Sashe 83
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
dhana, manya da ƙananun yara harma da tsaffi kowa ya tashi da wannan ibada a baki cike da ɗoki da fatan kammalawa lafiya. Yayinda Bilkisu ke kallon ikon ALLAH wajensu gambiya dangane da alkairin da ake fita dashi domin talakawa. Abin sai ya birgeta, a cikin ranta tana fatan kwatantawa taji idan zata iya watanara, sannan har yau da take nufar sati na biyu a masarautar bata taɓa gamo da Sarki Sameer ba, Safah ta sanar mata yaje saudia hutawa shida amaryarsa da suke kira Ammi, sai azumi yaje tsakkiya zai dawo sukuma su tafi Umarah
★★★★
Jay da muƙarrabansa sunyi busy matuƙa, ga aiki ga aikin sa kai gana hidimar bayin ALLAH duk ya haɗama kansa, burinsa ya kammala abubuwa da yawa cikin watannan, baya neman Bilkisu ne dan yana tausayinta sosai, ga azumi ga rana dan ruwa bai zaunaba sosai, gani yay ta rame masa a kwanakinan sosai sai tai haske kuma.
Abin mamaki Rose kuma saita shiga ja baya dasu, har takai saida Jay yamata magana da kasa, ranar kam dai yaga taɓara da iyayi, gashi yanaji da azuminsa. Shidai ya lalaɓata kawai dan yana buƙatar nutsuwa baison hayaniya.
Tuni yasa ana bibiyar masa bayan Ɓaleru duk inda ya sanya ƙafa batare da shi ya saniba, bayason kamasa a cikin watannan mai albarka shiyyasa yay tamkar ya manta da al'amarinsa, ga jikin ɗan-fir'auna da har gidan su Shahudah suka ɗauka ya mutu na nata sauƙi da warwarewa.
______________________
Kwanci tashi babu wahala wajen UBANGIJI azumi yakai tsakkiya, a daren sha bakwai sarki Sameer da Amaryarsa suka dawo, anyi murna da dawowar tasu sosai, dan ranar kam kowa ya shaida hakan a masarautar gagara badau, ranar gimbiya da kanta taima Takawa abincin buɗa baki a kicin ɗinta na sirri da babu mai shiga sai ita saiko Amintacciyar baiwarta. Tunda ta tafi ɓangarensa su bily basu sake jin ɗuriyartaba sai washe gari, sai a randa za'a ɗau azumi na sha takwas ne suka ganta, shima dan tasaka a kira mata bily ne.
Cikin girmamawa na gaisheta kamar yanda na saba, fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa min tare da kamo hannayena cikin nata. “Ɗiyata dama nasa a kiramin kene saboda zaku wuce Umrah gobe idan ALLAH ya kaimu ke da su Amaturrahman, an kammala miki komai insha ALLAH” Dama Boss ya sanarmin tun shekaranjiya, sai dai na nuna mata farin cikina sosai akan hakan itama tamkar bansan da tafiyarba, nakuma mata godiya. Ta cigaba da faɗin, “Naso ace tun farkon azumi kika tafi, sai dai mijinki ya sanarmin hakan bazai yuwuba saboda aikinki, dan akwai wata auntyna matar yayan abokin Takawa tanada makaranta ta musamman domin koyar da amare, ana gyaran jiki da komai a ciki, koya girki da dukkan dabarun zaman aure, itama ƴar nan ƙasarmu ce, dalilin ƙaddara ta shigo rayuwarmu, mun kaita domin neman magani sai yayan abokin Takawa yace shifa yayi mata, wannan shine dalilin zamanta a can itama”. Fuskata ɗauke da murmushi nace, “ALLAH sarki”. Itama murmushi tayi, “Yanzu dai yayi dukkan cuku-cukun daya dace a wajen aikinku insha ALLAH keda nan sai saura kwana biyar tarewarki, inason naga kin zama cikakkiyar mace mai amsa suna mace a fadar mijinta, mijinki babban mutumne sannan yanada wasu sirrika dake kaɗai zaki fahimci kayanki anan gaba, shiyyasa nakeso a gyaramin ke yanda ya kamata domin zukatan maƙiya su girgiza, waɗanda suke ganin baki kaiba su fahimci kin musu zarrah ta har abada kinji”. Hawayen dake ziraromin na share, bansan irin godiyar da zanma wannan baiwaba a rayuwata, itaɗin ta musamman ce a cikin jerin abubuwa masu muhimmanci da suka shigo rayuwata, ALLAH ya biyata da aljannarsa.
