Sashe 33
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
................Zagayen gidan gonar suka farayi suna hira mai daɗi da mutunta juna, sashen dabbobin da ake kiwo da sashen da ake noma, sashen kaji, kifi, su talo-talo, zabi, agwagi, kajin gida, zomaye, harda tantabaru, sai sashen itatuwan fruits, komai yana tafiya yanda yake buƙata, sun nufi inda Jawaad ya gyara shima suke fidda yankakkun kaji dasu zabbi da sauran duk nau'in ƙananun dabbobin da ake kiwo a wajen ana packaging nasu a ledoji a shiryasu a wasu robobi manya masu haske domin masu sari dake kaiwa birni, hakama ƙwan kaji da zabi dana talo-talo, sai inda ake tace tsaftatacciyar madarar shanu kuma ana sakawa a galoli shima, kowacce galon da adadin litar da take ci, da inda ake shirya dukkanin nau'in kayan itatuwa suma. Abin dai dolene ya burge mai kallo da ƙayatarwa sosai. Sai da suka shiga lungu da saƙo, ya kuma gamsuwa da yanda komai ke tafiya, yana ta ma ma'aikatan jinjina da sake basu ƙwarin gwiwa, inda yaga kuskure kuwa cikin hikima yake musu gyara ba yanda zasu fahimci gazawarsu ba, yanda yake tafiyar da al'amarinsu na ƙara masa girma a idonsu sosai da daraja. Bayan sun kammala zagayawa suka yada zango ƙarƙashin bukkar bunu da tasha gyara domin hutawa, gefenta kuma anyi ɗan gini mai 2 bedroom kawai, domin idan yazo da shirin kwana nan yake kwana ko gidan baba maigari, hirarsu suka cigaba dayi cikin nishaɗi, lokaci-lokaci Jay yakan amsa waya, wadda ta shafi aiki kuwa yakan tashi ya koma gefe idan ya gama ya dawo. Da rana sai ga abinci lafiyayye daga gidan baba maigari an aiko musu, harda fura mai ƙyau da tasha damu. Yini guda anan suka yisa, Jawaad yaji matsalolin jama'ar garinsa waɗanda zai iya kawo gyara da iya ƙarfin aljihunsa yace zaiyi, dan dama ya daɗe bai zoba kusan wata uku. wanda sukafi ƙarfinsa kuma zasu haɗa hannu domin neman taimakon wanda zai iya musu, Jawaad ya gaji mahaifinsa a abubuwa da dama, komai nashi na al'ummane, dukiyar da mahaifinsa ya bari bata rufe masa ido ya zama asharari ba, sai ya ɗora kyawawan aiyukansa akan wanda mahaifinsa ya fara, tare da nasa da ya ƙirƙira shima, yanda yake rayuwarsa a sauƙaƙe bazaka taɓa tunanin an tara masa irin wannan dukiyarba, dan ko iya gidan gonarnan ai al'amarine babba, balle kuma akwai wanima bayan wannan, bayan sauran abubuwa da shima nasa ƙoƙarin.
Bayan sunbar gidan gona gidan baba mai-gari suka koma, sun samu zama dashi da manyan gari suka tattauna akan maganar da sukai a gidan gona na abokansa, sai bayan sallar magriba Jawaad ya baro ƙauyen cike da tsaraba daga jama'a, duk da sunsan yanadashi hakan baisa suji ƙyashin ƙyautata masa da ni'imar da suma ALLAH yay musu ba. A hanya ya tsaya yay sallar isha'i kafin ya ƙarisa gidan Umma ƙarama. Tayi murnar ganinsa ita da yaranta, ya sauke mata tsarabarta anan da ɗibar mata wadda mutane suka bashi yay mata sallama ya tafi dan bai jimaba sosai, daga nan sai gidan Ummah babba, gidansu Nabeelah kenan, nanma sunyi murnar ganinsa, inda suka fara faɗansu shi da Batool kamar yanda suka saba, itama dai tsarabar ya ajiye musu ya tafi, a gida ya yada zango, kasancewar kowa ya shige sashensa shima nashi ya shige akan da safe zai fiddama kowa nasa kason, sauran ya kaima kakansa nasa shima, sai nasu Hafiz.
WASHE GARI LAHADI.
