← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 120 OF 168

Sashe 120

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Kiran sallar zuhur ne ya tashesu daga wannan zama, matan suka shige cikin gida sukuma mazan suka fita massallaci.
Bayan an idar suka dawo akaci abincin rana, Jawaad dai tsakura yay tayi yanzun ma, baici na kirki ba, hakama Bilkisu, Umm-Anum da take jinta sakayau yau tanata lura dasu sai dai batace komaiba har aka kammala aka tashi.
Takawa, Abbu, Abu-Siddiq suka fice masaukin su takawa dan su masa rakkiya yaje ya huta. Bilkisu kuma Umm-Anum ta tsareta ta kwanta barci, acewarta yanayin bily ya nuna barci takeji, kasa mata musu tayi ta kwanta, itako ta ɗaura kan bily saman cinyarta tana shafa mata kai har barcin mai nauyi kuwa yay awan gaba da Bilkisun, Anum dake ta tsegumi Umm-Anum tabar yayinta itama tazo ta raɓa bayan Bilkisun ta kwanta da yake a ɗakin Umm-Anum ɗinne. Ummu da Aunty Mahfuzah kuwa sun tafi can gidan aunty Mahfuzah ɗin suma.
Anuwar da Jawaad kuwa suna can sashen baƙi suma, Anuwar ya tsare Jay akan ya bashi labarin Abban su, sai shagwaɓa yake masa. Jawaad dake kwance cikin doguwar kujera yay murmushi idanunsa akan Anuwar dake zaune a ƙasan darduma jikin kujerar da yake a kwance hannunsu sarƙe dana juna. Cikin muryarsa dake a sanyaye yace, “Dear nima bansan Abba ba sosai, abubuwan da zan iya tunawa game da shi basu da yawa, dan banfi shekara bakwai ba ya rasu, sai dai kakanrmu mama maryam bata gusaba sai da ta maidamin tarihinsa tamkar karatu, dan sai da na haddacesa a cikin kaina tsaf, daga ni har kai da shi muke tsananin kama, musamman ma kai daka biyo har hasken sa, abubuwa ƙalilanne muka ɗakko Ummuna. Inada videos da dama da akayi lokacin da yake shugabancin ƙasarmu, ta hakane nakejin kamar na rayu da shi rayuwa mai tsaho...........”
Da sauri Anuwar ya ƙara ƙanƙame hannun Jawaad dake a cikin nashi yana faɗin, “Suna tare da kai yanzu?”. Murmushi Jawaad yayi ya kai hannu ya shafi kan Anuwar, “Da ganinka ɗan karan gaggawa ne da kai da rashin haƙuri yaron nan”. Yanda yay maganar da jan hancin Anuwar a ƙarshe ya saka Anuwar ɗin ƙyalƙyalewa da dariya, shima Jay murmushin sa ya sake faɗaɗawa yana maijin daɗin ganin Anuwar ɗin cikin nishaɗi. Wayarsa ya ɗauka ya lalubo folder da ta kasance duk hotunan Umm-Anum ne da Abban su sai shi. Miƙama Anuwar yay, jikinsa har ɓari yake wajen son amsar wayar abin tausayi, kallo ya shigayi yana hawaye sosai, hakan yasa Jawaad lumshe idonsa yana haɗiye abinda ya tarar masa a ƙirji na tausayinsu musamman ma Anuwar ɗin. Saurin buɗe idanu Jay yayi danjin yanda Anuwar ya fashe da kuka, ya kafesa da ido shima yana ƙoƙarin danne tasa zuciyar, “Haba my sweet Darling kamar ba namiji ba, kukan ya isa haka kaji lilly na”. Yay maganar da tashi zaune ya rungume Anuwar ɗin yana mai shafa masa baya, har saida yaji yayi shiru ya koma sauke ajiyar zuciya sannan ya barsa. Labarin ahalinsu da mahaifinsu ya cigaba da bashi cikin kulawa, wani gurin Anuwar yay kuka wani gurin yay dariya, haka suka kasance har akai kiran sallar la'asar, wanka Jawaad ya sakeyi da gaggawa suka fita massallaci.
Umm-Anum ma ta tada su Bilkisu sukayi tasu, bayan sun idarne ta saka mai aikinsu ta kawo abinci, zaunar da Bilkisu tayi tana faɗin, “Zauna na baki abincin nan da kaina, kwana biyu da zuwanku duk kun fara ramewa ke da mijin naki saboda rashin cin abinci, ina dalili”. Murmushi nayi cike dajin kunyarta, yanda take ƙoƙarin yin hausa sai abin keban dariya dan hausar kamar bata bahaushiya ba, wani wajenma kakarewa take ta kasa faɗa.
Duk yanda nakejin kunyarta haka na ringa amsar abincin da take bani da hannunta, sallamar su boss ta sakamu maida hankalinmu garesu, idanunsa a kaina dan haka nai azamar ɗauke nawa na maida ƙasa. “Kaima zo ka zauna” Umm-Anum ta faɗa idanunta akan Jawaad dake kallonsu cike da sha'awa dajin daɗi. Hannunsa ta riƙo ta zaunar ɗayan gefenta, ta ɗiba abincin takai bakinsa, “Haa!” ta faɗa kamar yanda akema yara. Ƙwallane suka cika idanun Jawaad ya buɗe bakinsa a hankali ta zuba masa, taunawa ya shigayi yana kallon yanda take sakama Bilkisu itama, gabansu Anuwar yazo ya durƙusa shima ya buɗe baki wai a basa. Umm-Anum ta zuba masa tare da dungure kansa. Anum ma zuwa tai ta tsugunna tana faɗin, “ALLAH nima sai an bani to, anma manta dani kamar banice autar ba”. Sosai abin ya bama Jawaad nishaɗi, su Bilkisu suka shiga yima Anum dariyar tsokana.
Hannunsa Jay ya ɗauraye, shima ya ɗiba ya kai bakin Umm-Anum, amsa tai tana murmushi ta shafa kansa da ƙoƙarin haɗiye hawayen da suke neman taho mata, murmushi Jay yayi ya ɗiba ya bama Anuwar shima, sannan ya bama Bilkisu da kunya ta kusan halakawa, Anum itace ƙarshe. Daka gansu kasan suna cikin farin ciki mai tsanani.
Haka suka ƙarasa wannan yini tare, har zuwa dare dan Abbu yau a gidan Uwargidansa ma yake ba nanba, hakan ne ya ƙara bama Umm-Anum damar sakewa da ƴaƴanta har dare ya farayi, daƙyar ta daure tace suje su kwanta haka nan gobe idan ALLAH ya kaimuma ranace ai. Da wannan kowa ya nufi makwancinsa badan sun gaji da kasancewa tare ba.
Chapter 120 · 0% Book details