Washe garima naje wajen aiki, sai dai yau bashi ya maidoni ba sawa yay sabon direbansa ya maidoni, gobe idan ALLAH ya kaimu kuma bazanje aikiba, dan ƙarfe huɗu zamu wuce, share hawayen dake zubomin nake akan abinda ya faru tsakanina dashi yanzu a office ɗinsa. Na roƙesane akan zanje gidan Dad nai masa sallama, dama tun farkon azuminan naketa masa magiyar ya kaini na gaishesa, bai taɓa kulaniba sai yau da yanema marina a office, yajamin dogon gargaɗi akan inhar na sake masa maganar Dad ALLAH sai ya fasan baki. Sake share hawayen nai zuciyata namin zafi da takaucinsa,
ni bansan mi Dad yaymasaba haka da zafi shi da ahalinsa, inason ganin koda mutum ɗayane a cikinsu amma abin ya gagara, sam yanzu bana ganin Yah Qaseem, narasa ina ya shiga baya zuwa Office, mike damunsa? Minene matsalarsa? Haka kawai bazai bar zuwa office ba ai?. Zafin boss yayi yawa, nikuma har zuwa yanzun ban taɓa jin sonsa a rainaba, nasan dai zan iya haƙurin zaman aure dashi amma badan inajinsa a raina da kalmar soyayya ba, bansan miyasa hakanba, har zuwa yanzu Yah Qaseem ne kaɗai a zuciyata, shi nakeso, shi na fara so, sai dai shikuma banajin sha'awar zama dashi matsayin miji, bansan miyasa hakanba shima. Ya ALLAH ka kawomin ɗauki bisa ruɗaɗɗen tunanina daya banbanta dana sauran mutane a yanzu.
Har muka bar ƙasar bana cikin walwala sam, sai wata irin matsananciyar damuwa da na tsinci zuciyata a ciki, wannan dalilin yasa har jirginma ya tashi ban tuna shine hawana na farkoba, Safah na lafe a jikina tana barci har muka sauka. mun sami tarba ta musamman daga wasu manyan mutane da bansan matsayinsu ba, sai dai ina tunanin waɗanda Gimbiya taban taƙaitaccen labarinsu ne ranar, sai dai wannan nafi ƙyautata zaton abokin takawane da iyalansa ba waccan mai makarantar bace da naji nafi ɗokin gani. Ƴan uwa abu mafi ɗaure kaina shine, maimakon najini cikin farin ciki da zuwa ƙasa mai tsarki a karo na farko a rayuwata sai saɓanin hakan ya biyo baya, kallonsu nike kawai tamkar wata sakarai, ƙirjina na wani irin zafi, sai can ƙasan zuciyata kuma nakejin wani irin sanyi dake kawomin sassauci a cikin ƙirjina kaɗan-kaɗan. Darene sosai, dan haka makwanci kawai aka bamu da abinci, nikam bammaciba na kwanta.
__________________________
Yau tunda ya tashi aiki wanka kawai yaje yay a gida ya kimtsa, sabon drivernsa mai suna Sadiq ya ɗaukesa sai gidan Alhaji Babba dan acan yake buɗa baki yanzun kullum, wataran kuma gidan Ummah babba, kokuma gidan Ummah ƙarama idan ta ishesa da ƙorafi. Haka kawai yau yakejin tamkar wani abu dake nesa dashi yana tunkarosa, minene? A ina yake? Itace amsar dakanzo masa akai-akai cikin shauƙinsa.