Washe gari lahadi, na tashi da burin abubuwa da dama, dan da daddare na samu Dad da yah Qassem ya kirashi, na faɗa masa zanje na gaida Inna zainabu yace naje sai driver ya kaini, na sanar masa zanhau napep saboda zan fara zuwa wajen aiki da aka sakani kafin naje canɗin idan na fito wajen saloon. Ina kammala gyaran ɗaki nai wanka, na fita nai breakfast sama-sama na koma ɗaki nai shiri. Doguwa
r rigace na saka ta Material baƙa da ratsin fari, ta zaunamin ɗas a jiki, gashi ta buɗe daga ƙasa bata wani matseniba sai a ƙirji kamar yanda tsarin ɗinkin yake, maɗaurin da akai mata na kama na ɗaure a bayana, sai ta kuma fita da ƙyau. Gashina dake a tsefe na kuma gyarama zaman ribbon, sanan na saka farar hula mai ƙyau, na kawo ƙaramin gyale baƙi na yana a kaina, tare da kalmashesa a ƙirjina ya rufe ruf na ɗora a kafaɗa ƙasanshi suka sauka bayana, basai an faɗaminba, ni kaina nasan nayi ƙyau, hakan yasa naita kallon kaina a mirror ina murmushi, a gurguje na ƙarasa kimtsawa na fito sagale da ƴar jikkata a kafaɗa ina ƙamshi mai sanyi, sai takalma masu ɗan tudu kaɗan, na riga na faɗama Mom zan fita dama tun da daddare, hakan yasa yanzu nai ficewata kaina tsaye tunda babu wanda ya tashi har Yah Qaseem da baisan zan fitaba, dan banfaɗa masabama gudun matsala.
Da ƙafa na taka har titi na tari napep na hau zuwa inda Oga Jabeer ya bani.
Bayan fitar Bilkisu daga gidan Mom ta fito daga ɗakinta, tanason tayi magana da Shahudah ne, shiyyasa tun ɗazun taketa dakon fitar bily, tana tsoron halin da Shahudah zata iya shiga da har bily zata sani, dan a ganinta bily ita kaɗaice bare a cikinsu da bai kamata tasan sirrinsu ba. Sam jiya batai barciba akan bayanin da Shahudah tai musu na zuwa ɓangaren Jawaad da tayi, ta fahimci sunyi kuskuren ƙin sanarma Shahudah gaskiyar lamari akan sakinta da Jawaad yayi tun lokacin da wancan al'amarin ya faru, ba damuwarta abinda Shahudah ta aikataba, damuwarta kar Jawaad ya sake gudun Shahudah akan hakan, dan ita kanta inhar zata faɗi gaskiya bata taɓa kama Jawaad da abun rashin gaskiya ba dangane da fasiƙanci, dan ko lokacin da basa ƙasar ma idan yaje musu hutu duk jarabar Shahudah da naci akan yazo suje club baya zuwa, ita kanta ma faɗa yake mata, shiyyasa da yaje take kame kanta. To tasan akan hakan Jawaad zai iya sake bijire musu ne dangane da maida Shahudah.
Tashin Shahudah kenan a barci tayo brush da alwala ta fito mom ta shigo, ƙarfe goma saura sai yanzune wai ake alwalar sallar asuba😭🤦🏻.
“Mom lafiya?” Shahudah dake ƙoƙarin saka gyale ta faɗa tana kallon mom. Mom ta zauna bakin gado tana faɗin, “Magana nazo muyi”. Zama Shahudah tai ta fasa sallan, Mom tace ba salla zakiyiba ne?” “Eh salla zanyi, amma muyi magana sai nayi daga baya”. “Karki damu tashi kiyi sallar zan jiraki”. Shahudah batace komaiba ta miƙe ta kabbara salla, wadda ALLAH kaɗai yasan mima take karantawa, dan a mintuna ƙalilan ta idar da kayarta ta dawo wajen mom dake zaune tai tagumi da juya abinda zai iya biyo baya a ranta. Motsin Shahudah ne ya maidota hayyacinta ta gyara zama, tare da kamo hannayen Shahudah duka cikin nata ta kafeta da idanu, “Shahudah magana zanyi miki, inason ki nutsu ki fahimta, domin muma a yanzu haka hanyar gyara ɓarnar da kikayi muke, munada tabbacin samun nasara kuma, abinda yasa muka yanke hukunci sanar mikin a yanzu dukda mun ɓoye a baya saboda gudun halin da zaki shiga, yanzu kam saboda karki sake ƙara tafka irin kuskuren da kikayi ranar na zuwa wajen Jawaad”.
