙe da kansa hayacinsa yay kan Anuwar jiki na rawa. Karɓarsa yay daga cinyar Anum ya maidosa jikinsa yana girgizashi. Sai dai ina numfashin Anuwar ya ɗauke ɗaf, Nabeelah da tun zuwan su Anuwar ta shiga ruɗani hartai masa video cikin hikima batare da kowa ya saniba ta matso tana faɗin, “Yayanmu a kawo ruwa ka zuba masa?”. Kansa kawai ya jinjina mata yana cigaba da ɗan bubbuga fuskar Anuwar da girgizasa. Nabeelah na kawo ruwar Abdul-raheem ya amsa, shine ya shafama Anuwar a fuska, wani irin nannauyan numfashi ya sauke. Jawaad ma ya sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yana lumshe idanunsa ya buɗewa akan Anuwar da shima ya buɗe nasa a hankali, kallon juna suke kallo irin na ruɗani da al'ajabi, basu da suke ganin kamainin nasu da junaba hatta su Bilkisu al'amarin ya kuma ruɗar dasu, dan ita saima yanzun data gansu a waje ɗaya ta sake tabbatar da hukuncin ubangiji, dai-dai da wani ɗan ɗigon baƙi dake gab da kunnen Jay akwaishi a jikin Anuwar shima exactly yanda na Jawaad ɗin yake.......
Jawaad ya kwantar da Anuwar jikin Ameen a hankali ya miƙe yabar wajen dan jikinsa wani irin tsuma yakeyi, idan kuma yay wasa shima hajijiyar zata iya kwasarsa ne takai ƙasa kamar yanda taima Anuwar.
Ruwa na ɗauka da sauri nabi bayansa dan tafiya yake yana haɗa hanya, Zaune na samesa a saman gado ya riƙe kansa da dukan hannayensa biyu, saurin ƙarasawa inda yake nayi ina faɗin, “Boss lafiya?”. hannuna ya riƙo cikin nashi tare da fisgoni na faɗa jikinsa, wata runguma data nema saka ƙirjina buɗewa yay min, ƙaramar ƙarar da nai ta sakashi sassautamin, muduka muka shiga sauke numfashi, munkai tsahon mintuna biyar a haka kafin ya miƙe dani zaune sosai a bakin gadon ya zauna tare da riƙo hannuna ya zaunar dani a kusa da shi. “Wanene wannan Miemaa? A ina kika sanshi?”. ƙasa nai da kaina dan gujema kallon daya kafeni da shi. saurin ɗago fuskata yayi muna kallon juna sosai, “Please Miemaa ba batun kunya mukeba, ki faɗamin wanene shi?”. “Bansan wanene shiba nima, sai dai nasan shiɗin ɗan Umm-Anum dana zauna a wajen tane, mamarsa itace na zauna wajenta a saudiyya sati biyun nan”. “Saudia?, kina nufin daga can yazo nan?”. “ƙwaraima kuwa harda ƙanwarsa ma Anum”.
Yace, “Innalillahi... mi hakan ke nufi? Wane irin kamannine wannan? Babu ta indafa yaron nan baya kama dani Miemaa?”. “Irin wannan ruɗanin nima na shiga a randa muka fara haɗuwa dasu, da yay magana wlhy nazata kaine, sai daga baya na iya fahimtar ba haka baneba, amma boss kafin Mamah ta rasu bata haifa maka ƙani bane?”. Yanda ya kafeni da idanunsa ya sakani yin ƙasa da nawa gabana na faɗuwa. Ya ɗora duka hannayensa saman fuskata ya ɗago, “Bilkisu Mamata ba rasuwa tayiba”. Yay maganar yana sakin fuskata ya miƙe zumbur yana girgiza kansa. saurin riƙo hannunsa nayi nima ganin zai fita a ɗakin, “Miya faru?”. Saurin dawowa yay ya sake zama. Muryarsa har sarƙewa take yace, “Inason ganin mamar yaran nan”. Bansan lokacin danai wata zabura ba nima ina faɗin, “Ganinta ba matsala bane, amma dan ALLAH da gaske kakeyi mama ba rasuwa tayi ba? To tana inane?”. Yanda nai masifar rikicewane ya sakashi kamo hannuna ya maidani inda nake ya zaunar shima yana wani kafeni da idanu fiye da ko yaushe, “Labarina mai tsahone, namiki alƙawarin a yau zakiji komai daya shafi mijinki, dan kema a yanzu kin zama ɗaya daga cikin family na, kobabu alaƙar jini a tsakaninmu ke matata ce, amma tabbas kamar yanda baba ƙaura ya faɗa Ƙaddarata tana tare da taki”. Cike da mamakin kalamansa nake kallonsa, amma fahimtar danai baya cikin hayyacin
