Sashe 66
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
wayar ya amsa masa sallama da gaisuwar da yake masa. “Ka isa garin nasu ne?” yay tambayar wa balarabe. Daga can muryar balarabe cike da damuwa yace, “Ganima harna dawo Alhaji, tun inacan naketa kiranka baka ɗagaba. sai dai baizo gidanba ma ashe, kuma mamansa tace har waya sunyi lokacin dazai taso”. Babu shiri Jawaad ya taka burki, yace, “Kana nufin canba gidaba tun ran juma'ar?”. “Eh wlhy Alhaji hakane”. Mutuwar zaune Jawaad yay a cikin motar, gabansa sai wata irin mahaukacin faɗuwa yake, cikin rawar jiki ya ɗauka wayar ya katse kiran balarabe ya fara laluben Jabeer. Yana ɗagawa ko sallama bai masaba yace, “Jabeer maza dubamin daga ina Gimba yake a halin yanzun?”. Daga can Jabeer yace, “Ƙila matarsa ta riƙesa bata gaji da ganin kayantaba”. A tsawace Jawaad yace, “Jabeer kabar wasa mana!!, ka nemomin yaron mutane Jabeer Please”. Ya ƙare maganar a hankali tamakar zai fashe da kuka. Hankalin Jabeer ne yay matuƙar tashi, baƙaramin girgiza zuciyarsa tayiba da jin yanda Jawaad yay magana da tsawa da sanyin murya kuma a ƙarshe. Jabeer yace “Yi haƙuri, yanzu kana Office ne?”. “Gani nan zuwa” kawai ya iya cemasa ya yanke wayar. Reverse yay tare ya figi motar da shegen gudu ya koma station.
A office ɗinsa ya iske Jabeer na jiransa, har wani jiri-jiri yakeji saboda tashin hankali, sai da ya zauna sannan Jabeer yace, “Mike faruwa da gimban?”.
“Jabeer nima ban saniba, ranar juma'a ya tafi weekend amma bai dawoba, shinefa nasa a bisa aga ko yana lafiya, amma sai aka tararma baijeba”.
Cikin ɗaurewar kai Jabeer yace, “Ya salam to ina yaje shiko? Yanzu abinda zamuyi bara mu bibiyi layin sa, ina fata kunyi waya dashi bayan tafiyar tasa?”. Kai kawai Jawaad ya girgizama Jabeer, yana faɗin, “Na kirashi jiya amma bai ɗagaba”. Jabeer yace, “Tunda dai kiran ya shiga zai taimaka mana”. Wayar kawai Jay ya miƙama Jabeer baice komaiba. Gaba ɗaya Jay ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai faman zagaye office ɗin yakeyi, Jabeer kuma nata ƙoƙarin ganin ya samo inda gimban yake, a haka Aliyu da Hafiz suka shigo suka samesa harma da Rose da dawowarta kenan daga tafiya. Haka suka duƙufa su huɗu suna taimakawa Jabeer. Inda alama ke nuna musu wayar gimba na nan ɗinne ya tada musu hankali har suka kasa aminta suketa sake ninƙayar bincike. Cikin girgiza kai Jabeer yace, “Kai abinnan akwai rikitarwa, mizai kaisa wannan dajin mai haɗari? Inaga bara nai magana da kamfanin layinan dan muna buƙatar bayanan da yafi haka”. Hafiz yace, “Hakan shine zai taimaka mana Jabeer, danni kainama ya kulle gaba ɗaya”.
Jawaad dai yama kasa cewa komai, zaune yake kawai tamkar butunbutumi. Aliyu ne yay kiran wanda yake musu aiki a kamfanin layin da gimba ke aiki dashi, bayan sunyi magana ya ajiye wayar Jabeer ya tura musu Number gimba.