“Mom ni dan ALLAH kimin magana kai tsaye, ki daina yimin wannan manya-manyan hausan naki da ba wani fahimtarsu nakeba, minene ya faru”. Yanda tai maganar da kumbura bakin shagwaɓa yasa mon yin ƴar dariya tana shafar kumatunta, “Nifa daɗina dake taɓara maman Dadynta, karki damu ai zan kaiki, kumani sonake ki iya hausar ai tunda yaren mamanki ce”. Shahudah batace komaiba sai ɓata fuska data sake yi. Mom ta ɗauka takardan data shigo dashi ta miƙama Shahudah. Babu musu Shahudah ta amsa tabuɗe takardan batare da tace komaiba.
Kasancewar Jawaad da turanci ya rubutama Shahudah takardan saki sai ta fahimci komai dallah-dallah. Hannunta na rawa da bakinta ta ɗaga takardar, “Mom kina nufin BB ne ya aiko min da wanan dan naje wajensa?”.
Kai Mom ta girgiza mata, “Badan kinje wajensa bane, wannan takardar shekararta biyar kenan a gidannan, mune dai bamu bakiba tun lokacin da akai rikicin zubar da cikin nan, munƙi bakine saboda gudun karki sake shiga wani hali akan wanda kika tsinci kanki a wancan lokacin, dan muna
Bayan sunbar gidan gona gidan baba mai-gari suka koma, sun samu zama dashi da manyan gari suka tattauna akan maganar da sukai a gidan gona na abokansa, sai bayan sallar magriba Jawaad ya baro ƙauyen cike da tsaraba daga jama'a, duk da sunsan yanadashi hakan baisa suji ƙyashin ƙyautata masa da ni'imar da suma ALLAH yay musu ba. A hanya ya tsaya yay sallar isha'i kafin ya ƙarisa gidan Umma ƙarama. Tayi murnar ganinsa ita da yaranta, ya sauke mata tsarabarta anan da ɗibar mata wadda mutane suka bashi yay mata sallama ya tafi dan bai jimaba sosai, daga nan sai gidan Ummah babba, gidansu Nabeelah kenan, nanma sunyi murnar ganinsa, inda suka fara faɗansu shi da Batool kamar yanda suka saba, itama dai tsarabar ya ajiye musu ya tafi, a gida ya yada zango, kasancewar kowa ya shige sashensa shima nashi ya shige akan da safe zai fiddama kowa nasa kason, sauran ya kaima kakansa nasa shima, sai nasu Hafiz.
WASHE GARI LAHADI.
Washe gari lahadi, na tashi da burin abubuwa da dama, dan da daddare na samu Dad da yah Qassem ya kirashi, na faɗa masa zanje na gaida Inna zainabu yace naje sai driver ya kaini, na sanar masa zanhau napep saboda zan fara zuwa wajen aiki da aka sakani kafin naje canɗin idan na fito wajen saloon. Ina kammala gyaran ɗaki nai wanka, na fita nai breakfast sama-sama na koma ɗaki nai shiri. Doguwa
r rigace na saka ta Material baƙa da ratsin fari, ta zaunamin ɗas a jiki, gashi ta buɗe daga ƙasa bata wani matseniba sai a ƙirji kamar yanda tsarin ɗinkin yake, maɗaurin da akai mata na kama na ɗaure a bayana, sai ta kuma fita da ƙyau. Gashina dake a tsefe na kuma gyarama zaman ribbon, sanan na saka farar hula mai ƙyau, na kawo ƙaramin gyale baƙi na yana a kaina, tare da kalmashesa a ƙirjina ya rufe ruf na ɗora a kafaɗa ƙasanshi suka sauka bayana, basai an faɗaminba, ni kaina nasan nayi ƙyau, hakan yasa naita kallon kaina a mirror ina murmushi, a gurguje na ƙarasa kimtsawa na fito sagale da ƴar jikkata a kafaɗa ina ƙamshi mai sanyi, sai takalma masu ɗan tudu kaɗan, na riga na faɗama Mom zan fita dama tun da daddare, hakan yasa yanzu nai ficewata kaina tsaye tunda babu wanda ya tashi har Yah Qaseem da baisan zan fitaba, dan banfaɗa masabama gudun matsala.
