← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 167 OF 168

Sashe 167

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

             A ɓangaren rose kam ta buga ta buga taga babu ci, mai shiga tsakanin soyayyar Jawaad da Bilkisu sai dai ALLAH. Babu kalar ƙulle-ƙulle da munafurcin da bataima bily ba a station ɗin sai dai babu tasiri, daga ƙarshema da Jawaad ya ganota sai yasa akai mata transfer waje mai nisa a tsakaninsu. Wannan abu ya sakata jin takaici harda kukanta kuwa, ballema randa taji anƙarama su bily girma da ƙyaututtuka susucewa tayi duk da itama harda ita, a ganinta bily batakai ta kamotaba, amma ya ta iya da abinda yafi ƙarfin wuta inji kishiyar ƙonanniya. tana kewar jawaad ainun. dan koba komai idan tana ganinsa kusa da ita tana ɗanjin sassauci.

__________________
ZAFAFA 2021
_______________

             Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.

       Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥

★★★★

     A gidan Iyayen gayya kuwa ai ba'a cewa komai, cikin Bilkisu da har yanzu gata nanneda ya fito sosai, dan yana cikin wata na bakwai. Tattali sosai take samu a wajan Jawaad da duk ahalinsuma baki ɗaya, inda aka maido mata Nabeelah gidan tana tayata zama, gefe kuma tana shan soyayyarta da masoyinta Anuwar.
          Faruwar wannan al'amari ya sake maida bily miskilar gaske, dan ko Jawaad ɗin idan bata gadamaba saita yini batai masa maganar data zarta gomaba. Ta ƙara ƙwazo akan aikinta fiye da zaton mai hasashe, musamman ma da bayan lafawar abubuwa suka samu ƙarin girma itada duk jami'an da sukaje wannan aiki a waccan rana. Saboda cikinta dai bata fita operation, sai dai tayi ayyukan cikin gida kawai daga office. A gefe kuma tana sake samun ƙwazo da horo a wajen mijinta, wanda a kullum cikin sake nuna mata ƙauna da soyayya mai tsanani yake. Sam baison yaga tashin hankalinta ko damuwarta balle fushinta. Shidai fatansa ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo masa little Beejay kamar yanda yake faɗa a kullum.

          Cikin Bilkisu nada watanni taƙwas Jawaad ya sakata ɗaukar hutun dole, acewarsa saita haihu ƴarsa tayi ƙwari sanan. Aranar da hakan ta faru harda kukanta, amma sai yaƙi kulatama yay kamar bai jitaba, sai Anuwar dake mata dariya shi da Nabeelah suka koma lallashinta da lallaɓata.
        Tana shiga watan haihuwa Ummah babba tace zata maidata can gidanta, dan bazai yuwu a barta ta zauna nan babu babba tare da ita ba. Babu kunya Jawaad ya murje idanu yace shifa bai yardaba, idan dan babbane ya amince asamo wata tsohuwar ta zauna da ita, amma shi bai yarda matarsa tai nesa da shiba gaskiya.
     Ranar Bily ta tasashi gaba ta dinga kwasar dariyar mugunta, dan kawai ta rama abinda yay mata na sakata ɗaukar hutu a office saita shiya kaya kusan akwai huɗu na tafiya gidan Ummah babba, aiko ya murje ido ya balbaleta da masifa kamar zai cinyeta ɗanya jagab🤣.
      Aifa ganin yanda ya harzuƙa dole Ummah babba ta janye ƙudirinta, aka samo wata dattijuwa zata zauna dasu, ga kuma Nabeelah da Anuwar tare dasu. Ummah ƙarama da babba kusan kullum saisunje ganinta. Hakama maman Amina, dan cikin na shiga wata tara sai ya ƙara girma kamar wadda zata haifa ƴan biyu.

