Sashe 51
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Abinda ya farunne ya saka Dad yanke shawarar ɗaura auren Bily da Qaseem a wannan safiya ta juma'a dan kowa ya huta duk da basusan ainahin abindama ake bibiyar Bilkisu da shiba, ɗari bisa ɗari Mom ta bashi goyon baya. Ana idar da sallar asuba Dad ya nufi gidan Alhaji baba ya sanar masa halin da ake ciki tare da neman alfarmar haɗawa dana Shahudah da Jawaad, zuwa bayan salla idan ALLAH ya kaimu a cewar Dad sai ayi biki su tare. Alhaji baba bai musaba, dan yana fatan jikan nasa matsalarsa ta zama babu aure tazo ƙarshe. Daga gidan Alhaji baba gidansu Jawaad Dad ya wuce, a canma sun tattauna dasu Uncle Nasir kafin ai kiran Jawaad dake shirin tafiya Office.
Koda suka sanar masa shirinsu shima babu musu ya amsa musu, harma amincewar tasa da gaggawa ya basu ɗunbin mamaki, amma shi saiya fuske abinsa tamkar baiga mamakin nasuba sam ko bai fahimtaba, ya kuma fiddo kuɗin sadaki a take ya direma Uncle Nasir har dubu ɗari biyar. Kasa haƙuri kam sukai saida suka tanka akan hakan, batare daya kallesuba yace ai Alhaji baba ne ya kirasa ya sanar masa kafin su sukirashi, cikin gamsuwa da maganarsa Dad yace to ya rage kuɗin sunyi yawa, dubu ɗari sun isa. Murmushi Jay yayi yana wani susar ƙeya, kansa a ƙasa yace, “Karka damu Dad nariga na fidda kuɗin matsayin sadakin, Uncle kuje dasu wajen ɗaurin auren kawai please. Albarka suka saka masa tare da sallamarsa, yay musu sallama ya tafi fuskarsa ɗauke da wani shegen murmushi daya tsayama Uncle Nasir da Dad a ƙahon zukata. Dad ya dawo gida, yayinda Jay yanufi office ya nema alfarma tare da gayama Sir Ahmad abinda ake ciki. Sannan ya sanarma su Hafiz ma, sunyi matuƙar mamaki, amma ganinsa a wani yanayin da suka kasa yima fassara sai basuja zancen da nisaba suka shiga faɗama mutanensu nanan office da waɗanda suke kusa irinsu Abbati ta waya.
Maza nata haramar tafiya massallaci, inda daga canne za'a ɗauro auren bayan idar da sallar juma'a, yayinda ahalin gidansu Momy keta tururuwar zuwa gidan harma da tsiraru na ɓangarensu Dad kamar su inna Zainabu. Duk wannan abunda ke faruwa babu sanin bily, tanacan tanata barci abinta.
Massallaci ya cika tab da al'ummar musulmi yara da manya da matasa da tsoffi harma da mata dakanje sallar juma'a kasancewar wannan ranar ranace ta musamman a garemu, bayan an idar da sallar juma'a kamar yanda aka saba akai sanarwar ɗaure-ɗauren aure daza'ayi daban-daban wanda harda nasu Qaseem a ciki. Duk wanda yaga Qaseem a yau zai tabbatar yana cikin farin ciki, dan kuwa yaci ado da wata ɗanyar shadda fara ƙal da Dad ya bashi ya sanya, sai walƙiya da walwalin angwanci yakeyi kamar ka sacesa ka gudu, ga haƙoransa farare tas sun kasa rufuwa. Sai dai nayi iya dubana da waige-waige bangano ko mai kama da Jawaad ba balle shiɗin kansa, saisu Aliyu da suma duk suke sanye da shaddoji a yau, da alama dai gida suka koma bayan zancen ya riskesu suka canja shiri.