Shi dai Alhaji babba kallonsa kawai yake amma baice komaiba, sai da suka dawo salla sukai zaman buɗa baki sannan, ya kai dubansa ga Jay da keta juya cokali cikin kofin kuni yana ɗan murmushi. “Wai nikam gwauron nan yau miya saka farin ciki haka?”. Kallonsa Jay yay fuskarsa ɗauke da murmushin har yanzun, yace, “Babu komai Baba, kawai dai”. Murmushi shima Alhaji baban yayi, “Kawai dai haka ka tsinci kanka kaima ko?”. Kai Jay ya jinjina masa yana lumshe ido. Alhaji babba yace, “Nima haka na tashi da farin ciki, sai nakeji tamkar wani abu dana daɗe da rasawa zai dawo gareni, sai nakeji kamar wani abuna mai muhimmanci ya haɗu da abuna mai muhimmanci, sai nakeji kamar wani abun da na daɗe ina neman amsarsane lokacin sanin amsar yayi, a daren jiya nayi mafarkin ƴaƴana guda biyu cikin farin ciki, tabbas Jawaad inaji a raina wani abu mai daraja da haske na matsowa zuwa garemu”. Jawaad sauraren Alhaji babba kawai yake yana murmushi irin wanda ya kasance mai tsada a garesa, ya ɗora kansa a kafaɗar kakansa yana sake ƙawata murmushinsa, “Ya ALLAH ya tabbatar da wannan hasashe naka ya zama alkairi kakana”. Shafa kansa Alhaji babba yay yana murmushi da faɗin, “Amin ya rabbi jikallena, amma yakama ka dawo nan kwanaki goman nan na ƙarshe muyisu tare cikin ƙololuwar ibada, ka ajiye duk wani aiki gefe”. Jay ya tashi zaune sosai yana kallon kakan nasa, yace, “Nima nayi wannan tunanin, sai dai banason takura maka da yawa”. Ranƙwashi Alhaji babba ya kai masa bisa kai, Jay yay saurin kaucewa yana dariya da haɗe hannayensa waje guda alamar na tuba.
Bayan sun dawo daga salla suka iske Ummah babba da ƙarama sunzo, dama sunce yau zasuzo. Jay ya zauna tsakkiyarsu yana dariya da faɗin, “Saini ɗan gatan ALLAH, Ummahs ɗina duka tare dani”. Atare sukai dariya da riƙe hannayensa, Ummah babba tace, “Ja'iri kamar ya wani damu damu?”. Karyar da kai Jay yayi ya ɗora saman kafaɗarta, murya a sanyaye yace, “Idan ban damu da kuba dawa zan damu Ummah?, kuɗin duniyatace, sannan haskena, aikine kawai ke hanani rawar gab
an hantsi”. Guntuwar dariya tayi da shafa kansa, ta sumbaci hannunsa tana mai saka masa albarka.
Kasancewar basu da ishashen lokaci suka fara tattaunawa akan maganar lefe da dama shine ya kawosu. Da farko Jawaad yace su barsa zaiyi, amma sukace sam bazai yuwuba, na farkoma dan an nuna musu fin ƙarfine Uncles ɗinsa sukace zasuyi, to wannan kam suma sune zasuyi insha ALLAH.
Jawaad yay shiru yana murmushi dajin ƙaunarsu mai narkar da zuciya na ratsasa, zamansa ya gyara a kujerar daya koma shi kaɗai yana kallonsu, “Nagode sosai iyayena, kun sharemin hawayen maraici tuni, bani da abin biyanku sai dai naita muku addu'oin gamawa da rauwa lafiya, idan na ganku saina manta bani da Uwa, idan kuka kalleni sai nake ganin Mah-mah har yanzu tana tare dani, ida har tabar duniya ina roƙon UBANGIJI yasa ana nuna mata dukkan alkairanku ga gudan jininta, idan tana duniya ina fatan ganinta na bata labarin alkairanku ga gudan jininta, ku......” “Ya isa haka kaji Muhammadu, insha ALLAH inaji a jikina BILKEESU tana raye, insha ALLAH kafin nabar duniya saina ganta” Alhaji babba yay maganar yana share hawayen da suka ɗan zubo masa. Ummah da Ummah ƙarama ma kuka suke, Jay gwanin dakiya babu hawayen zahiri saina zuci kawai.