Ganin magriba tayi Aliyu yace, “;
Boss ka kwantar da hankalinka, ni ina ganin ko wasune suka Kidnapping ɗinsa bazasu kaisa wannan jajejinba, kawai sunyi hakane domin rikita mana tunani, idan muka kwantar da hankalinmu zamu fahimci komai cikin sauƙi, yanzu dai Ma'aruff ɗin yace daganan zuwa safiya zai turo mana komai, inaga muje muyi salla da addu'ar ALLAH ya kuɓutar dashi a duk inda yake, a kuma hannun duk wanda yake”.
A tare suka amsa da amin har Jawaad.
Koda suka fito daga salla Jawaad ya tafi gidane kawai cike da matsananciyar damuwa, bai shiga gidaba sai da yay sallar isha'i.
A wannan dare idan har akace Jawaad yay barci to ɓarawone, kwana yay miƙama UBANGIJI kukansa akan gimba da murɗaɗɗun al'amuran dake faruwa a tsakaninan, roƙon ALLAH yake ya bashi ƙarfin zuciya dana jajircewa, ya kuma haskaka masa abinda yake a duhu daya gaza fahimta. Mutuwar ɗan-fir'auna, ɓatan gimba, mafarkinsa, dalilin aure da akaso yi tsakanin bilkisu da wanda ba mutumin kirkiba, damuwar da yaga Alhaji babba jiya a ciki. Duk wanda ya roƙa UBANGIJI yana mai ƙasƙantar da kai da fatan samu bai yanke ƙauna daga rahamarsaba ALLAH sai ya amince masa, ya kuma dafama al'amarinsa ta inda bai zato ko tsammani ba.
Jawaad ya tashine da wata irin dakiyar zuciya, duk wani ɗigon tsoro da fargaba daya haifarmasa da ruɗa
ni da kasala a daren jiya sai yaji sun gudu, ya tashi cike da yaƙinin son tunkarar abinda ke tunkarosa. Dolene koda zai halaka da izinin ALLAH sai ya gano suwaye suka kashe ɗan fir'auna, miyasa suka kasheshi?, minene a binne da rayuwarsa da ɗan-fir'auna yaso sanar masa, yanaji a jikinsa kisan ɗan fir'auna nada nasaba da abinda ya shafesa, minene shi? Wannan ne bai saniba.
Ƙarfe bakwai na safe ya gama shirinsa yabar gidan, yau ko gadonsa bai gyaraba, saƙo ya gani daga gimbiya Munaya akan zatasa akai Bilkisu wajen aiki basaima ya wahal da kansaba, idan sun tashi sai ya dinga maidota da kansa.
Yaji daɗin hakan, dan dama yanata juya yanda zai dinga yawonan batare da wataran yay lattiba shiɗinan gwani ayyuka da yawa. Station ya nufa cike da zumuɗin son zuwa yaji ya ake ciki akan gimba.
________________________________
Tunda muka shiga cikin masarauta notin kaina ya nema kwancewa, karon farko a tarihim rayuwata dana fara shigarta, ƴan uwa bansan yanda zan musalta muku abinda na ganiba, abinda kawai zan iya ce muku masarautar gagara badau wani katafaren garine kawai mai zaman kansa dake ɗauke da ɗumbin al'umma kala-kala masu abubuwan kallo. Kaina bai sake kuncewa ba sai da muka shiga sashen da naji ance na sarauniyane mahaifiyar su Amaturrahman, wato garin daɗi na nesa, angulu data leƙa masai. Nidai bana cewa uffan, binsu kawai nake tamkar raƙumi da akala. Mun yada zango a katafaren ɗakin Amaturrahman da Meenal sai Amatullah idan tazo daga Niger. Amaturrahman ce ta tsaya kaina da hidima har saida nai wanka na canja kaya aka kawo abinci ta takurani naci sannan ta barni na huta, muna zaune tana ɗan jana da hira saƙon gimbiya ya iso garemu daga amintacciyar baiwarta akan tace na kwanta na huta, kuma a bani dukkan kulawar data dace.
