Sashe 56
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Zuwa 10:30am na safe dukkan mai alhakin tofa albarkacin baki akan wannan matsalar ya hallara a gidan Dady, bisa umarnin Alhaji baba daya buƙaci hakan, dan yanason jin gaskiyar magan akan abinda Jawaad ya faɗa masa gameda zancen Azeema da yace sunsani. Jawaad yana jerin waɗanda sukazo a farko-farko dan tare yake da Alhaji baba, hakan kuwa yaso bama kowa mamaki dan sunsan halinsa sarai da iya ƙin zuwa wajen meeting akan lokaci saiya gama shanya jama'a, amma yau abin mamaki sai gashi cikin masu sakkon zuwa.
Bayan isowar Imam da wasu daga cikin manyan massallacin da aka ɗaura auren Salman da Qaseem daya rame sosai tamkar wanda ya kwana biyu yana jiyya suka shigo suma, ya ƙara haske da tsayi abin tausayi, Jawaad dai baiko kalli inda Qaseem yakeba, amma shi Qaseem sai binsa yake da wani irin mugun kallo tunda suka shigo.
Imam ne ya buɗe taro da addu'a, a kuma dai-dai lokacinne Shahudah da Mom da suka taho daga asibiti bisa matsawar Shahudahn suka shigo suma, wajen zama suka samu idon Shahudah akan Jawaad tana mai kwarar da hawaye, itama harta rame kwana ɗaya kacal. Bayan imam ya kammala addu'oi ya ɗaura bayani da cewar, “Nasan kowa dake nan yana neman amsar tambayarsane a gareni, wadda yinin jiya har zuwa dare na ɓata lokacine wajen nemota nima amma har safiyar yau ban samo amsarba, narasa wannan wane irin cuɗaɗɗen al'amarine mai sarƙaƙiya, a hasashena har junnu saida na kawo dukda bani da tabbacin haka balle hujja, ban saniba shin ko a cikinku wani nada amsar da nima nake cikin ruɗani da bulayin nemanta?”.
Shiru falon yayi babu wanda ya iyayin koda tari, sai shashshekar kukan Shahudah kawai ke tashi. Uncle Nasir ne yay ƙarfin halin bama Shahudah umarni akan ta tashi ta fita. kafaɗa ta maƙe alamar bazata tashinba, ta koma jikin Momy ta lafe tana masa kallon harara dukda kasancewarsa wan uwarta. Babu wanda ya iya sake cewa komai game da tashin Shahudah, dan kuwa anga iyayenta basu tankaba alamar basu da damuwa da zaman nata su. Jawaad yay gyaran muryar da kowa ya maida hankali kansa, batare da ya kalli kowaba yace, “Imam kayi haƙuri, babu ta inda zaka iya samo amsar sarƙaƙiyar jiya kaida duk wanda keda alhakin sanin sirrin massallacin nan. Ni dasu Momy mune kawai masu wannan amsar, dukda inada tabbaci da yaƙinin bayanmu wasu sunsan komai koda ba duka ba”. kaf falon babu wanda bai sagade yana kallon Jawaad ba, yayinda Momy ta miƙe zumbur tana nunashi, “Amma kai dai Jawaad anyi shaiɗanin yaro, a gidan ubanwa nake da amsar? Ni dama tun jiya da akace an nemeka an rasa nasan kaine shaiɗanin daya dace a nema dukka
n amsoshinnan a wajenka.......”
Murmushi Jay yayi, sai dai baice komaiba, hasalima kansa a duƙe yake bai kalli kowaba har yanzun. Alhaji baba ne ya tsaida Momy jin tanata aibanta masa jika, “A'ishatu, inaga mubashi dama muji ina maganganunsa suka dosa kafin mu yanke hukunci koda na furucin bakine, mudukanmu nan a ƙage muke dason jin amsa, yakamata muji yaya akai aka kwana a ragaya bayan munsan shirinmu a tandun mai ne”. Magana Momy zata sakeyi Qaseem yace, “Momy Please ki zauna miji munafurcin dazai faɗa”. Ƙwafa Momy tayi ta koma ta zauna saboda gargaɗin da Uncle Uwaisu yay mata da idanu.
