← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 168

Sashe 68

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

ashe.
        A bazata sukaji Ƙaura yace, “Yarinya yaya sunanki?”. Duk juyowa sukai su duka suna kallonsa dason ganin dawa yake tsakanin bily da Rose?. Sai sukaga da Bilkisu yake dan itace gab dashi kuma itace ta gaidashi tunda sai yanzu ta ganshi, gashi ta kafeshi da idanu tamkar maison tuna inda ta sanshi. Tambayar da yaymatane yasata dawowa hayyacinta, tace, “Bilkisu”. “Balqeesa! mai gadon zinari kenan” baba ƙaura ya faɗa yana wani murmushi tamkar yanda yay ɗazun akan Jay. Jawaad zaiyi magana L. General ya riƙe masa hannu yana girgiza kai alamar kar yace komai. Komawa yay ya tsaya badan yasoba danshi al'amarin tsohon ya fara bashi haushi. Sarai ƙaura yaga abinda Jawaad yayi, danta wutsiyar ido yake kallon duk miotsinsa, amma sai yay kamar hankalinsa akan Bilkisun kawai yake. Har Lieut.. General ya basu Umarnin shiga Jirgin Ƙaura ya sake jefama Bily tambaya. “Balqeesa! yaya sunan mahaifinki?”.  Yanzunkam ba Jawaad kaɗaiba kowama abin yazo masa wuya banda Rose, ahaka zasuyi tafiyar da wannan mutumin mai shegen tambaya da bin ƙwaƙwƙwafin mutum?. A miskile Bilkisu ta amsa masa da “Adam makaho”. Duk ido suka zubama Ƙaura suji mizaice, amma sai ya ɗauke kansama gaba ɗaya kamar bashi yay tambayar aka bama amsa ba.
    Ganin yanda yay ɗin yasa L.. General cemusu su shiga. Haka duk suka fara shiga suna ƙunƙuni da hararar baba ƙaura daketa murmushin da basusan inda ya dosaba. Jay ya matsa ya kama hannun Bily dake tsaye tamkar wadda aka tsayar, ajiyar zuciya ta sauke dan tayi nisane a tuno mafarkinta na daren jiya wanda ayanzu ta tuna acan taga fuska wannan tsohon. Baba Ƙaura dake biye da bayansu ya ƙure hanunsu dake cikin na juna da ido yana murmushinsa har yanzu, sai da suka taka ƙafarsu zasu hau jirgin yace, “Sara da sassaƙa baya hana gamji tohowa”. Daga Jawaad har Bilkisu sunji furucin baba ƙaura sarai, harma Jay ya juyo zaiyi magana sai kuma ya fasa.
       “Karka damu yaro faɗi duk abinda ke ranka, nima nawa nake faɗa dan bana bari a ciki ta kasheni. Ƙwai cikin ƙaya na gani ajiyar ALLAH”. Karan farko da kalaman tsohon suka saka gaban Jawaad faɗuwa, kalmar Ƙwai cikin ƙaya idan bai mantaba ya taɓa jinta a cikin mafarkinsa mai Sarauniyar da har yau basan inda ya dosaba. Har suka zauna idonsa bai daina kallon baba ƙaura ba da yay biris da kowa tamkar bashi ya gama takale-takalen maganaba yanzun.
         Gaba ɗayansu duk da addu'a a bakinsu har jirgin ya ɗaga sararin subahana.

      Duk da wannan shine karona na farko a hawa jirgi abin mamaki babu wani tsoro ko ƙauyanci tattare dani, kodan helicopter ne oho, nasan dai lokacin da zamuyi sama na riƙo hanun wanda bansan wanene ba sai da muka dai-daita na fahimci Rose ce, aiko tacika tayi fam da haushi, har nai mamaki da bata turo hannunaba, sai daga baya na fahimci Boss dake facing ɗinmu ne yaymata shamaki da hakan dan duk abinda zamuyi zai iya gani.
         Haka mukai ninƙaya a tafiya idanuna sun gaza daina kallon tsoho mai kayan fatu, har jirginmu ya samu sauka. Jejine maiban mamaki da al'ajabi, bakajin komai sai kukan tsuntsaye da mabanbanta sauti da zuciya bazata iya hasaso minene ba. Kowa kagani hankalinsa a tashe yake da wannan jeji amma banda tsohon nan. Haka muka firfito kowa na karanta addu'ar da tazo masa a baki, wani irin makeken ruwane kwance ƙar-ƙar har haskensa na ɗaukar idanu a gabanmu, Oga Aliyu yace, “Ikon ALLAH, amma a taswurar jejin nan bamuga wannan ruwanba sam, ko masu zanen taswirar basu san da shi bane?”. “Wlhy Aliyu wannan shine abinda nake ayyanawa a raina yanzun” Jabeer ya faɗa murya a harɗe.
           Tsohon nan ya bimu da kallo ɗaya bayan ɗaya sai kuma ya girgiza kansa da faɗin, “Wannan ruwa zuwayyene ba zaunanne ba”. “Kamar ya?”. Suka kusan haɗa baki wajen tambaya.
     Ƙin basu amsa yay, saima kallonsa daya maido gareni, “Ɗiyata Balqeesa bismillah saka ƙafarki a ruwannan” sosai naji gabana ya faɗi, idanuna suka cika da ƙwalla, ganin babu wanda yay magana a cikinsu yasa na ɗaga ƙafa zan nufi ruwan. Caraf aka riƙomin hannu, basai na juyaba ƙamshinsa kawai ya bani amsar shine, murya a kausashe yace, “Baba ya zaka turata shiga wannan ruwan maikama