sa, shiyyasa nai tunanin yana buƙatar yafara yin wanka yaci abinci sannan. nace, “Kayi haƙuri to ka fara yin wanka kaci abinci sannan dan magriba na gab”. Baice dani komaiba sai kallona da yakeyi har yanzun, hakan yasa na miƙe na shiga bayi. Ruwan wanka na haɗa masa, inda na barsa anan nazo na sake samunsa. Sai dai yanzu riƙe yake da kofi a hannu alamar yana shan ruwa. “Ga ruwan can?”. Idanunsa ya ɗago ya kalleni da miƙomin hanunsa na haggu. Baya naja ina maƙe kafaɗa nace, “Kaje kayi wanka bara na duba su Anuwar ɗin”. Muryarsa ƙasa-ƙasa yace, “Dama ɗazun kin kashemin waya, yanzu kuma nace kizo zaki gudu, laifi biyu kenan nasan maganinki ai, zaki biya bashinsune”.
Saida na kusa zuwa ƙofa sannan na juyo ina faɗin, “To nima idan na kiraka a waya ka kashe shikenan ai ka rama ko?”. Miƙewa yay yana ɓalle maɓallan rigarsa, “Ai nafi ƙarfin ramawa ta haka yarinya”. Tsayawa nai ina kallonsa fuskata a marairaice, “To gani na dawo ai, amma dan ALLAH faɗamin ta yaya zaka rama? Nifa ɗazun wlhy bansan mizan baka bane shiyyasa na kashe”. “Kin tabbatar?”. Kaina na ɗaga masa. Yay murmushi kawai batare da ya sake cewa komaiba. Hakan yasa nace, “Naje dan ALLAH? Kaga an barsu su kaɗai”. Kansa kawai ya ɗagamin. Nikam tuni nai waje. Mamakine ya kamani ganin falon wayam, na leƙa ɗayan falon har zuwa ɗakina nanma babu kowa, a rikice na fito harabar gidan saina iske babu motarsu, abinda ya sake ɗaure kaina har Nabeelah babu itama. Dawowa nai ɗakinsa danna sanar masa saina iske harya shiga wankan, da sauri na ɗauki wayarsa dan tawa babu kuɗi ciki na shiga laluben sunan Ummu. Bugu biyu kuwa ta ɗaga tamkar dama jira take. Kafin tai magana nai sallama dan karta ɗauka ko shine, ko gaisheta ban tsaya yiba nace, “Ummu.......” katseni tai itama da faɗin nasan mizaki tambaya kwantar da hankalinki, Anuwar ne ya sake suma shiyyasa nace su taho gida, yana da Asthma shiyyasa gashi basu taho dako inhaler ɗinsa ba ma, sun faɗamin komai daya faru yanzu ina mijin naki shi?”. Ya shiga wanka Ummu, ya kumace zai sanarmin da komai daya shafesa”. “Alhmdllh mu dama wannan muke jira ai, saiki nutsu sosai ki fahimci komai yanda yake, ta hakane zamu tabbatar da abinda yake gaskiya, sannan nasan zai iya cewa zai biyosu idan ya fito yaji sun taho, karki faɗa masa Anuwar ɗin yana cikin wani haline, nafiso sai zuwa da safe idan ALLAH ya kaimu inma zaizo ɗin kuzo tare”. “To Ummu insha ALLAHU zanyi hakan, amma inaji a raina wlhy abinda muke zargin gaskiyane, dan yace mamarsa bata rasuba”. “Da gaske?”. “Wlhy kuwa Ummu”. “To shikenan bara na barki karya fito”.
Ummu na yanke wayar kuwa na goge kiran na dawo ɗakin na ajiye masa wayarsa, fita na sakeyi domin yin salla nima dan anata kira.