Shirun da akaine ya saka Jawaad ɗagowa, yace, “Inaga kafin warware dukkan sarƙaƙiyar massallaci yakama musan wacece Azeema da aka ɗaurama Qaseem aure da ita? Domin wannan shine kawai zai zama mabuɗin buɗe mana gaskiyar abinda muke son sani baki ɗaya”. Tsit falon yay saboda bugawar da zukatansu sukai a lokaci ɗaya babu zato ko tsammani da zuwa furucin Jawaad ɗin a garesu. Alhaji baba ya katse shirun da cewar, “Banda abunka Muhammad Jawaad muma ai duk amsar da muke nema kenan akan Habib da Azeema?”.
Jawaad yace, “Hakane Alhaji baba, amma ina ganin karmu jata da nisa, domin su Uncle duk sunsan wacece Azeema da Habib, idan ka cire Imam da jama'arsa, kai da Uncle Sulaiman, Uncle Sadiq, Qaseem, kune kaɗai kuke neman ƙarin bayani”. Uncle Sulaiman yace, “To mukam saiku amsa mana kunata sake dilmiyar damu a hasashe”. Fuskar Uncle Nasir a matuƙar ɗaure cikin kafe Jawaad da idanu yace, “Mikake nufi da waɗanan kalaman naka?”.
Jawaad yace, “Babu abinda nake nufi Uncle, kawai dai ina son kowa ya fahimci daga ina matsalar take harshi Qaseem ɗin da aka ɗaurama aure.......”
Cike da masifa Momy ta sake katse Jawaad da faɗin, “Inma wani munafurci ka ƙulla kai zai ƙaremawa, inace dai sokake kace mune muka haɗa auren Azeema da Qaseem batare daya saniba, to ai mun isane, yarinyar da ya kawo yanason zai aura batai manaba, tayaya idan shi baisan ciwon kansaba mu zamu biye masa duk muzama mahaukatan?”.
Cikin ɓacin rai Jay yace, “Amma miyasa ni da nazo neman a bani na aura kukace Qaseem shi zai aureta?”. Yanzukam tamkar Momy zata mari Jawaad ta bashi amsa a matuƙar zafafe “Saboda Shahudah tafi ƙarfin yin kishi da ita, bandama rashin mutunci da raini irin naka Jawaad, bakaji kunyar zuwa a gaban idanunmuba kace mu haɗa maka ƴar cikinmu da wadda mukema alfarma mu aura maka”. Sosai zuciyar Jawaad take sake hasala, sai dai ƙoƙarin dannewa yake dan koba komai Momy yayar mahaifinsa ce ita, cikin ƙoƙarin danne fushinsa yace, “Amma Momy dan kawai baƙwa ɓuƙatar marainiyar ALLAH ta jingini da jininku sai kuje ku biya wani kuɗi dan ya aureta bayan kunsan shiɗin ba mutumin kirki baneba? Wai shin nawa ita wannan duniyar take da har muke tunanin wanda muka tseramawa bazai taɓa taddomu ba? Baƙwason ta auri ɗanku, baƙwason tayi kishi da ƴarku, tominene fa'idar biyan wani ya aureta? Saiku barta ALLAH ya kawo mata wani mijin, shi kuma Qaseem ku sanar masa bakwason alaƙarsa da ita bawai saikun cutar da itaba ta hanyar da batajiba bata ganiba.......”
Qaseem ya miƙe a fusace zaiyi magana Uncle Sulaiman da baƙin ciki ya lulluɓe yay saurin katseshi daga shi har Jawaad ɗin, yace “Kai Qaseem kaga zauna, ku kuma Kunga kudaina mana magana a cuɗe daga kai har Humaira, shin minene ya faru?”.