An fara ɗaura aure guda biyu da baida alaƙa dasu Dady, kafin a ɗaura wani da yaso bama kowa mamaki, wato dai Sabira da wani waishi Habib, ankuma roƙi Uncle Nasir dake kusa ya zama wakilinsu saboda wai wakilan amarya masu isoba har lokacin, wannan shine ya gogema mutane da yawa abinda ya taɓa musu zukata, ɗaurin aure na huɗu daya biyo baya shima bashi da alaƙa dasu Qaseem ɗin, saida akai kusan na mutum uku kafin a ɗaura na Qaseem da Azeema, jikin Qaseem har rawa yake ya miƙe zaiyi magana amma sai Uncle Uwaisu ya maida
shi ya zaunar yana mai sanar masa bafashi ake nufiba maybe wasune daban, ajiyar zuciya Qaseem ya sauke dukda dai hankalinsa bai kwantaba, gashi iya dubansa baimaga Dad a wajenba, bayan kuma tare dashi sukazo masallaci, ɗaurin aure na ƙarshe baki ɗaya shine ya tada hankalin dukkan mai alaƙa dashi, wato Jawaad Abdul-aziz da amaryarsa Bilkisu Adam, Alhaji Baba wakilin amarya Uncle Nasir da yay zaton da Shahudah ya kasance wakilin Ango, saida aka ambatanefa yaji wasan ya canja salo. Qaseem yama manta a ina suke, take yanke yaci kwalar imam da masa tambayar yaya haka ta faru?. Da ƙyar ƴan agaji suka ɓanɓare imam a hannun Yah Qaseem, cikin tsagwaron tashin hankali Dad da Qaseem ya gaza gani ɗazun a masallacin ya shiga jeroma imam tambayoyi shima. imam da duk bai fahimcesuba yace shifa a haka aka kawo masa sunayen anguna da amaren da za'a ɗaurama aure a yau, kuma iyakarsu kenan ya kammala gama takardar. Yay maganar yana nuna musu.
Ganinfa za'a iya bama hammata iska a massalacine ya saka ƴan agaji sallamar kowa akace su Dad su fito a shiga inda ya dace ayi magana, sannan ana neman dukkan angunan da aka ɗaura aurensu ba dai-dai ba.
Yah Qaseem kawai aka gani a cikin anguna, amma babu Jawaad babu Habibu da aka ɗaurama Shahudah, kuma kowa yayi imanin yaga Jawaad a massallaci kafin a tada sallah, yanzukam an nemesa ƙasa da sama tamkar allurar mayya an rasa. Kowa ƙoƙarinsa ya kira wayar Jawaad amma sam taƙi shigama, gefe kuma ana jajen wanene habib ɗin da aka ɗaurama aure da Shahudah?.
Lokacin da ake waccan dambarwar a lokacinne shikuma Salman ya kira Shahudah ya sanar mata komai, kafin ya kira Momy itama, yana tsaka da sanar mata abinda ke faruwa Shahudah ta nufi ɗakin Bilkisu da wuƙar data ɗakko daga kicin tsirara tana iƙirarin yaufa saita kasheta.
A masallaci komai ya hargitse, imam ya tara dukkanin ƴan agajin massallacin dake da alhakin rubuta sunayen waɗanan anguna da amare anata jera musu tambayoyi, dan kuwa dai Dad da kansa shine ya kawo list ɗin farko kuma an tabbatar yanada banbanci da wanda yake a hannun imam a yanzu. Sudai ƴan agajin dakeda wannan alhaki sun tabbatar abinda suka gani kenan, sannan kuma ga takardar farko da Dad ya kawo an samo kuma bata da alaƙa data yanzun. Abun ya ɗaurema kowa kai hatta da imam ɗin kansa, dan shidai yanada yaƙinin babu yanda za'ai ƴan agajin su bada abinda ba haka yakeba, dan invitations ake kawo musu na ma'auratan da duk za'a ɗaurama aure a satin, sukuma saisu rubuta sunayensu a takarda gabaki ɗaya domin samun sauƙi, nasu Jawaad kuma a rubuce Dad ya kawo tunda ba'a buga invitation card ba abin yazo a ƙure. TO A INA MATSALAR TAKE?.
Wannan itace tambayar dake a bakin kowa a wajen musamman lokacin da Yah Qaseem ya yanke jiki ya faɗi a sume shima. Dai-dai kuma da kiran da akaima Dad akan tashin hankalin dake faruwa a cikin gidansa. Abin tausayi sai kawai Dad ya fashe da kuka shima yana neman faɗuwar, cikin amincin ALLAH Uncle Sulaiman ya samu damar tarosa da faɗin, “Haba Alhaji Ali, ka kwantar da hankalinka mana, na tabbata saɓani aka samu ko kuskure, kuma abune mai sauƙi da nake ganin zamu warwaresa da gaggawa, Jawaad ya sakima Qaseem matarsa, haka shima wannan da bama asan ko wanenen ba ya sakema Jawaad matarsa”. Kasa magana Dad yayi, dan babu abinda yake fahimta daga kalaman Uncle Sulaiman, gaba ɗayama numfashinsa neman barin gangar jikinsa yakeyi.