____________________________
★★★★
Jay da muƙarrabansa sunyi busy matuƙa, ga aiki ga aikin sa kai gana hidimar bayin ALLAH duk ya haɗama kansa, burinsa ya kammala abubuwa da yawa cikin watannan, baya neman Bilkisu ne dan yana tausayinta sosai, ga azumi ga rana dan ruwa bai zaunaba sosai, gani yay ta rame masa a kwanakinan sosai sai tai haske kuma.
Abin mamaki Rose kuma saita shiga ja baya dasu, har takai saida Jay yamata magana da kasa, ranar kam dai yaga taɓara da iyayi, gashi yanaji da azuminsa. Shidai ya lalaɓata kawai dan yana buƙatar nutsuwa baison hayaniya.
Tuni yasa ana bibiyar masa bayan Ɓaleru duk inda ya sanya ƙafa batare da shi ya saniba, bayason kamasa a cikin watannan mai albarka shiyyasa yay tamkar ya manta da al'amarinsa, ga jikin ɗan-fir'auna da har gidan su Shahudah suka ɗauka ya mutu na nata sauƙi da warwarewa.
______________________
Kwanci tashi babu wahala wajen UBANGIJI azumi yakai tsakkiya, a daren sha bakwai sarki Sameer da Amaryarsa suka dawo, anyi murna da dawowar tasu sosai, dan ranar kam kowa ya shaida hakan a masarautar gagara badau, ranar gimbiya da kanta taima Takawa abincin buɗa baki a kicin ɗinta na sirri da babu mai shiga sai ita saiko Amintacciyar baiwarta. Tunda ta tafi ɓangarensa su bily basu sake jin ɗuriyartaba sai washe gari, sai a randa za'a ɗau azumi na sha takwas ne suka ganta, shima dan tasaka a kira mata bily ne.
Cikin girmamawa na gaisheta kamar yanda na saba, fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa min tare da kamo hannayena cikin nata. “Ɗiyata dama nasa a kiramin kene saboda zaku wuce Umrah gobe idan ALLAH ya kaimu ke da su Amaturrahman, an kammala miki komai insha ALLAH” Dama Boss ya sanarmin tun shekaranjiya, sai dai na nuna mata farin cikina sosai akan hakan itama tamkar bansan da tafiyarba, nakuma mata godiya. Ta cigaba da faɗin, “Naso ace tun farkon azumi kika tafi, sai dai mijinki ya sanarmin hakan bazai yuwuba saboda aikinki, dan akwai wata auntyna matar yayan abokin Takawa tanada makaranta ta musamman domin koyar da amare, ana gyaran jiki da komai a ciki, koya girki da dukkan dabarun zaman aure, itama ƴar nan ƙasarmu ce, dalilin ƙaddara ta shigo rayuwarmu, mun kaita domin neman magani sai yayan abokin Takawa yace shifa yayi mata, wannan shine dalilin zamanta a can itama”. Fuskata ɗauke da murmushi nace, “ALLAH sarki”. Itama murmushi tayi, “Yanzu dai yayi dukkan cuku-cukun daya dace a wajen aikinku insha ALLAH keda nan sai saura kwana biyar tarewarki, inason naga kin zama cikakkiyar mace mai amsa suna mace a fadar mijinta, mijinki babban mutumne sannan yanada wasu sirrika dake kaɗai zaki fahimci kayanki anan gaba, shiyyasa nakeso a gyaramin ke yanda ya kamata domin zukatan maƙiya su girgiza, waɗanda suke ganin baki kaiba su fahimci kin musu zarrah ta har abada kinji”. Hawayen dake ziraromin na share, bansan irin godiyar da zanma wannan baiwaba a rayuwata, itaɗin ta musamman ce a cikin jerin abubuwa masu muhimmanci da suka shigo rayuwata, ALLAH ya biyata da aljannarsa.