Koda Jawaad ya fito a gaggauce yay shiri ya fita massallaci, bai kawo komai a ransa game da rashin ganinsuba a falon, yayi zaton sun tafi salla matan kuma sun shige ciki, yanayin da yake ciki kuma ya saka bai kula da babu motarsu a harabar gidanba.
Ana idar da salla gida ya nufo, dai-dai Bilkisu itama ta fito daga kicin tana haɗa masa abinci a d/table. Tsayawa yay kawai yana kallonta daga cikin falon...
Jin idanu na yawo kaina ya sakani ɗagowa nima, cikin sanyin murya nace, “Ga abinci”.
Ɗauke kansa yay daga gareni, ya tako zuwa dani ɗin yaja kujera ya zauna, “Su suna ina?”. “Sun tafi”. Na faɗa ina ƙoƙarin zuba masa abincin, Da sauri ya ɗago ya kalleni, “Bangane sun tafi ba, miyasa?”. “Takawane ya kira yace su koma gida hakanan”.
“Aiko dolene na nabi bayansu dan zuciyata ta kasa samun nutsuwa, inason yima yaronan tambayoyi”. Saurin zuwa nai gabansa murya a sanyaye nace, “Kayi haƙuri zuwa safiya mana, nima akwai abubuwa da yawa dazan faɗa maka game dasu wanda tunda naga kamaninka dasu naita samowa dama dan na kawosu gareka”. Murmushi yayi ya jawoni kawai ya rungume a jikinsa batare da yace komaiba.............✍
Maganar gaskiya man kaina ya gama tsiyayewa antafi yajin aiki daga yau😓😫🚶🏻.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAF
[1/6, 5:08 PM] Abbu Saleh Kurami: SAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
Domin samun littafin Ƙwai cikin ƙaya daga farkon ko taɓa Link ɗin da ke ƙasa.
👇👇👇👇
.
https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🥚Ƙwai Ciki Ƙaya🥚
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 45
Yanda yay maganar tamkar numfashinsa zai ɗauke baki ɗayane ya kuma tadamana hankali mukai kansa mu duka. Duk yanda nake zumuɗin son ganin yanayin dazasu shiga idan sun haɗu da juna sai hankalina ya tashi.
Ƙarar da Anum ta ƙwalla ce ta maido Jawaad da shima yake riƙe da kansa hayacinsa yay kan Anuwar jiki na rawa. Karɓarsa yay daga cinyar Anum ya maidosa jikinsa yana girgizashi. Sai dai ina numfashin Anuwar ya ɗauke ɗaf, Nabeelah da tun zuwan su Anuwar ta shiga ruɗani hartai masa video cikin hikima batare da kowa ya saniba ta matso tana faɗin, “Yayanmu a kawo ruwa ka zuba masa?”. Kansa kawai ya jinjina mata yana cigaba da ɗan bubbuga fuskar Anuwar da girgizasa. Nabeelah na kawo ruwar Abdul-raheem ya amsa, shine ya shafama Anuwar a fuska, wani irin nannauyan numfashi ya sauke. Jawaad ma ya sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yana lumshe idanunsa ya buɗewa akan Anuwar da shima ya buɗe nasa a hankali, kallon juna suke kallo irin na ruɗani da al'ajabi, basu da suke ganin kamainin nasu da junaba hatta su Bilkisu al'amarin ya kuma ruɗar dasu, dan ita saima yanzun data gansu a waje ɗaya ta sake tabbatar da hukuncin ubangiji, dai-dai da wani ɗan ɗigon baƙi dake gab da kunnen Jay akwaishi a jikin Anuwar shima exactly yanda na Jawaad ɗin yake.......
Jawaad ya kwantar da Anuwar jikin Ameen a hankali ya miƙe yabar wajen dan jikinsa wani irin tsuma yakeyi, idan kuma yay wasa shima hajijiyar zata iya kwasarsa ne takai ƙasa kamar yanda taima Anuwar.
