← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 96 OF 168

Sashe 96

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

abinda ke faruwar tukunna, dan kinga al'amarin yazo da ruɗani a ciki”. Shiru Ummah tai na wasu sakanni, cikin sauke ajiyar zuciya tace, “Hakane kuma Jawaad, rashin faɗa matan yanzu yanada amfani, dan ko ƴan gidanku karmu bari su sani yanzun sai mun gama sanin komai mu kanmu”. Jay yace, “Insha ALLAHU Ummah bazasu sani ba”.
       Baibar gidan Ummah ba sai kusan ƙarfe uku na rana. Daga nan gida Ummah ƙarama yaje itama, itakam harma tafi Ummah Babba shiga ruɗani, saboda ita mutumce mai ƙarancin juriya akan farin ciki ko ɓacin rai, duk wanda ta tsinci kanta a ciki saika ganesa tattare da ita. itama dai ya jima anan suna tattaunawa, dan saida akai sallar la'asar sannan ya baro gidan.
           Gida ya nufa dan a gajiye yake ga barci yanaji sosai cikin idanunsa. Dai-dai traffic light ta tsayar dashi idonsa ya hango masa ɓaleru cikin mota, wanda ke a bayan motar ya kalla ya ɗauke kansa, sai kuma yay saurin sake kallon motar. Abinda ya faɗo masa a raine ya sakashi saurin ɗaukar wayarsa ya shiga WhatsApp, saƙon gimba da har yanzu yana nan ya kunna, ya maimaita dai-dai inda gimba yake sanar masa sunan Alh...Alh..k......
         Ganin an basu hanya ya harba motar gaba hankalinsa nakan motar su ɓalerun, gefen titi ya gangara yabi motar da kallo harta ɓacema ganinsa, a fili ya furta ‘Tabbas Alhaji Kokino Gimba kake nufi’ yay maganar da ɗan dukan sitiyarin motar yana cije lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi, kafin ya furzar da huci mai ƙarfi ya kife kansa a sitiyarin na kusan tsahon mintuna bakwai. Tabbas inhar tunaninsa nakan dai-dai matarnan ce, to minene alaƙarta da Gimba?. Bashi da mai bashi amsa, dan haka wayarsa ya ɗauka yay kira, bugu biyu kuwa aka ɗaga daga can cike da girmamawa. Bai tsaya sauraren gaisuwarba yace, “Hameed kana tare da ɓaleru ne yanzu haka?”. Daga can aka amsa masa da, “Yes Sir, ai da naga ma irin sabuwar motarka a traffic yanzu har na ɗauka kaine”. “Kaga manta da wannan, wa yake ja a motar?”. “Alhaji Sadi Kokino ne sir” “Ka tabbata shine?”. “Wlhy shine Sir”. Shiru Jay yayi yana murza goshinsa, ya sauke zazzafan numfashi da faɗin, “Amma kacemin Drivern Mr Gebrail ne ai?”. “Wlhy Sir tunda na fara aikin nan tare da shi nake ganinsa, ni kaina yau da naga ya ɗauki Alhaji Kokinon nasha mamaki, shiyyasa ban gazaba wajen bibiyarsu”. Sitiyari Jay ya sake daka da ƙarfi, “Hameed akwai matsala, kodai sun shirya bada ƙafane dama dankar a bibiyesu, kokuma sunada tabbacin akwai mai bibiyarsu, yanzu haka suna ina?”. “To Sir nikam ka sakani a ruɗani, amma gamu a anguwar Sanni zasu shiga wani gida mai farin gate”. “Maza kabar wajennan Hameed, kuma duk abinda ka gani bai makaba ka tabbatar ka kirani, gobe idan ALLAH ya kaimu kazo ka sameni a A.Y street”. Cikin mamakin da babu damar tambaya Hameed yace, “Okey Sire”. Yanke wayar Jay yayi ya maida akalar kiran ga Jabeer, yana ɗagawa shima bai saurari tsokanar da yake masaba ta ango ango yace, “Jabeer kuna Office ne?”. “Eh muna Office, lafiya naji muryarka haka?”. “Jabeer inason yanzun nan ku bincikamin Number da Gimba yay wayar ƙarshe da ita a randa aka ɗaukesa, a ina mai ita yake yanzu haka? Sannan macece ko namiji?”. “Okey boss ina zuwa”. Yanke kiran Jawaad yayi ya tada motarsa yabar wajen, kansa tsaye tashar da ake hawan motar garin su Gimba ya nufa. Nesa da wajen yay fakin tare da kiran Dattijon nan a waya. Mintuna uku kuwa basu cikaba sai gashi. Motar ya buɗe masa ya shiga sannan ya maida ya rufe. Saida suka gaisa Jay yace, “Ka tabbatar yarinyarnan tana mana aikin da muke buƙata?” “Sosai kuwa Alhaji, ai itama kanta batasan aiki take manaba a kansa, yanzu haka ɗazun take sanarmin wai yau zasuje wani gidan dirama wani mawaƙi zaiyi wasa na musamman akan soyayyarsu da ɓalerun”. Murmushi Jay dake ɗan wasa da yatsun hannunsa saman sitiyari yayi, “Address ɗin wajen, sunan mawaƙin, time ɗin da zai shiga wajen da tashinsa?”. Dattijo yay ƴar dariya da faɗin, “Ai Alhaji kamar dama nasan zaka tambaya duk sai da na samo waɗanan amsoshin kaf, gasu a rubuce”. Amasar takardar Jay yayi yana jinjina kai, ya ciro kuɗi ya miƙa masa yana faɗin, “Ga cikon kuɗin aikinka nagode”. Baki a washe dattijo yac