To lallai naga hidima mai ban mamaki da al'ajabi wadda har kuka sai da nayi, ashe nima mutumce mai daraja irin haka? Ɗawainiyar da akeyi dani ta zabtare kaso mafi yawa na damuwar da nake ciki akan abubuwa kashi-kashi da basu ƙirguwa, tunda Safah kuma taji labarin nazo tadawo ɗakin su Amaturrahman ta tare tanata min hira. Banga gimbiya ba har dare yay muka kwanta, da safe kuma na tashi da shirin fita aiki kamar yanda boss ya tabbatarmin zasu zo ɗaukata, sunata barcinsu nai shirina tsaf, na cika wayata da caji dan haka nai tunin tanan zai kirani, sai dai kusan 7: 00am saiga ɗaya daga cikin bayin gidan tazo isarmin saƙon kira, bin bayanta nai muka fita, mun isa wajen Amintacciyar baiwar gambiya dake falon farko tana jiranmu, na gaisheta da girmamawa saboda babbar mace ce, itama cike da fara'a ta amsa min tana faɗin, “Sarauniyar gagara badau na gaisheki baƙuwar alkairi, baki samu ganinta bane tunda kika iso saboda takawa yana mura, tana sashenshi tun jiya tana bashi kulawa, akwai driver dake tsumayenki a waje ta bada umarnin a kaiki garesa”. Fuskata ɗauke daɗan murmushi nace, “Nagode mama, ALLAH ya bama maimartaba lafiya mai amfani da nisan kwana”. “Amin ya rabbi” ta amsamin damin nuni Abinci da aka ɗora akan babban yire wai na breakfast ɗina, badan nasoba ta tsareni naci sannan tayomin rakkiya waje.
Duk azatona gimba zan tarar, sai dai na iske saɓaninsa, da alama madai wannan acikin masarautar yake shima, dalleliyar mota baƙa wulik yaymin nuni dana shiga bayan mun gaisa, tamkar kazar da ƙwai ya fashema a ciki haka na shiga zuciyata najin tarin ƙaunar waɗanan adalan mutane, ada nazata idan na rasa mafakar gidan Dad bazan sake samun watantaba, sai gashi alkairai nata niye da rayuwata. Tafiya muke ina tunani kala-kala a cikin raina ciki harda fargabar haɗuwata da mutum biyu, wato Boss da Yah Qaseem, tayaya zanyi aiki cikin nutsuwa a tsakkiyar waɗanan zakunan?.
★★★★★
Jay da isowarsa kenan babu daɗewa yana zaune a kujerarsa ta office yana ɗan taɓa aiki da tsumayen su Jabeer, baifi mintuna gomaba suka shigo a jere su huɗu har Rose data dawo jiya, gaisuwa sukai cikin musabaha Rose kuma ta gaishesa kafin duk su zauna, binsu kawai da kallo Jawaad yake. Jabeer ya nuna masa takardar dake hanunsa yana faɗin, “Wannan sune bayanan da Ma'aruff ya kawo yanzun nan”. Jay
A office ɗinsa ya iske Jabeer na jiransa, har wani jiri-jiri yakeji saboda tashin hankali, sai da ya zauna sannan Jabeer yace, “Mike faruwa da gimban?”.
“Jabeer nima ban saniba, ranar juma'a ya tafi weekend amma bai dawoba, shinefa nasa a bisa aga ko yana lafiya, amma sai aka tararma baijeba”.
Cikin ɗaurewar kai Jabeer yace, “Ya salam to ina yaje shiko? Yanzu abinda zamuyi bara mu bibiyi layin sa, ina fata kunyi waya dashi bayan tafiyar tasa?”. Kai kawai Jawaad ya girgizama Jabeer, yana faɗin, “Na kirashi jiya amma bai ɗagaba”. Jabeer yace, “Tunda dai kiran ya shiga zai taimaka mana”. Wayar kawai Jay ya miƙama Jabeer baice komaiba. Gaba ɗaya Jay ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai faman zagaye office ɗin yakeyi, Jabeer kuma nata ƙoƙarin ganin ya samo inda gimban yake, a haka Aliyu da Hafiz suka shigo suka samesa harma da Rose da dawowarta kenan daga tafiya. Haka suka duƙufa su huɗu suna taimakawa Jabeer. Inda alama ke nuna musu wayar gimba na nan ɗinne ya tada musu hankali har suka kasa aminta suketa sake ninƙayar bincike. Cikin girgiza kai Jabeer yace, “Kai abinnan akwai rikitarwa, mizai kaisa wannan dajin mai haɗari? Inaga bara nai magana da kamfanin layinan dan muna buƙatar bayanan da yafi haka”. Hafiz yace, “Hakan shine zai taimaka mana Jabeer, danni kainama ya kulle gaba ɗaya”.