Ruwa na ɗauka da sauri nabi bayansa dan tafiya yake yana haɗa hanya, Zaune na samesa a saman gado ya riƙe kansa da dukan hannayensa biyu, saurin ƙarasawa inda yake nayi ina faɗin, “Boss lafiya?”. hannuna ya riƙo cikin nashi tare da fisgoni na faɗa jikinsa, wata runguma data nema saka ƙirjina buɗewa yay min, ƙaramar ƙarar da nai ta sakashi sassautamin, muduka muka shiga sauke numfashi, munkai tsahon mintuna biyar a haka kafin ya miƙe dani zaune sosai a bakin gadon ya zauna tare da riƙo hannuna ya zaunar dani a kusa da shi. “Wanene wannan Miemaa? A ina kika sanshi?”. ƙasa nai da kaina dan gujema kallon daya kafeni da shi. saurin ɗago fuskata yayi muna kallon juna sosai, “Please Miemaa ba batun kunya mukeba, ki faɗamin wanene shi?”. “Bansan wanene shiba nima, sai dai nasan shiɗin ɗan Umm-Anum dana zauna a wajen tane, mamarsa itace na zauna wajenta a saudiyya sati biyun nan”. “Saudia?, kina nufin daga can yazo nan?”. “ƙwaraima kuwa harda ƙanwarsa ma Anum”.
Yace, “Innalillahi... mi hakan ke nufi? Wane irin kamannine wannan? Babu ta indafa yaron nan baya kama dani Miemaa?”. “Irin wannan ruɗanin nima na shiga a randa muka fara haɗuwa dasu, da yay magana wlhy nazata kaine, sai daga baya na iya fahimtar ba haka baneba, amma boss kafin Mamah ta rasu bata haifa maka ƙani bane?”. Yanda ya kafeni da idanunsa ya sakani yin ƙasa da nawa gabana na faɗuwa. Ya ɗora duka hannayensa saman fuskata ya ɗago, “Bilkisu Mamata ba rasuwa tayiba”. Yay maganar yana sakin fuskata ya miƙe zumbur yana girgiza kansa. saurin riƙo hannunsa nayi nima ganin zai fita a ɗakin, “Miya faru?”. Saurin dawowa yay ya sake zama. Muryarsa har sarƙewa take yace, “Inason ganin mamar yaran nan”. Bansan lokacin danai wata zabura ba nima ina faɗin, “Ganinta ba matsala bane, amma dan ALLAH da gaske kakeyi mama ba rasuwa tayi ba? To tana inane?”. Yanda nai masifar rikicewane ya sakashi kamo hannuna ya maidani inda nake ya zaunar shima yana wani kafeni da idanu fiye da ko yaushe, “Labarina mai tsahone, namiki alƙawarin a yau zakiji komai daya shafi mijinki, dan kema a yanzu kin zama ɗaya daga cikin family na, kobabu alaƙar jini a tsakaninmu ke matata ce, amma tabbas kamar yanda baba ƙaura ya faɗa Ƙaddarata tana tare da taki”. Cike da mamakin kalamansa nake kallonsa, amma fahimtar danai baya cikin hayyacin
sa, shiyyasa nai tunanin yana buƙatar yafara yin wanka yaci abinci sannan. nace, “Kayi haƙuri to ka fara yin wanka kaci abinci sannan dan magriba na gab”. Baice dani komaiba sai kallona da yakeyi har yanzun, hakan yasa na miƙe na shiga bayi. Ruwan wanka na haɗa masa, inda na barsa anan nazo na sake samunsa. Sai dai yanzu riƙe yake da kofi a hannu alamar yana shan ruwa. “Ga ruwan can?”. Idanunsa ya ɗago ya kalleni da miƙomin hanunsa na haggu. Baya naja ina maƙe kafaɗa nace, “Kaje kayi wanka bara na duba su Anuwar ɗin”. Muryarsa ƙasa-ƙasa yace, “Dama ɗazun kin kashemin waya, yanzu kuma nace kizo zaki gudu, laifi biyu kenan nasan maganinki ai, zaki biya bashinsune”.