da ruwan tsafi?”. Mu duka kallonsa mukai, Jawaad da shima maganar ta suɓuce masane kawai babu shiri yay saurin dafe kai da faɗin, “Sorry, ina nufin ruwan daga gani yanada ban al'ajab, tunda nake ban taɓa ganin ruwa mai ƙyawunsa ba da ɗaukar ido irin haka”. Murmushi mai sauti mukaga Baba ƙaura yayi, cikin ɗauke kai daga garemu yace, “Dole saimun ƙetarashi zamu kai inda muke hari, anmana katanga da shine domin mu juya, kuma wlhy kunji na rantse wannan yarinyar kaɗaice zata ƙetarashi kafin mu sami hanya, dan tanada taurari masu ƙarfin gaske”. A take duk suka zubamin ido, ni kaina wata irin jarumta nakeji da dakiyar zuciya da bansan yaushe na sameta ba. Hafiz yace, “Kana nufin har kai da akai iƙirarin kasan ciki da bai ɗin jejin?”. “Yaro, baiwa kowa da irin tasa, wani har yabar duniya babu mai fahimtar tasa, wani ko harmutsin duniya ke bayyana tasa, waniko nasarorinsane, wani ko hatsabibancinsa ne, wannan idanun da kake gani ALLAH kaɗai yasan ajiyar da yay a cikinsu”.
       Kai kawai duk muka shiga jinjina masa, boss yace, “Inhar zata ƙetara ruwannan sai dai tare dani”. Murmushi baba ƙaura yay kawai ya nuna mana hanya.
   Sai da mukaje gab da ruwan yace, “ku tabbatar a tare ƙafafunku suka sauka, kuma da bismillah”. Umarninsa mukabi mukai yanda yace, ni dai harda ƙarama wata addu'ar nayi, wani irin azabar sanyi ne mai keta fata da tsoka ya shiga cikin jijiyoyi ya gauraye da jini ne ya riskemu lokacin da ƙafafunmu dake cikin takalma suka sauka cikin ruwan, atake muka fara rawar ɗari dagani har boss, maimakon muyi ƙoƙarin komawa baya sai naji ya fisgi hannuna mun sake saka ƙafafunmu na haggu suma, abin mamaki sai gamu mun jiƙe da zufa sharkaf dalilin zafin daya riskemu kuma a yanzu tamkar ana tafasamu a garwashi, zafin bashida maraba da wani zafi dana taɓaji kwanakin baya da bazan tuna dalilin jinsa ba. Sake fusgata Boss yay muka cigaba da tafiya dukda azabar dake ratsa jikkunanmu. Wani irin mahaukacin ihu ne mai ƙarfin gaske ta karaɗe jejin, gaba ɗaya ruwan da muke tsakkiya ya koma jini, da farko na tsorata, amma addu'ar da naji Boss ya kamo yanayi tuni nima na karɓa masa ina mamuƙeshi. Ɗaf ruwan ya ɗauke lokaci ɗaya tare da kukan, sai ƙarar iskar guguwa mai ƙarfin gaske da mukeji tana tinkaromu, a take muka daina ganin komai saboda guguwar tai mana ruf. Wata muguwar shaƙa naji anmin a wuya, nai ƙoƙarin fincike hannuna cikin na boss danna ƙwaci kaina amma hakan ya gagara, ashe shima shaƙesan akai,  da hannuna na haggu na shiga laluben abinda ya shaƙenin, dan idona a rufe yake saboda guguwar data lulluɓemu. Ɗumbin mamaki ya kamani jin jikin mutumne da gaske, jikin da ya taɓa riskata a cikin wasu darare da sam na mantasu a cikin ƙwaƙwalwata, cikin amincin UBANGIJI Hannuna ya sauka a nasa wuyan shima, na damƙi sarƙar dake wuyan na fincika da masifar ƙarfin dana san daga UBANGIJINA ne kawai. A take jejin yay wata irin girgiza tare da wasu irin gigitattun ƙararraki ta mabanbanta muryoyi. Daga haka ban sake sanin mike faruwa ba.

           Yanda aka shaƙe bilkisu haka shima Jawaad aka shaƙesa, sai dai shi saɓanin itane, maimakon ya samu nasarar fisgar sarƙar wuya sai yasamu nasarar ciran wani abu dake hanun wanda ya shaƙesan, danshi hanunsa yay ƙoƙarin cirewa daga wuyansa da aka shaƙe.
      Da sauri yay azamar taro Bilkisu jikinsa ya rungumeta da ƙyau yana cigaba da karanto addu'a, isakar data lulluɓesu ta fara washewa a hankali har suka bayyana filin subahana, babu wancan ruwan da suka riska a farko, hasalima wajen tsaunine.
        Su Hafiz da suka samu kariyar UBANGIJI daga wannan guguwa da basusan daga ina ta ɓulloba duk suka miƙe daga rumfar da Baba ƙaura yay musu da jikinsa. Dan ranƙwafe yake kansu ya baza hannayensa tamkar maison tattaro wani abu.
      Gaba ɗayansu kansu Jay dake durƙushe a ƙasa kan Bily bisa cinyarsa yana girgizata sukai, baba ƙaura yay murmushi yana mai ɗaga hannayensa sama da zuba kirari wa UBANGIJIN AL'ARSHI, idanunsa na zubda hawaye, sai yanzune ya fahimci ƙaddarar zamansa cikin gari na tsahon shekara biyu bayan halaka masa iyalinsa da akai, UBANGIJI mai hikima, UBANGIJI mai rahama, sarkin da baya
Chapter 68 · 0% Book details