Sosai zuwa yanzu fushin Jawaad ya kasa dannuwa, cikin zafin zuciya da kowa yasanshi da ita idan aka kaisa bango yace, “Wato Uncle yarinyace suke riƙo a gidansu, har takai maganar aure ya shiga tsakaninta da Qaseem, kuma sune suka amince masa, amma kuma sai suka koma ta bayan fage suka nema masa auren Azeemar gwaggo Hajarah. Bayan kuma Alhaji baba yaje akan su bani auren yarinyar amma suka nuna min cewar shi Qaseem ɗinne zai aureta. Abinda kuma zai baka mamaki ita kuma yarinyar suka samu wani da sam ba mutumin kirki bane suka biyashi akan zasu aura masa ita yarinyar batare datasan da shirinsu ba, kuma sun nuna masa duk badaƙalar da za'ayi karya sake ya saketa, wannan shine dalilin dayasa na koma nima ta hanyar da sukabi na canja nasu shirin
Bayan isowar Imam da wasu daga cikin manyan massallacin da aka ɗaura auren Salman da Qaseem daya rame sosai tamkar wanda ya kwana biyu yana jiyya suka shigo suma, ya ƙara haske da tsayi abin tausayi, Jawaad dai baiko kalli inda Qaseem yakeba, amma shi Qaseem sai binsa yake da wani irin mugun kallo tunda suka shigo.
Imam ne ya buɗe taro da addu'a, a kuma dai-dai lokacinne Shahudah da Mom da suka taho daga asibiti bisa matsawar Shahudahn suka shigo suma, wajen zama suka samu idon Shahudah akan Jawaad tana mai kwarar da hawaye, itama harta rame kwana ɗaya kacal. Bayan imam ya kammala addu'oi ya ɗaura bayani da cewar, “Nasan kowa dake nan yana neman amsar tambayarsane a gareni, wadda yinin jiya har zuwa dare na ɓata lokacine wajen nemota nima amma har safiyar yau ban samo amsarba, narasa wannan wane irin cuɗaɗɗen al'amarine mai sarƙaƙiya, a hasashena har junnu saida na kawo dukda bani da tabbacin haka balle hujja, ban saniba shin ko a cikinku wani nada amsar da nima nake cikin ruɗani da bulayin nemanta?”.
Shiru falon yayi babu wanda ya iyayin koda tari, sai shashshekar kukan Shahudah kawai ke tashi. Uncle Nasir ne yay ƙarfin halin bama Shahudah umarni akan ta tashi ta fita. kafaɗa ta maƙe alamar bazata tashinba, ta koma jikin Momy ta lafe tana masa kallon harara dukda kasancewarsa wan uwarta. Babu wanda ya iya sake cewa komai game da tashin Shahudah, dan kuwa anga iyayenta basu tankaba alamar basu da damuwa da zaman nata su. Jawaad yay gyaran muryar da kowa ya maida hankali kansa, batare da ya kalli kowaba yace, “Imam kayi haƙuri, babu ta inda zaka iya samo amsar sarƙaƙiyar jiya kaida duk wanda keda alhakin sanin sirrin massallacin nan. Ni dasu Momy mune kawai masu wannan amsar, dukda inada tabbaci da yaƙinin bayanmu wasu sunsan komai koda ba duka ba”. kaf falon babu wanda bai sagade yana kallon Jawaad ba, yayinda Momy ta miƙe zumbur tana nunashi, “Amma kai dai Jawaad anyi shaiɗanin yaro, a gidan ubanwa nake da amsar? Ni dama tun jiya da akace an nemeka an rasa nasan kaine shaiɗanin daya dace a nema dukka
n amsoshinnan a wajenka.......”
Murmushi Jay yayi, sai dai baice komaiba, hasalima kansa a duƙe yake bai kalli kowaba har yanzun. Alhaji baba ne ya tsaida Momy jin tanata aibanta masa jika, “A'ishatu, inaga mubashi dama muji ina maganganunsa suka dosa kafin mu yanke hukunci koda na furucin bakine, mudukanmu nan a ƙage muke dason jin amsa, yakamata muji yaya akai aka kwana a ragaya bayan munsan shirinmu a tandun mai ne”. Magana Momy zata sakeyi Qaseem yace, “Momy Please ki zauna miji munafurcin dazai faɗa”. Ƙwafa Momy tayi ta koma ta zauna saboda gargaɗin da Uncle Uwaisu yay mata da idanu.
Shirun da akaine ya saka Jawaad ɗagowa, yace, “Inaga kafin warware dukkan sarƙaƙiyar massallaci yakama musan wacece Azeema da aka ɗaurama Qaseem aure da ita? Domin wannan shine kawai zai zama mabuɗin buɗe mana gaskiyar abinda muke son sani baki ɗaya”. Tsit falon yay saboda bugawar da zukatansu sukai a lokaci ɗaya babu zato ko tsammani da zuwa furucin Jawaad ɗin a garesu. Alhaji baba ya katse shirun da cewar, “Banda abunka Muhammad Jawaad muma ai duk amsar da muke nema kenan akan Habib da Azeema?”.