Saida na kusa zuwa ƙofa sannan na juyo ina faɗin, “To nima idan na kiraka a waya ka kashe shikenan ai ka rama ko?”. Miƙewa yay yana ɓalle maɓallan rigarsa, “Ai nafi ƙarfin ramawa ta haka yarinya”. Tsayawa nai ina kallonsa fuskata a marairaice, “To gani na dawo ai, amma dan ALLAH faɗamin ta yaya zaka rama? Nifa ɗazun wlhy bansan mizan baka bane shiyyasa na kashe”. “Kin tabbatar?”. Kaina na ɗaga masa. Yay murmushi kawai batare da ya sake cewa komaiba. Hakan yasa nace, “Naje dan ALLAH? Kaga an barsu su kaɗai”. Kansa kawai ya ɗagamin. Nikam tuni nai waje. Mamakine ya kamani ganin falon wayam, na leƙa ɗayan falon har zuwa ɗakina nanma babu kowa, a rikice na fito harabar gidan saina iske babu motarsu, abinda ya sake ɗaure kaina har Nabeelah babu itama. Dawowa nai ɗakinsa danna sanar masa saina iske harya shiga wankan, da sauri na ɗauki wayarsa dan tawa babu kuɗi ciki na shiga laluben sunan Ummu. Bugu biyu kuwa ta ɗaga tamkar dama jira take. Kafin tai magana nai sallama dan karta ɗauka ko shine, ko gaisheta ban tsaya yiba nace, “Ummu.......” katseni tai itama da faɗin nasan mizaki tambaya kwantar da hankalinki, Anuwar ne ya sake suma shiyyasa nace su taho gida, yana da Asthma shiyyasa gashi basu taho dako inhaler ɗinsa ba ma, sun faɗamin komai daya faru yanzu ina mijin naki shi?”. Ya shiga wanka Ummu, ya kumace zai sanarmin da komai daya shafesa”. “Alhmdllh mu dama wannan muke jira ai, saiki nutsu sosai ki fahimci komai yanda yake, ta hakane zamu tabbatar da abinda yake gaskiya, sannan nasan zai iya cewa zai biyosu idan ya fito yaji sun taho, karki faɗa masa Anuwar ɗin yana cikin wani haline, nafiso sai zuwa da safe idan ALLAH ya kaimu inma zaizo ɗin kuzo tare”. “To Ummu insha ALLAHU zanyi hakan, amma inaji a raina wlhy abinda muke zargin gaskiyane, dan yace mamarsa bata rasuba”. “Da gaske?”. “Wlhy kuwa Ummu”. “To shikenan bara na barki karya fito”.
Ummu na yanke wayar kuwa na goge kiran na dawo ɗakin na ajiye masa wayarsa, fita na sakeyi domin yin salla nima dan anata kira.
Koda Jawaad ya fito a gaggauce yay shiri ya fita massallaci, bai kawo komai a ransa game da rashin ganinsuba a falon, yayi zaton sun tafi salla matan kuma sun shige ciki, yanayin da yake ciki kuma ya saka bai kula da babu motarsu a harabar gidanba.
Ana idar da salla gida ya nufo, dai-dai Bilkisu itama ta fito daga kicin tana haɗa masa abinci a d/table. Tsayawa yay kawai yana kallonta daga cikin falon...
Jin idanu na yawo kaina ya sakani ɗagowa nima, cikin sanyin murya nace, “Ga abinci”.
Ɗauke kansa yay daga gareni, ya tako zuwa dani ɗin yaja kujera ya zauna, “Su suna ina?”. “Sun tafi”. Na faɗa ina ƙoƙarin zuba masa abincin, Da sauri ya ɗago ya kalleni, “Bangane sun tafi ba, miyasa?”. “Takawane ya kira yace su koma gida hakanan”.
“Aiko dolene na nabi bayansu dan zuciyata ta kasa samun nutsuwa, inason yima yaronan tambayoyi”. Saurin zuwa nai gabansa murya a sanyaye nace, “Kayi haƙuri zuwa safiya mana, nima akwai abubuwa da yawa dazan faɗa maka game dasu wanda tunda naga kamaninka dasu naita samowa dama dan na kawosu gareka”. Murmushi yayi ya jawoni kawai ya rungume a jikinsa batare da yace komaiba.............✍
Maganar gaskiya man kaina ya gama tsiyayewa antafi yajin aiki daga yau😓😫🚶🏻.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAF
[1/6, 5:08 PM] Abbu Saleh Kurami: SAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
Domin samun littafin Ƙwai cikin ƙaya daga farkon ko taɓa Link ɗin da ke ƙasa.
👇👇👇👇
.
https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🥚Ƙwai Ciki Ƙaya🥚
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 45