Washe garima naje wajen aiki, sai dai yau bashi ya maidoni ba sawa yay sabon direbansa ya maidoni, gobe idan ALLAH ya kaimu kuma bazanje aikiba, dan ƙarfe huɗu zamu wuce, share hawayen dake zubomin nake akan abinda ya faru tsakanina dashi yanzu a office ɗinsa. Na roƙesane akan zanje gidan Dad nai masa sallama, dama tun farkon azuminan naketa masa magiyar ya kaini na gaishesa, bai taɓa kulaniba sai yau da yanema marina a office, yajamin dogon gargaɗi akan inhar na sake masa maganar Dad ALLAH sai ya fasan baki. Sake share hawayen nai zuciyata namin zafi da takaucinsa,
ni bansan mi Dad yaymasaba haka da zafi shi da ahalinsa, inason ganin koda mutum ɗayane a cikinsu amma abin ya gagara, sam yanzu bana ganin Yah Qaseem, narasa ina ya shiga baya zuwa Office, mike damunsa? Minene matsalarsa? Haka kawai bazai bar zuwa office ba ai?. Zafin boss yayi yawa, nikuma har zuwa yanzun ban taɓa jin sonsa a rainaba, nasan dai zan iya haƙurin zaman aure dashi amma badan inajinsa a raina da kalmar soyayya ba, bansan miyasa hakanba, har zuwa yanzu Yah Qaseem ne kaɗai a zuciyata, shi nakeso, shi na fara so, sai dai shikuma banajin sha'awar zama dashi matsayin miji, bansan miyasa hakanba shima. Ya ALLAH ka kawomin ɗauki bisa ruɗaɗɗen tunanina daya banbanta dana sauran mutane a yanzu.
Har muka bar ƙasar bana cikin walwala sam, sai wata irin matsananciyar damuwa da na tsinci zuciyata a ciki, wannan dalilin yasa har jirginma ya tashi ban tuna shine hawana na farkoba, Safah na lafe a jikina tana barci har muka sauka. mun sami tarba ta musamman daga wasu manyan mutane da bansan matsayinsu ba, sai dai ina tunanin waɗanda Gimbiya taban taƙaitaccen labarinsu ne ranar, sai dai wannan nafi ƙyautata zaton abokin takawane da iyalansa ba waccan mai makarantar bace da naji nafi ɗokin gani. Ƴan uwa abu mafi ɗaure kaina shine, maimakon najini cikin farin ciki da zuwa ƙasa mai tsarki a karo na farko a rayuwata sai saɓanin hakan ya biyo baya, kallonsu nike kawai tamkar wata sakarai, ƙirjina na wani irin zafi, sai can ƙasan zuciyata kuma nakejin wani irin sanyi dake kawomin sassauci a cikin ƙirjina kaɗan-kaɗan. Darene sosai, dan haka makwanci kawai aka bamu da abinci, nikam bammaciba na kwanta.
__________________________
Yau tunda ya tashi aiki wanka kawai yaje yay a gida ya kimtsa, sabon drivernsa mai suna Sadiq ya ɗaukesa sai gidan Alhaji Babba dan acan yake buɗa baki yanzun kullum, wataran kuma gidan Ummah babba, kokuma gidan Ummah ƙarama idan ta ishesa da ƙorafi. Haka kawai yau yakejin tamkar wani abu dake nesa dashi yana tunkarosa, minene? A ina yake? Itace amsar dakanzo masa akai-akai cikin shauƙinsa.
