← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 168

Sashe 90

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Lokacin da shagali ke gudana a gidan Dad tashin hankali suke fuskanta, dan kuwa dai Salman ne ya gano hotunan biki na yawo a yanar gizo waɗanda ke wajen dinner nata ɗorawa, kunsan mutane da waya a hannu tamkar abu na cizonsune idan suka gani, tun fara dinner ɗin suketa ɗakar hotuna suna ɗorawa wasuma harda videos. Aiko Salman yaci karo da su, shigowa gida yay ya kunna tv dan son ganin wainar da ake toyawa a wajen kasancwwar babu wanda yaje a cikinsu Momy ta hana. Yana zama Aamilah na fitowa, zama tayi suna kallo tare da zagin Bilkisu da Jawaad, hayaniyarsu ta saka Shahudah dake kwance a ɗaki zazzaɓi ya rufe fitowa, aiko tai mummunan gani, dan kuwa dai-dai wajen da Jay ya lashe cake ɗinan daya saka a hancin Bilkisu taci karo dashi, idan ba kallon tsaf kaima wajenba zaka ɗauka kissing ɗin Bilkisu ya keyi. Ƙara kawai ta ƙwalla ta yanke jiki ta faɗi.
Duk kanta sukayi da ihu har Momy Da Dad dake sakkowa daga sama. Girgizawar duniya da sakama Shahudah ruwa taƙi koda motsi, a take hankalinsu ya ƙara kaiwa ƙololuwar tashi suka kwasheta zuwa asibiti likitoci suka rufu a kanta. Har zuwa yanzun dai babu wani bayanin farfaɗowarta kuma.............🤦🏻✍

Duk wanda suka kirani jiya ban ɗagaba suyi haƙuri, ngd sosai kuma da addu'oinku gareni na samu lafiya🤦🏻.

ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🥚 Ƙwai Cikin Ƙaya!🥚

.

Book Two

.

Bilyn Abdull 📚:

Page 39

.................Tsaye kawai Jawaad daya shigo yay yana kallon Bilkisu da keta faman shashashar kuka, ya ɗan sauke ajiyar zuciya yana girgiza kansa. Sai ya tuna da randa aka kai masa Shahudah, cikin kayan barci ya shiga ya sameta zaune hankalinta a kwance tana buga game a waya, amma ita jiba duk da ba daga ainahin iyayenta aka rabotaba ta kasa barin kuka. Idanunsa ya lumshe a hankali da ƙara sauke ajiyar zuciya. Ya cire hular da babbar rigan, daga shi sai wando da ƴar cikin da iyakarta rafin cinyarsa. Ƙarasawa yay gaban gadon ya zauna kusa da ita, dauriya kawai yake dan kansa ciwo yake masa shima, hannunta ya kamo batare da yayi magana ba.

Gaba na ne ya faɗi dan banji motsin shigowar kowa ba, gyalen dana rufe har fuskata da shi nai saurin janyewa dan naji tsoro, ya murza hannuna dake cikin nashi yana faɗin, “Tashi zaune, K baƙya gajiya da kukane?”. Yay maganar da kamoni sosai ya miƙar. Koda na tashi zaunen ban yarda na kallesa ba, ya sake murza hannuna da har yanzu yake a cikin nashin. Idanuna naɗan rumtse ina ƙoƙarin danne abinda nakeji.

Jay dake kallonta ya girgiza kansa kawai tare da kai hannu ya janye gyalen data rufe fuska “Jiba yanda wannan kukan ya saka miki zazzaɓi, amma bazaki tausayima kankiba ki barsa haka, indai danni akeyi a ya isa haka na yafe”. Kamar jira take yay magana wasu hawayen suka sake zubowa sharrr. Kai Jawaad ya dafe kawai yana lumshe ido da sake buɗewa a kanta, shi kukan natama ya fara bashi dariya, sudai mata a duniya suyi kuka shine jin daɗinsu, ya sauke numfashi kaɗan yana ƙoƙarin danne dariyarsa. “Tashi muje kici abinci kisha magani sai mu dawo ki cigaba da kukan kamar ƙyafi samun ruwan hawayen sosai ai”. Mamakin maganarsa yasa na ɗago na kallesa. Yace, “To miye na kallon nawa? Ba daɗi kukan yake miki ba?”. Ɓata fuska nayi nasa hannu na goge hawayen. Bai sake cewa komaiba ya miƙar dani tsaye, kunyace ta kamani nai azamar ɗaukar gyalena daya zame zan maida, amma sai ya riƙe, yana nunamin hanya alamar muje. Cikin rawar murya nai magana a karo na farko tun shigiwarsa, “To ka bani gyalen”. Matsowa yay gab dani sosai, hakan yasa naja baya idanuna na sake tara ƙwalla, Hannuna kawai ya kama batare da ya bani gyalenba bai kuma cemin komaiba muka fito falo.