       ★★★★★★

A wannan ɗan tsakanin akasha bikin su Amaturrahman suma, inda Bilkisu ko sau ɗaya bata samu leƙawaba saboda cikinta, Jay yace idan ta haihu taje taima Ummu ALLAH ya sanya alkairi.
        Bayan anyi biki an shashshare Umm-Anum da itama ta halarta da Aunty Mahfuzah sukazo nan dansu gaisa da Alhaji babba. Randa suka cika kwana uku gidan Alhaji babban sai sukazo nan gidan Jay duba bily, danshi kullum yana zuwa can ya gaidasu, itako saita waya tunda bata fita sam.
        Ta taresu da tsantsar farin ciki, inda sukuma suketajin tausayinta da mata fatan sauka lafiya. Su Anuwar ne dai ke amsawa, itako kanta na a ƙasa dan kunya.
     Anuwar ya kumbura fuska yana kallon Umm-Anum daketa mammatsa ma bily hannunta daya kumbura. “Umm-Anum gaskiya nimafa amin aure, so kuke sai little tazo duniya taga Abbanta tuzuru”.
       Dariya duk suka sanya ƴan falon, banda Jay dake zaune gefen Umm-Anum yana latsa waya, yadai ɗan ɗago ya kalli Anuwar ɗin ya zuba masa harara ya ɗauke kansa. Sai da suka gama dariyarsu sannan ya sake kallonsa fuska babu wasa. “Kai baka da kunya ko......?” “A'a yayanmu nifa wlhy gaskiya na faɗa, yanzu dan ALLAH little zataji daɗine idan aka haifota ta iskeni babu aure, ita dai ai nasan tanason iske kawunta a dattijonsa ko”. Kai kawai Jay ya girgiza ya sake ɗauke kansa, dan indai shaƙiyancine akazo wajen Anuwar kowa ya shafama kansa lafiya, duk masifarsa kuresa yake shima har yagaza cewa komai.
     Umm-Anum da itama ke dariya yanzun tace, “To ni miye nawa, aiga mai maka auren nan a gabanka” tai maganar tana nuna Jay. Tasowa yay ya tsuguna a gaban Jay ɗin yana wani marairaice fuska. “Yayanmu dan ALLAH ka aurar dani kar a haifi little ina a ƙasa” yay maganar cikin harshen nasara da haɗawa da ƴar hausar daya fara kowa wajen Nabeelah”. Kunnensa Jay ya kama ya murɗa da ƙarfi, aiko a take yahau roƙo daban haƙuri. su Bily kuma namasa dariya.
     Cak ta tsaya daga dariyar tata jin bayanta ya riƙe, ta shiga yamutsa fuska tanason fiskewa amma hakan ya gagara, kamar wasa saiga ƙaramar magana ta zama babba, dan kuwa kafin wani dogon lokaci naƙuda ta tashi gadan-gadan, dama a gaba ɗaya kwanakinan naƙudar tsaye takeyi.
       Cike da rikicewa Jay ya sugunmeta daga ita har cikin sai mota, Anuwar ya jasu sai asibiti.

BAYAN AWA BIYAR.

        Bayan gumurzu da wahalar da bily tasha a ɗakin haihuwa ta sunkuto ɗiyarta mai kama da ubanta sak, dan yarinyafa tun bata gama hucewaba kamanin Jawaad ɓaro-ɓaro a fuskarta, sai dai kalar fatarta tazo daɗan duhu saɓanin yanda ake haihuwar jarirai farare tas.
      Ai murna wajen wannan ahali ba'a magana, a take Jay ya tauna dabino ya zuba mata a baki tare da miƙama Anuwar yay mata huɗiba da suna BILKEESU MAI GADON ZINARI, Alƙawarin ALLAH ya cika, Jawaad Abdul-aziz yousif ya zama Ɗan BILKEESU, mijin BILKEESU, baban BILKEESU, saura kakan BILKEESU🙄😜🤣lol.

          A ranar aka sallami mai jego da jinjirarta dan suna cikin ƙoshin lafiya, bakin Jay ya kasa rufuwa, ya murje idanu sai kulawa yakebama matarsa da ƴarsa a gaban kowa.
     Washe gari ƴan barka suka fara ɓarkowa ta ko ina, ciki kuwa harda Shahudah dataita kuka dan damuwa, yayinda takejin zafi da tsanar bily har cikin ranta. (Shiriyar wanifa sai ALLAH yaso, bashi yuwuwa lokacin damu mukaso😫).
      Yah Qaseem ma ya kawo ƴar Aminatunsa, hakama matan su Jabeer dasu Ummie da abokan aikinsu harma da ƙawayen makaranta. Bily kam tayi goshi, kaga ƴar gatan dangi. Baba ƙaura ma daya koma daji abinsa tuni sai gashi yazo, dan yace yafi son zaman can, alkairan da manyan ƙasa sukai masa dasu Jawaad duk tattarawa yay ya bada gidan marayu, acewarsa sun fishi buƙata, sai dai ya riƙe waya suna gaisawa da abokan arziki irinsu jay, tananma ya sanar masa da haihuwar anayinta.

         Su Umm-Anum basu komaba har saida akai suna, inda kowa dai yasan sunan jinjira BILKEESU. Su Firdausi duk sunzo sun taka rawar gani, hakama abokansa su Abbati na ƙauyensu, inda ɗunbin jama'a sukai masa alkairi da dama wanda shi wasuma bai sansuba.
        Amaryar jego tasha gayu harta gaji, koni dai ta gama burgeni aradu🤗, balle kuma ubangayya Jay. Ansha hotuna inda naita hango fans cikin ƴan taron suna🤗. (Kunyima Jay halacci gaskiya😘😘😍🤣, dan yau Ƴan Team Beejay da team Qaseem da team Shahudah duk sun dunƙule waje ɗaya😋☺😉💃🏻.

★★★★★
Chapter 167 · 0% Book details