Shi dai Alhaji babba kallonsa kawai yake amma baice komaiba, sai da suka dawo salla sukai zaman buɗa baki sannan, ya kai dubansa ga Jay da keta juya cokali cikin kofin kuni yana ɗan murmushi. “Wai nikam gwauron nan yau miya saka farin ciki haka?”. Kallonsa Jay yay fuskarsa ɗauke da murmushin har yanzun, yace, “Babu komai Baba, kawai dai”. Murmushi shima Alhaji baban yayi, “Kawai dai haka ka tsinci kanka kaima ko?”. Kai Jay ya jinjina masa yana lumshe ido. Alhaji babba yace, “Nima haka na tashi da farin ciki, sai nakeji tamkar wani abu dana daɗe da rasawa zai dawo gareni, sai nakeji kamar wani abuna mai muhimmanci ya haɗu da abuna mai muhimmanci, sai nakeji kamar wani abun da na daɗe ina neman amsarsane lokacin sanin amsar yayi, a daren jiya nayi mafarkin ƴaƴana guda biyu cikin farin ciki, tabbas Jawaad inaji a raina wani abu mai daraja da haske na matsowa zuwa garemu”. Jawaad sauraren Alhaji babba kawai yake yana murmushi irin wanda ya kasance mai tsada a garesa, ya ɗora kansa a kafaɗar kakansa yana sake ƙawata murmushinsa, “Ya ALLAH ya tabbatar da wannan hasashe naka ya zama alkairi kakana”. Shafa kansa Alhaji babba yay yana murmushi da faɗin, “Amin ya rabbi jikallena, amma yakama ka dawo nan kwanaki goman nan na ƙarshe muyisu tare cikin ƙololuwar ibada, ka ajiye duk wani aiki gefe”. Jay ya tashi zaune sosai yana kallon kakan nasa, yace, “Nima nayi wannan tunanin, sai dai banason takura maka da yawa”. Ranƙwashi Alhaji babba ya kai masa bisa kai, Jay yay saurin kaucewa yana dariya da haɗe hannayensa waje guda alamar na tuba.
Bayan sun dawo daga salla suka iske Ummah babba da ƙarama sunzo, dama sunce yau zasuzo. Jay ya zauna tsakkiyarsu yana dariya da faɗin, “Saini ɗan gatan ALLAH, Ummahs ɗina duka tare dani”. Atare sukai dariya da riƙe hannayensa, Ummah babba tace, “Ja'iri kamar ya wani damu damu?”. Karyar da kai Jay yayi ya ɗora saman kafaɗarta, murya a sanyaye yace, “Idan ban damu da kuba dawa zan damu Ummah?, kuɗin duniyatace, sannan haskena, aikine kawai ke hanani rawar gab
an hantsi”. Guntuwar dariya tayi da shafa kansa, ta sumbaci hannunsa tana mai saka masa albarka.
Kasancewar basu da ishashen lokaci suka fara tattaunawa akan maganar lefe da dama shine ya kawosu. Da farko Jawaad yace su barsa zaiyi, amma sukace sam bazai yuwuba, na farkoma dan an nuna musu fin ƙarfine Uncles ɗinsa sukace zasuyi, to wannan kam suma sune zasuyi insha ALLAH.
Jawaad yay shiru yana murmushi dajin ƙaunarsu mai narkar da zuciya na ratsasa, zamansa ya gyara a kujerar daya koma shi kaɗai yana kallonsu, “Nagode sosai iyayena, kun sharemin hawayen maraici tuni, bani da abin biyanku sai dai naita muku addu'oin gamawa da rauwa lafiya, idan na ganku saina manta bani da Uwa, idan kuka kalleni sai nake ganin Mah-mah har yanzu tana tare dani, ida har tabar duniya ina roƙon UBANGIJI yasa ana nuna mata dukkan alkairanku ga gudan jininta, idan tana duniya ina fatan ganinta na bata labarin alkairanku ga gudan jininta, ku......” “Ya isa haka kaji Muhammadu, insha ALLAH inaji a jikina BILKEESU tana raye, insha ALLAH kafin nabar duniya saina ganta” Alhaji babba yay maganar yana share hawayen da suka ɗan zubo masa. Ummah da Ummah ƙarama ma kuka suke, Jay gwanin dakiya babu hawayen zahiri saina zuci kawai.
____________________________