e, “Nine da godiya ai Alhaji, ALLAH ya ƙara buɗi na alkairi, idan wani aikinma ya taso wlhy a kawo zanyi”. Jawaad baice komaiba sai murmushi kawai.
     Dattijo na fita kiran Jabeer na shigowa, ɗagawa yay yasa a kunne batare da yayi magana ba. Daga can Jabeer yace, “Tabbas Boss mace ce, sunan da tai register layin dashi shine Safara'u Hashimu, kakanta Bala, sunan mahaifiyarta Indo, kakaninta na wajen uwa Hassan da Baraka, shekarunta sittin da huɗu a duniya, asalinta ƴar garin Tsamiya ce, yanzu haka alama ta nuna ana amfani da layin a anguwar Habbun.........” Jay ya katsesa da faɗin, “Habbun kuma? Ba garin nan bafa kenan?”. “Kwarai hakane”. Baya Jay yay ya jingina da kujerar yana furzar da huci, kafin yace, “Hasashena ba dai-dai bane kenan?”. Daga can Jabeer yace, “Kai minene hasashen naka da?”. “Jabeer akwai wata mata lokacin case ɗin nan na Alhaji kokino mun haɗu da ita a gidansa idan baka mantaba itace ta taimakemu sosai har muka ɗauke mata yaro mai suna Yazeed, da ina zargin itace Gimba ke magana a gidan Alhajin nan da bai ƙarisa faɗaba”. “Tabbas Boss hasashenka ba kuskure bane, tun a wancan lokacin naso nace muku kodai Alhaji Kokino Gimba ke nufi, dan na taɓa ganinsa a ƙofar gidan farkon fara maka aiki lokacin bikinmu da Surayya, kasan matar Alhaji kokino ƙanwar maman tace, yanzu abinda za'ai shine kabani daga nan zuwa safiya insha ALLAHU zan bincika komai”. “Okey babu damuwa, shima yaron nan yau insha ALLAHU zan kamashi dan na kula akwai wani abu damu bamu saniba”. “A'a haba boss, ka bari wani a cikinmu ya kamashi mana, karka shigarma Mami lokacinta, amma mika hasaso mana”. “Da kaina zan kamashi Jabeer, dan akwai saƙon da nakeson bari a kamun nasa, abinda na hasaso kuma sai mun haɗu zamu tattauna”. Ya kashe ƙittt batare da ya jira amsar Jabeer ɗinba.
     Wayar Bilkisu ya kira, sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga dan bata kawo a ranta shi bane, ba Number data sani bace. Shiru tai taƙi magana, dan haka shi yay sallama. Yanda ta amsa sallamar ne yasashi fahimtar ta gane wanene yanzun, zamansa ya gyara da ƙoƙarin dai-daita muryarsa dake cike da ɓacin rai, “Am sorry kicema ƙawayenki suje kawai zan haɗu dasu zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, wani uziri yane ya riƙeni gaba ɗaya shiyyasa ban dawo ba”. Murya a sanyaye bily tace, “To zan faɗa musu, amma bakaci abinciba fa, haka kake yawo da yunwa?”. Idanun Jawaad ya lumshe yana murmushi, ji yay duk ɓacin ran da ya tarar masa a ƙirji yana guduwa, yace, “Karki damu da anyi magriba zan dawo isha ALLAH, jin muryarki kawai tasa nama ƙoshi, ke dai ki shirya amsar angonki kawai ƙanwar Jay.......” ƙittt ta yanke wayar daga can.
        Jawaad ya girgiza kansa yana murmushi har kumatunsa na loɓawa, motar ya tada yay gaba har lokacin murmushi ya gaza barin fuskarsa.

___________________________

             Tunda su Zuhrah suka wuce sai naji gidan duk babu daɗi, ga wani motse-motse da naketa famanji amma narasa takamaimai a ina nake jinsan, nai jarumtar dakewa dan bana son na ruɗar da kaina, sai kuma na koma ganin tamkar gittawar inuwoyi ta jikin Windows, da farko dai naso fita na leƙa waje, sai kuma wata zuciya ta gargaɗeni dayin hakan, yanda kaina ya farayin nauyine yasa na jawo wayata na kunna karatun Al-Qur'ani mai girma, a hankali nutsuwa ta fara saukarmin, naji kaina ya saki na koma normal, gidan kuma yay wani irin yin tsitt mai ban mamaki, babu motsin nan sam, ko ƙarar na'urorin dake aiki da wutar dake a kwai duk bakajin ƙararsu, ban ɗauki hakan komaiba na cigaba da zama a falon har aka fara kiraye-kirayen sallar magriba, Miƙewa nai da shirin sake wanka, dan ɗazun lokacin sallar azhar da zanyi salla ganin ɗingon jini yasa banyi ba, amma yanzu dana duba gab da su Ummie zasu wuce kuma ya sake ɗaukewa, dama nasan ɗazun nayi gaggawar yin wanka dan ƙa'idane sai bayan sallar azhar nake wanka ko la'asar duk da lokaci kan ɗan canja min wani watan.
       Wayar na ɗauka na shige bedroom, Kayan da zan saka na fara cirowa a drawer na ajiye, dan waɗan nan dazan cire ɗin jini yaɗan ɗiga a sket ɗin kaɗan sai yanzu na kula ma. Batare dana kashe karatunba nabar wayar a saman gado na cire
Chapter 96 · 0% Book details