Da ƙafa na taka har titi na tari napep na hau zuwa inda Oga Jabeer ya bani.
Bayan fitar Bilkisu daga gidan Mom ta fito daga ɗakinta, tanason tayi magana da Shahudah ne, shiyyasa tun ɗazun taketa dakon fitar bily, tana tsoron halin da Shahudah zata iya shiga da har bily zata sani, dan a ganinta bily ita kaɗaice bare a cikinsu da bai kamata tasan sirrinsu ba. Sam jiya batai barciba akan bayanin da Shahudah tai musu na zuwa ɓangaren Jawaad da tayi, ta fahimci sunyi kuskuren ƙin sanarma Shahudah gaskiyar lamari akan sakinta da Jawaad yayi tun lokacin da wancan al'amarin ya faru, ba damuwarta abinda Shahudah ta aikataba, damuwarta kar Jawaad ya sake gudun Shahudah akan hakan, dan ita kanta inhar zata faɗi gaskiya bata taɓa kama Jawaad da abun rashin gaskiya ba dangane da fasiƙanci, dan ko lokacin da basa ƙasar ma idan yaje musu hutu duk jarabar Shahudah da naci akan yazo suje club baya zuwa, ita kanta ma faɗa yake mata, shiyyasa da yaje take kame kanta. To tasan akan hakan Jawaad zai iya sake bijire musu ne dangane da maida Shahudah.
Tashin Shahudah kenan a barci tayo brush da alwala ta fito mom ta shigo, ƙarfe goma saura sai yanzune wai ake alwalar sallar asuba😭🤦🏻.
“Mom lafiya?” Shahudah dake ƙoƙarin saka gyale ta faɗa tana kallon mom. Mom ta zauna bakin gado tana faɗin, “Magana nazo muyi”. Zama Shahudah tai ta fasa sallan, Mom tace ba salla zakiyiba ne?” “Eh salla zanyi, amma muyi magana sai nayi daga baya”. “Karki damu tashi kiyi sallar zan jiraki”. Shahudah batace komaiba ta miƙe ta kabbara salla, wadda ALLAH kaɗai yasan mima take karantawa, dan a mintuna ƙalilan ta idar da kayarta ta dawo wajen mom dake zaune tai tagumi da juya abinda zai iya biyo baya a ranta. Motsin Shahudah ne ya maidota hayyacinta ta gyara zama, tare da kamo hannayen Shahudah duka cikin nata ta kafeta da idanu, “Shahudah magana zanyi miki, inason ki nutsu ki fahimta, domin muma a yanzu haka hanyar gyara ɓarnar da kikayi muke, munada tabbacin samun nasara kuma, abinda yasa muka yanke hukunci sanar mikin a yanzu dukda mun ɓoye a baya saboda gudun halin da zaki shiga, yanzu kam saboda karki sake ƙara tafka irin kuskuren da kikayi ranar na zuwa wajen Jawaad”.
“Mom ni dan ALLAH kimin magana kai tsaye, ki daina yimin wannan manya-manyan hausan naki da ba wani fahimtarsu nakeba, minene ya faru”. Yanda tai maganar da kumbura bakin shagwaɓa yasa mon yin ƴar dariya tana shafar kumatunta, “Nifa daɗina dake taɓara maman Dadynta, karki damu ai zan kaiki, kumani sonake ki iya hausar ai tunda yaren mamanki ce”. Shahudah batace komaiba sai ɓata fuska data sake yi. Mom ta ɗauka takardan data shigo dashi ta miƙama Shahudah. Babu musu Shahudah ta amsa tabuɗe takardan batare da tace komaiba.
Kasancewar Jawaad da turanci ya rubutama Shahudah takardan saki sai ta fahimci komai dallah-dallah. Hannunta na rawa da bakinta ta ɗaga takardar, “Mom kina nufin BB ne ya aiko min da wanan dan naje wajensa?”.
Kai Mom ta girgiza mata, “Badan kinje wajensa bane, wannan takardar shekararta biyar kenan a gidannan, mune dai bamu bakiba tun lokacin da akai rikicin zubar da cikin nan, munƙi bakine saboda gudun karki sake shiga wani hali akan wanda kika tsinci kanki a wancan lokacin, dan muna