Shugabannin massallacin dai nata ƙoƙarin binciken tushen wannan matsala da basu taɓa cin karo da itaba a tsahon rayuwarsu, anɗaura auren da babu adadi a shekarun wanzuwar massallacin amma hakan bai taɓa faruwaba koda da kuskure kuwa, babban tashin hankalinsu ma shine wanene Habib da aka ɗaurama Shahudah aure dashi?, dan kuwa dai an nema wakilan nasama an rasa balleshi kansa, matsalar Qaseem da Jawaad kam kowa yana ganin tanada mafita tunda su an rigada an sansu gasu kuma ƴan uwan juna.
Imam da kansa ya gama ɗaukar zafi gaba ɗaya ya cire rawanin kansa yana sharce gumi da faɗin, “Wannan wace irin matsalace haka? Tayaya za'ace an ɗaura auren da sam bashi da alaƙa da juna?”. Qaseem shi
ne mijin Bilkisu, an ɗaurama Jawaad, Shahudah itace matar Jawaad an bama Habib, Habib shine mijin Azeema, an bama Qaseem, Qaseem da Jawaad ahali ɗaya suka fito, a tare kuma aka kawo sunayensu, to yaya akai shi Habib mai mata azeema suka shiga cikin wannan sarƙaƙiyar? Idanma ance wajen haɗe sunayen waje ɗayane dan a sauƙaƙama liman wahala to tayaya abin ya kasance haka? Kenan suk yandama akai aka dawo akwai saka hanun hadiman masallacin kenan?. hakan bazai kasance mai yuwaba dan gashi dukkan bincike anyi babu wani baƙon al'amari daya shigo har aka bama imam ainahin takardar amare da angwayen wannan satin, wadda kuma kowane ɓangare suke nuna ba ita bace imam yay amfani da ita, kenan dukkan matsalar a yanzu tadawo ta tattarane gama shi imam ɗin dan kowa shi yake zargi.
★★★★★★
Ganin babu wata mafita anan Alhaji baba ya shawarcesu da tafiya gida kawai aje a samu nustuwa kafin a fuskanci matsalar cikin kwanciyar hankali a nema masalaha a kanta.
Kowa yay na'am da batun Alhaji baba, dan haka aka ɗunguma zuwa gidan Dad da tushen matsalar take.
Koda suka sanar masa shirinsu shima babu musu ya amsa musu, harma amincewar tasa da gaggawa ya basu ɗunbin mamaki, amma shi saiya fuske abinsa tamkar baiga mamakin nasuba sam ko bai fahimtaba, ya kuma fiddo kuɗin sadaki a take ya direma Uncle Nasir har dubu ɗari biyar. Kasa haƙuri kam sukai saida suka tanka akan hakan, batare daya kallesuba yace ai Alhaji baba ne ya kirasa ya sanar masa kafin su sukirashi, cikin gamsuwa da maganarsa Dad yace to ya rage kuɗin sunyi yawa, dubu ɗari sun isa. Murmushi Jay yayi yana wani susar ƙeya, kansa a ƙasa yace, “Karka damu Dad nariga na fidda kuɗin matsayin sadakin, Uncle kuje dasu wajen ɗaurin auren kawai please. Albarka suka saka masa tare da sallamarsa, yay musu sallama ya tafi fuskarsa ɗauke da wani shegen murmushi daya tsayama Uncle Nasir da Dad a ƙahon zukata. Dad ya dawo gida, yayinda Jay yanufi office ya nema alfarma tare da gayama Sir Ahmad abinda ake ciki. Sannan ya sanarma su Hafiz ma, sunyi matuƙar mamaki, amma ganinsa a wani yanayin da suka kasa yima fassara sai basuja zancen da nisaba suka shiga faɗama mutanensu nanan office da waɗanda suke kusa irinsu Abbati ta waya.