Jawaad dai yama kasa cewa komai, zaune yake kawai tamkar butunbutumi. Aliyu ne yay kiran wanda yake musu aiki a kamfanin layin da gimba ke aiki dashi, bayan sunyi magana ya ajiye wayar Jabeer ya tura musu Number gimba.
Ganin magriba tayi Aliyu yace, “;
Boss ka kwantar da hankalinka, ni ina ganin ko wasune suka Kidnapping ɗinsa bazasu kaisa wannan jajejinba, kawai sunyi hakane domin rikita mana tunani, idan muka kwantar da hankalinmu zamu fahimci komai cikin sauƙi, yanzu dai Ma'aruff ɗin yace daganan zuwa safiya zai turo mana komai, inaga muje muyi salla da addu'ar ALLAH ya kuɓutar dashi a duk inda yake, a kuma hannun duk wanda yake”.
A tare suka amsa da amin har Jawaad.
Koda suka fito daga salla Jawaad ya tafi gidane kawai cike da matsananciyar damuwa, bai shiga gidaba sai da yay sallar isha'i.
A wannan dare idan har akace Jawaad yay barci to ɓarawone, kwana yay miƙama UBANGIJI kukansa akan gimba da murɗaɗɗun al'amuran dake faruwa a tsakaninan, roƙon ALLAH yake ya bashi ƙarfin zuciya dana jajircewa, ya kuma haskaka masa abinda yake a duhu daya gaza fahimta. Mutuwar ɗan-fir'auna, ɓatan gimba, mafarkinsa, dalilin aure da akaso yi tsakanin bilkisu da wanda ba mutumin kirkiba, damuwar da yaga Alhaji babba jiya a ciki. Duk wanda ya roƙa UBANGIJI yana mai ƙasƙantar da kai da fatan samu bai yanke ƙauna daga rahamarsaba ALLAH sai ya amince masa, ya kuma dafama al'amarinsa ta inda bai zato ko tsammani ba.
Jawaad ya tashine da wata irin dakiyar zuciya, duk wani ɗigon tsoro da fargaba daya haifarmasa da ruɗa
ni da kasala a daren jiya sai yaji sun gudu, ya tashi cike da yaƙinin son tunkarar abinda ke tunkarosa. Dolene koda zai halaka da izinin ALLAH sai ya gano suwaye suka kashe ɗan fir'auna, miyasa suka kasheshi?, minene a binne da rayuwarsa da ɗan-fir'auna yaso sanar masa, yanaji a jikinsa kisan ɗan fir'auna nada nasaba da abinda ya shafesa, minene shi? Wannan ne bai saniba.
Ƙarfe bakwai na safe ya gama shirinsa yabar gidan, yau ko gadonsa bai gyaraba, saƙo ya gani daga gimbiya Munaya akan zatasa akai Bilkisu wajen aiki basaima ya wahal da kansaba, idan sun tashi sai ya dinga maidota da kansa.
Yaji daɗin hakan, dan dama yanata juya yanda zai dinga yawonan batare da wataran yay lattiba shiɗinan gwani ayyuka da yawa. Station ya nufa cike da zumuɗin son zuwa yaji ya ake ciki akan gimba.