Jawaad yace, “Hakane Alhaji baba, amma ina ganin karmu jata da nisa, domin su Uncle duk sunsan wacece Azeema da Habib, idan ka cire Imam da jama'arsa, kai da Uncle Sulaiman, Uncle Sadiq, Qaseem, kune kaɗai kuke neman ƙarin bayani”. Uncle Sulaiman yace, “To mukam saiku amsa mana kunata sake dilmiyar damu a hasashe”. Fuskar Uncle Nasir a matuƙar ɗaure cikin kafe Jawaad da idanu yace, “Mikake nufi da waɗanan kalaman naka?”.
Jawaad yace, “Babu abinda nake nufi Uncle, kawai dai ina son kowa ya fahimci daga ina matsalar take harshi Qaseem ɗin da aka ɗaurama aure.......”
Cike da masifa Momy ta sake katse Jawaad da faɗin, “Inma wani munafurci ka ƙulla kai zai ƙaremawa, inace dai sokake kace mune muka haɗa auren Azeema da Qaseem batare daya saniba, to ai mun isane, yarinyar da ya kawo yanason zai aura batai manaba, tayaya idan shi baisan ciwon kansaba mu zamu biye masa duk muzama mahaukatan?”.
Cikin ɓacin rai Jay yace, “Amma miyasa ni da nazo neman a bani na aura kukace Qaseem shi zai aureta?”. Yanzukam tamkar Momy zata mari Jawaad ta bashi amsa a matuƙar zafafe “Saboda Shahudah tafi ƙarfin yin kishi da ita, bandama rashin mutunci da raini irin naka Jawaad, bakaji kunyar zuwa a gaban idanunmuba kace mu haɗa maka ƴar cikinmu da wadda mukema alfarma mu aura maka”. Sosai zuciyar Jawaad take sake hasala, sai dai ƙoƙarin dannewa yake dan koba komai Momy yayar mahaifinsa ce ita, cikin ƙoƙarin danne fushinsa yace, “Amma Momy dan kawai baƙwa ɓuƙatar marainiyar ALLAH ta jingini da jininku sai kuje ku biya wani kuɗi dan ya aureta bayan kunsan shiɗin ba mutumin kirki baneba? Wai shin nawa ita wannan duniyar take da har muke tunanin wanda muka tseramawa bazai taɓa taddomu ba? Baƙwason ta auri ɗanku, baƙwason tayi kishi da ƴarku, tominene fa'idar biyan wani ya aureta? Saiku barta ALLAH ya kawo mata wani mijin, shi kuma Qaseem ku sanar masa bakwason alaƙarsa da ita bawai saikun cutar da itaba ta hanyar da batajiba bata ganiba.......”
Qaseem ya miƙe a fusace zaiyi magana Uncle Sulaiman da baƙin ciki ya lulluɓe yay saurin katseshi daga shi har Jawaad ɗin, yace “Kai Qaseem kaga zauna, ku kuma Kunga kudaina mana magana a cuɗe daga kai har Humaira, shin minene ya faru?”.
Sosai zuwa yanzu fushin Jawaad ya kasa dannuwa, cikin zafin zuciya da kowa yasanshi da ita idan aka kaisa bango yace, “Wato Uncle yarinyace suke riƙo a gidansu, har takai maganar aure ya shiga tsakaninta da Qaseem, kuma sune suka amince masa, amma kuma sai suka koma ta bayan fage suka nema masa auren Azeemar gwaggo Hajarah. Bayan kuma Alhaji baba yaje akan su bani auren yarinyar amma suka nuna min cewar shi Qaseem ɗinne zai aureta. Abinda kuma zai baka mamaki ita kuma yarinyar suka samu wani da sam ba mutumin kirki bane suka biyashi akan zasu aura masa ita yarinyar batare datasan da shirinsu ba, kuma sun nuna masa duk badaƙalar da za'ayi karya sake ya saketa, wannan shine dalilin dayasa na koma nima ta hanyar da sukabi na canja nasu shirin