Maza nata haramar tafiya massallaci, inda daga canne za'a ɗauro auren bayan idar da sallar juma'a, yayinda ahalin gidansu Momy keta tururuwar zuwa gidan harma da tsiraru na ɓangarensu Dad kamar su inna Zainabu. Duk wannan abunda ke faruwa babu sanin bily, tanacan tanata barci abinta.
Massallaci ya cika tab da al'ummar musulmi yara da manya da matasa da tsoffi harma da mata dakanje sallar juma'a kasancewar wannan ranar ranace ta musamman a garemu, bayan an idar da sallar juma'a kamar yanda aka saba akai sanarwar ɗaure-ɗauren aure daza'ayi daban-daban wanda harda nasu Qaseem a ciki. Duk wanda yaga Qaseem a yau zai tabbatar yana cikin farin ciki, dan kuwa yaci ado da wata ɗanyar shadda fara ƙal da Dad ya bashi ya sanya, sai walƙiya da walwalin angwanci yakeyi kamar ka sacesa ka gudu, ga haƙoransa farare tas sun kasa rufuwa. Sai dai nayi iya dubana da waige-waige bangano ko mai kama da Jawaad ba balle shiɗin kansa, saisu Aliyu da suma duk suke sanye da shaddoji a yau, da alama dai gida suka koma bayan zancen ya riskesu suka canja shiri.
An fara ɗaura aure guda biyu da baida alaƙa dasu Dady, kafin a ɗaura wani da yaso bama kowa mamaki, wato dai Sabira da wani waishi Habib, ankuma roƙi Uncle Nasir dake kusa ya zama wakilinsu saboda wai wakilan amarya masu isoba har lokacin, wannan shine ya gogema mutane da yawa abinda ya taɓa musu zukata, ɗaurin aure na huɗu daya biyo baya shima bashi da alaƙa dasu Qaseem ɗin, saida akai kusan na mutum uku kafin a ɗaura na Qaseem da Azeema, jikin Qaseem har rawa yake ya miƙe zaiyi magana amma sai Uncle Uwaisu ya maida
shi ya zaunar yana mai sanar masa bafashi ake nufiba maybe wasune daban, ajiyar zuciya Qaseem ya sauke dukda dai hankalinsa bai kwantaba, gashi iya dubansa baimaga Dad a wajenba, bayan kuma tare dashi sukazo masallaci, ɗaurin aure na ƙarshe baki ɗaya shine ya tada hankalin dukkan mai alaƙa dashi, wato Jawaad Abdul-aziz da amaryarsa Bilkisu Adam, Alhaji Baba wakilin amarya Uncle Nasir da yay zaton da Shahudah ya kasance wakilin Ango, saida aka ambatanefa yaji wasan ya canja salo. Qaseem yama manta a ina suke, take yanke yaci kwalar imam da masa tambayar yaya haka ta faru?. Da ƙyar ƴan agaji suka ɓanɓare imam a hannun Yah Qaseem, cikin tsagwaron tashin hankali Dad da Qaseem ya gaza gani ɗazun a masallacin ya shiga jeroma imam tambayoyi shima. imam da duk bai fahimcesuba yace shifa a haka aka kawo masa sunayen anguna da amaren da za'a ɗaurama aure a yau, kuma iyakarsu kenan ya kammala gama takardar. Yay maganar yana nuna musu.
Ganinfa za'a iya bama hammata iska a massalacine ya saka ƴan agaji sallamar kowa akace su Dad su fito a shiga inda ya dace ayi magana, sannan ana neman dukkan angunan da aka ɗaura aurensu ba dai-dai ba.
Yah Qaseem kawai aka gani a cikin anguna, amma babu Jawaad babu Habibu da aka ɗaurama Shahudah, kuma kowa yayi imanin yaga Jawaad a massallaci kafin a tada sallah, yanzukam an nemesa ƙasa da sama tamkar allurar mayya an rasa. Kowa ƙoƙarinsa ya kira wayar Jawaad amma sam taƙi shigama, gefe kuma ana jajen wanene habib ɗin da aka ɗaurama aure da Shahudah?.
Lokacin da ake waccan dambarwar a lokacinne shikuma Salman ya kira Shahudah ya sanar mata komai, kafin ya kira Momy itama, yana tsaka da sanar mata abinda ke faruwa Shahudah ta nufi ɗakin Bilkisu da wuƙar data ɗakko daga kicin tsirara tana iƙirarin yaufa saita kasheta.