________________________________
Tunda muka shiga cikin masarauta notin kaina ya nema kwancewa, karon farko a tarihim rayuwata dana fara shigarta, ƴan uwa bansan yanda zan musalta muku abinda na ganiba, abinda kawai zan iya ce muku masarautar gagara badau wani katafaren garine kawai mai zaman kansa dake ɗauke da ɗumbin al'umma kala-kala masu abubuwan kallo. Kaina bai sake kuncewa ba sai da muka shiga sashen da naji ance na sarauniyane mahaifiyar su Amaturrahman, wato garin daɗi na nesa, angulu data leƙa masai. Nidai bana cewa uffan, binsu kawai nake tamkar raƙumi da akala. Mun yada zango a katafaren ɗakin Amaturrahman da Meenal sai Amatullah idan tazo daga Niger. Amaturrahman ce ta tsaya kaina da hidima har saida nai wanka na canja kaya aka kawo abinci ta takurani naci sannan ta barni na huta, muna zaune tana ɗan jana da hira saƙon gimbiya ya iso garemu daga amintacciyar baiwarta akan tace na kwanta na huta, kuma a bani dukkan kulawar data dace.
To lallai naga hidima mai ban mamaki da al'ajabi wadda har kuka sai da nayi, ashe nima mutumce mai daraja irin haka? Ɗawainiyar da akeyi dani ta zabtare kaso mafi yawa na damuwar da nake ciki akan abubuwa kashi-kashi da basu ƙirguwa, tunda Safah kuma taji labarin nazo tadawo ɗakin su Amaturrahman ta tare tanata min hira. Banga gimbiya ba har dare yay muka kwanta, da safe kuma na tashi da shirin fita aiki kamar yanda boss ya tabbatarmin zasu zo ɗaukata, sunata barcinsu nai shirina tsaf, na cika wayata da caji dan haka nai tunin tanan zai kirani, sai dai kusan 7: 00am saiga ɗaya daga cikin bayin gidan tazo isarmin saƙon kira, bin bayanta nai muka fita, mun isa wajen Amintacciyar baiwar gambiya dake falon farko tana jiranmu, na gaisheta da girmamawa saboda babbar mace ce, itama cike da fara'a ta amsa min tana faɗin, “Sarauniyar gagara badau na gaisheki baƙuwar alkairi, baki samu ganinta bane tunda kika iso saboda takawa yana mura, tana sashenshi tun jiya tana bashi kulawa, akwai driver dake tsumayenki a waje ta bada umarnin a kaiki garesa”. Fuskata ɗauke daɗan murmushi nace, “Nagode mama, ALLAH ya bama maimartaba lafiya mai amfani da nisan kwana”. “Amin ya rabbi” ta amsamin damin nuni Abinci da aka ɗora akan babban yire wai na breakfast ɗina, badan nasoba ta tsareni naci sannan tayomin rakkiya waje.
Duk azatona gimba zan tarar, sai dai na iske saɓaninsa, da alama madai wannan acikin masarautar yake shima, dalleliyar mota baƙa wulik yaymin nuni dana shiga bayan mun gaisa, tamkar kazar da ƙwai ya fashema a ciki haka na shiga zuciyata najin tarin ƙaunar waɗanan adalan mutane, ada nazata idan na rasa mafakar gidan Dad bazan sake samun watantaba, sai gashi alkairai nata niye da rayuwata. Tafiya muke ina tunani kala-kala a cikin raina ciki harda fargabar haɗuwata da mutum biyu, wato Boss da Yah Qaseem, tayaya zanyi aiki cikin nutsuwa a tsakkiyar waɗanan zakunan?.
★★★★★
Jay da isowarsa kenan babu daɗewa yana zaune a kujerarsa ta office yana ɗan taɓa aiki da tsumayen su Jabeer, baifi mintuna gomaba suka shigo a jere su huɗu har Rose data dawo jiya, gaisuwa sukai cikin musabaha Rose kuma ta gaishesa kafin duk su zauna, binsu kawai da kallo Jawaad yake. Jabeer ya nuna masa takardar dake hanunsa yana faɗin, “Wannan sune bayanan da Ma'aruff ya kawo yanzun nan”. Jay