Dukda kaina a ƙasa yake nasan falon nan ya haɗu, ga wani ƙamshi mai kwantar da zuciya na tashi a cikinsa. Cikin kujera ya zaunar dani shima ya zauna kusa dani, ya buɗe filet ɗin dake akan centre table ɗin falon, ƙamshi mai daɗi ya daki hancina, kajine guda biyu da suka sami gashi mai ƙyau da tsafta. Yace, “Kici abinci kisha magani jikinki yayi zafi da yawa”. “Nifa na ƙoshi”. Na faɗa murya na rawa. Banza yaymin ya ɗebo naman da hannunsa ya kawo min a baki. matsar da fuskata nai ina girgiza kaina da sake faɗin, “ALLAH da gaske nake na ƙoshi”.

Shiru yay na wasu sakanni baice komaiba yana kallona, kafin ya ajiye wanda ya ɗebo ɗin ya matsoni sosai, Hannunsa kawai naji saman haɓata ya ɗago fuskata, muryarsa babu alamar wasa yace, “Iyayi zakimin danma kinga zan baki kazan ƙyauta, ALLAH garama kici da arziƙi, bar ganin period kikeyi inada hanyoyin da zan sakaki kukan da kike sha'awar yi mai dalili, idan kuma kinji ƙarya kar kici na nuna miki ainahin kalata da baki saniba”. Tunda ya fara maganar idona ya cika da ƙwalla, na fara ƙyaƙyƙyaftasu.

Fuska Jawaad ya haɗe sosai, dan ya kula sai ya buɗe mata wuta zasu dai-daita, a ɗan kausashe yace, “Miemaa!”. Da sauri na ɗago na kallesa jin yanda ya kira sunan a daƙile. Ya tsatstsareni da idanunsa dake tattare da ɗumbin gajiya, duk yanda naso janye nawa ya hanani. “Na miki kama da abin wasanki?”. Kaina na girgiza masa da sauri. “Inhar kika bari waɗanan hawayen suka zubo ALLAH saikin gane kurenki”.

“Dan ALLAH kayi haƙuri, wlhy nima bada sona suke zubowa ba, wani irin tsoro nakeji a raina, saina dinga ganin kamar gilmawar inuwa kuma idanuna, sannan a ƙasan zuciyata wani irin zafi nakeji, kamin addu'a a cikin ruwa”. Kafeta yay kawai da idanu na wasu sakanni, ya ɗan ciza leɓensa na ƙasa yana jawota jikinsa ya rungume. “Ki daure kinji, ki dinga ƙarfafa zuciy

arki, insha ALLAHU babu abinda zai faru ALLAH na tare damu da duk al'amuranmu, kefa jarumace na sani, ko kinaso suci galaba a kanki?”. A hankali na girgiza masa kaina hawayen da nake maƙalewa na sauka masa saman ƙirji, nace, “Insha ALLAH zanyi kamar yanda kace”. Yace, “Yauwa my sweet princess, tashi kici abinci ki manta da komai dake zo miki a rai kinji”.

Munkai tsahon mintuna uku a haka kafin ya ɗagoni, addu'ar yaymin a cikin ruwa kamar yanda na buƙata ya bani na sha, a take na fara zufa duk da kuwa falon fanka na aiki, wata nutsuwace ta fara saukarmin a hankali har naji nauyin da kaina yayi ya ragu sosai, sai ajiyar zuciya kawai naketa saukewa. Da kansa ya bani naman, duk da a kunyace nake matuƙa haka na daure naci, sai dai banci da yawaba nace na ƙoshi, amma ƙin saurarena yayi ya cigaba damin ɗurar dole. Daƙyar na samu ya barni, tashi yay babu jimawa ya dawo ɗauke da ɗan box a hannu, ni dai harma na ɗan fara gyangyaɗi dan sosai naji nutsuwa a daga ruɗanin dana fara shiga ɗazun, dama ga yunwa kuma. magani ya bani na sha.