A masallaci komai ya hargitse, imam ya tara dukkanin ƴan agajin massallacin dake da alhakin rubuta sunayen waɗanan anguna da amare anata jera musu tambayoyi, dan kuwa dai Dad da kansa shine ya kawo list ɗin farko kuma an tabbatar yanada banbanci da wanda yake a hannun imam a yanzu. Sudai ƴan agajin dakeda wannan alhaki sun tabbatar abinda suka gani kenan, sannan kuma ga takardar farko da Dad ya kawo an samo kuma bata da alaƙa data yanzun. Abun ya ɗaurema kowa kai hatta da imam ɗin kansa, dan shidai yanada yaƙinin babu yanda za'ai ƴan agajin su bada abinda ba haka yakeba, dan invitations ake kawo musu na ma'auratan da duk za'a ɗaurama aure a satin, sukuma saisu rubuta sunayensu a takarda gabaki ɗaya domin samun sauƙi, nasu Jawaad kuma a rubuce Dad ya kawo tunda ba'a buga invitation card ba abin yazo a ƙure. TO A INA MATSALAR TAKE?.
Wannan itace tambayar dake a bakin kowa a wajen musamman lokacin da Yah Qaseem ya yanke jiki ya faɗi a sume shima. Dai-dai kuma da kiran da akaima Dad akan tashin hankalin dake faruwa a cikin gidansa. Abin tausayi sai kawai Dad ya fashe da kuka shima yana neman faɗuwar, cikin amincin ALLAH Uncle Sulaiman ya samu damar tarosa da faɗin, “Haba Alhaji Ali, ka kwantar da hankalinka mana, na tabbata saɓani aka samu ko kuskure, kuma abune mai sauƙi da nake ganin zamu warwaresa da gaggawa, Jawaad ya sakima Qaseem matarsa, haka shima wannan da bama asan ko wanenen ba ya sakema Jawaad matarsa”. Kasa magana Dad yayi, dan babu abinda yake fahimta daga kalaman Uncle Sulaiman, gaba ɗayama numfashinsa neman barin gangar jikinsa yakeyi.
Shugabannin massallacin dai nata ƙoƙarin binciken tushen wannan matsala da basu taɓa cin karo da itaba a tsahon rayuwarsu, anɗaura auren da babu adadi a shekarun wanzuwar massallacin amma hakan bai taɓa faruwaba koda da kuskure kuwa, babban tashin hankalinsu ma shine wanene Habib da aka ɗaurama Shahudah aure dashi?, dan kuwa dai an nema wakilan nasama an rasa balleshi kansa, matsalar Qaseem da Jawaad kam kowa yana ganin tanada mafita tunda su an rigada an sansu gasu kuma ƴan uwan juna.
Imam da kansa ya gama ɗaukar zafi gaba ɗaya ya cire rawanin kansa yana sharce gumi da faɗin, “Wannan wace irin matsalace haka? Tayaya za'ace an ɗaura auren da sam bashi da alaƙa da juna?”. Qaseem shi
ne mijin Bilkisu, an ɗaurama Jawaad, Shahudah itace matar Jawaad an bama Habib, Habib shine mijin Azeema, an bama Qaseem, Qaseem da Jawaad ahali ɗaya suka fito, a tare kuma aka kawo sunayensu, to yaya akai shi Habib mai mata azeema suka shiga cikin wannan sarƙaƙiyar? Idanma ance wajen haɗe sunayen waje ɗayane dan a sauƙaƙama liman wahala to tayaya abin ya kasance haka? Kenan suk yandama akai aka dawo akwai saka hanun hadiman masallacin kenan?. hakan bazai kasance mai yuwaba dan gashi dukkan bincike anyi babu wani baƙon al'amari daya shigo har aka bama imam ainahin takardar amare da angwayen wannan satin, wadda kuma kowane ɓangare suke nuna ba ita bace imam yay amfani da ita, kenan dukkan matsalar a yanzu tadawo ta tattarane gama shi imam ɗin dan kowa shi yake zargi.
★★★★★★
Ganin babu wata mafita anan Alhaji baba ya shawarcesu da tafiya gida kawai aje a samu nustuwa kafin a fuskanci matsalar cikin kwanciyar hankali a nema masalaha a kanta.
Kowa yay na'am da batun Alhaji baba, dan haka aka ɗunguma zuwa gidan Dad da tushen matsalar take.