Sashe 111
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina zaune a sofa ɗin dake ɗakin ina duba abinda su Ummah suka kawomin ya shigo, ban yarda mun haɗa idoba nace, “Yayanmu kaga abinda su Ummah suka kawomin”. Muryarsa a sanyaye yace, “Kin gode, ALLAH ya saka da alkairi”. Ɗagowa nai naɗan kallesa na janye idanuna. “Baka da lafiya ne?”. “Mi kika gani?” ya faɗa yana ɗaukar agogonsa dake kan mirror na. “Naji muryarka a sanyaye ne”.
Murmusa yayi ya miƙomin hannun da zaisa agogon, babu musu na fara ɗaura masa. Harma na fidda rai ga samun amsa nikam, sai da na kammala ɗaura masanne ya ranƙwafo tare da sumbatar laɓɓana, cikin ƙaramin sauti yace, “Bazaki ganeba Miemaa”. Idanuna na ɗago na kallesa, ya ɗagemin gira ɗaya yana cije leɓensa na ƙasa. “Kimin addu'a zan fita”. Duk da banason fitar haka na daure nai masa fatan alkairi da dawowa lafiya, sake ranƙwafowa yay ya sumbaci laɓɓana da cewa “Amin” sannan ya fice.
Na sauke ajiyar zuciya da tattare kayan na maidasu inda suke sannan na miƙe, gidan duk sai yamin babu daɗi, dan haka na saka silifas tare da hijjab na fito harabar gidan dan inɗan rage kaɗaici, na ɗan zazzagaya ina tsinkar flowers ɗin da aka ƙawata gidan dasu masu ƙamshi, sai gab da magriba na shige ciki, falonsa na nufa kai tsaye domin tunawa da kofunan dasu Ummah sukasha lemo ban kwasosu ba, na gama tattarewa zan fito idona ya sauka akan file daya ajiye a kan hannun kujera, ajiye kofunan nai na ɗaukesa da nufin kaimasa ɗaki dan nasan mantashi yay anan. Takardun dake ciki suka zubo ƙasa a mistake, ‘Ya salam’ na faɗa ina duƙawa na tattaro su, ido na tsirama ɗaya daga cikin takardar domin ganin sunan Dad ɓaro-ɓaro, mamaki yay matuƙar kamani, na koma na zauna a kujera ina dubawa daki-daki. Kai nane ya nema kullewa, daga gefe kuma zuciyata najin wani irin takaicinsa, waishi mutumin nan mi ya ke nufi da ƴan gidanmu ne? Na kula gaba ɗaya bayanan dake a file ɗin akan ƴan gidanne, sunan Dad, mom da yah Qaseem yafi na kowa fitowa ma, maidawa nai na dangwarar da file ɗin na ɗauka kofinan na fita ina ƙunƙuni, ko wankesu ban tsaya yiba na ajiyesu a kicin ɗin na fito. Ɗakina na shiga raina duk babu daɗi, Dad ya wuce duk yanda yake zato a gareni daga shi har zuri'arsa baki ɗaya, Dad yaymin abinda sauran dangina suka gaza yimin, Dad ya tallafi maraicina a lokacin da rayuwata ke walagigin ƙila wakala, ta sanadin gatan da Dad yay minne har shiɗin ya sameni ya aura, lokaci yayi da yakamata nasan komai dangane da aurenmu da shi da yanda akai na koma hannunsa ba Yah Qaseem ba, inason sanin ina Yah Qaseem yake ne shin? Miya faru ne ranar ɗaurin aurenmu har aka ɗauramin aure da boss?’. da wannan tunane-tunanen na shiga bayi, wanka nayo da alwala raina duk a dagule, na shafa mai sama-sama tare da zira siket da riga marasa nauyi a jikina waɗanda sam basu kamamin jiki ba. Hoda naɗan shafa kaɗan da lipsgloss na saka turare sannan na tada salla, bayan an idar ban tashi daga saman abin sallar ba na ɗauka Al-Qurani nahau karatu, har saida aka kira sallar isha'i sannan na tashi nayi har shafa'i da wutiri dan yanda nakejin idanuna na bauri nasan kwanciyar wuri zanyi yau.
Koda na fito saina shiga k
icin na ɗauraye kofunan sannan nai zaman gyara masa fruit duk da raina a dagule yake, na shirya tambayoyi fal ina jiran ya dawo na shiga yi masa su. Nayi nisa a tunani har bansan ya shigo kicin ɗinba, ƙamshinsa da alamar mutum da najine ya sakani ɗagowa da sauri. Ajiyar zuciya naɗan sauke dan baƙaramin tsorata naiba da farko, nace, “Ni ALLAH kaban tsoro”.