“Tashi kije ki kwanta dare na sake yi”. Kaina dake a ƙasa na ɗaga masa na miƙe, rashin gyalenan a jiki duk jina nake a matuƙar takure.

Jay ya bita da kallo harta shige, ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana jingina da kujerar tare da lumshe idanunsa, tausayi take bashi sosai, kallo ɗaya zakai mata ka fahimci tanada damuwa sosai, yasan zafin rashin iyaye, dan haka yake tausayin duk wanda bai dasu, balle mace ma mai rauni irinta dake zagaye da ruɓaɓɓun dangi gaba ɗaya, garashi dangin uwa na ɗauke masa kewa da damuwa ma. Yanzukam ya samu kwanciyar hankali duk wani motsinta zai kasance a kan idanunsa, a yanzune zai binciko abinda ke binne da iznin ALLAH.

Da wannan tunanin ya tashi ya shiga ɗakinsa, wanka yayi da ruwa mai zafi yay shafa'i da wutiri, maganin shima yasha dan kansa ciwo yake masa sosai dauriya kawai yakeyi.

★★★★★★

Kasancewar maganin da ya bata harda na barci tuni barcin yay awan gaba da ita, kayantane a jikinta bata canjaba, hakan ya saka Jawaad daya shigo tsura mata idanu, komanta ya ƙara canjawa, musamman ma fatarta tai wani irin gogewa sai ƙyalli takeyi, a fuskarta kawai zaka karanci bata da son hayaniya, komai nata tsaka tsakine, hakan yasa ƙyawunta ya kasance mai sanyi, a kallo ɗaya bazaka taɓa ganin sirrin ƙyawunta ba dan batada cika ido irin na Shahudah, yanda take nutsatstsiya haka ƙyawuntama a hankali yake bayyana ga mai kallonta. Tanada kwarjini da cikar haiba na isassun mata masu kamun kai. Yaɗan lumshe ido ya sake buɗewa a kanta, a fili ya furta, ‘Sai jan ajin tsiya da miskilanci ga tsoro kuma ba’. Yay maganar yana nufar akwatinta da aka jiye alamar kayantane a ciki, buɗewa yay, a sama yaci karo da kayan barci har kala uku, doguwar riga da bazata wuce rabin cinyaba, sai riga da wando kala biyu. Riga da wandon ya ɗauka dan sun ɗanfi kauri da mutunci, yasan dai saka matasu akayi daga gani. Zama yay bakin gadon kusa da ita, ya janye bargon data rufama ƙafafunta zuwa ƙugu, zif ɗin rigar ya janye ƙasa bayan ya zame ɗan kwalinta gashinta da yasha gyara yanata ƙamshi ya bayyana.

Cikin barci naji ana ƙoƙarin ciremin kaya, da ƙyar na buɗe idanuna sai naci karo da shi, ai babu shiri na miƙe zaune duk da jikina babu wani ƙarfi, na dafe rigar da har ya ciren hannu guda batare da na yarda mun haɗa ido ba.

Kayan daya ɗakko mata ya ajiye saman cinyarta yana miƙewa, “Ki canja waɗanan kayan dan zasu takuraki sunyi nauyi da kwanciya barci”.

Da kallo kawai na iya bin bayansa ina haɗiye tsoron da saura kaɗan ya hudan zuciya, gaba ɗaya mamaki al'amarinsa ke bani, wai dama haka yake boss ɗinan ashe, yanzu daban farkaba nufinsa shine zai sauyan kayan? Tabɗi wlhy daya gama dani kuwa. Saida yaje ƙofa zai fita sannan ya juyo yana kallona, “Idan kika bari mintunan dana ɗiba miki ya cika baki tashi kin sauya kayan nanba, hummm..” yay maganar murya ƙasa-ƙasa amma daɗan karsashi sannan ya fice.
Chapter 90 · 0% Book details