“Ai ke komai abin tsorone a wajenki daman” ya faɗa yana juyawa ya fita a kicin ɗin. Ɓata fuska nayi na cigaba da aikina, sai da na kammala tsaf na ɗoro akan tray tare da ruwa da lemo sannan na fito. Ganin baya babban falo saina nufi parlorn sa. Nanma baya nan, na ajiye tray ɗin na nema waje na zauna jiransa ya fito danna amayar da abinda ke a raina, duk da tsoron da nakeji kuwa. Kusan zaman mintuna talatin nayi sannan ya fito, ya canja kayansa zuwa wando da riga farare tas masu taushi alamar yayi wanka. Yanda ya kalleni na kula baiyi tunanin ganina a nanba, amma sai ya basar ya zauna yana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya kamar wani saraki. “Bani remote ɗin can”. Miƙewa nai na ɗakko masa. Inata dai danne abinda ke raina dan son yin koyi da nasiha da dabarun da Umm-Anum ta koyamin. Sai da ya kunna television ɗin sannan yace, “Sun wuce”.
Kallonsa nayi nace, “Su wanene?”. Kamar bazai tankaba ya maida hankalinsa ga labaran, harma na fidda rai sai naji yace, “Daga masarauta nake”. Duk da na fahimci waɗanda yake nufin sai nace, “Wai kana nufin su Anuwar?”. Kansa kawai ya ɗagamin. Na fahimci ransa a jagule yake, amma duk da haka banji zan iya haƙuri ban masa maganar su Dad ba. Ruwan dana tsiyaya na miƙa masa, ya amsa tare da haɗewa da hannuna, ɗagowa nai mukaima juna kallon ido cikin ido, murya a sanyaye yace, “Jibi idan ALLAH ya kaimu zan wuce saudia”. “Nidai dan ALLAH mu tafi tare, kuma ma ai ni ta sani ba kaiba”. Karon farko datun shigowarsa naga yayi fra'a, ya ɗan murmusa da zare kofin daga hannuna ya kai bakinsa, sai da yasha ruwan sosai ya ajiye kofin sannan ya sake dubana, “Kinada kuɗin jirgine?”. Da sauri nace, “Eh” cikin karsashi da ƙarfin gwiwa. Yace, “Yayi ƙyau hajjaju”. Yay maganar da buɗe plate ɗin dana rufe fruit dana yayyanko a cikin bowl ɗin glass. Cokali mai yatsu dana haɗo da shi ya ɗauka ya fara sha hankalin kwance kamar nace nasane🙄😒.
Shiru falon yayi sai tv daketa subaɗi, saida ya sha kusan quarter sannan ya juyo ya kalleni, “Zo nan naji mike damunki ne?”. Mamaki ya kamani, ya akai ya fahimta? Saurin gyara yanayina nai da cewa, “Babu abinda ke damuna sai barci”. yaɗan tsuramin idanu sannan ya janye, “Tunda yau na fara saninki ko?. Taso nace”. Tashi nai zuwa inda yake ina kumbura fuska, ya fisgoni da ƙarfi na faɗa saman cinyarsa, ƴar ƙara na saki wadda ni kaina nasan ta shagwaɓace, “Shiiii” ya faɗa yana saka kankana a baki, bakinsa ya ɗora kan nawa ya sakamin kankanar dake bakin nasa cikin nawa. Na yamutse fuska kaɗan a raina ina faɗin ‘ƙazanta’. Ɗallar bakina da yay ya sakani sake ɓata fuska dan naji zafi, ya ɗage gira ɗaya da faɗin, “Nasan ai gulmata kikai a zuciyarki”. Saida na shanye sannan nace, “Nidai nasan banyiba ai”. Bai tanka minba ya cigaba da bani fruit ɗin shima yana sha, saida nace masa na ƙoshi sannan ya barni. Zameni yay na kwanta a kujerar kaina na saman cinyarsa, wannan damar dana samuce ta bani damar faɗin, “boss wai dan ALLAH wane laifi Dad yay makane?”. Kallona yay cikin ido ya watsar, ya maidama hankakinsa ga kallon labaransa hankali kwance. Iya kaiwa ƙarshe nakai da haushi, hakan yasa na sake maimaita tambayar kozai fusata ya bani amsa, amma nanma saiya shareni, aifa nakai ƙarshen harzuƙa, na fashe masa da kuka, “Wai miye laifin Dad ne da Yah Qaseem a gareka? Bayan tarin ƙauna da kulawa da suka nuna maka dagasu har Momy, ƴa fa suka ɗauka sukutum suka baka ka aura, basu ji komaiba suka sake bakani duk da kuwa ɗansu jininsune ya dace na aura, sannan ƴarsu da ke tsananin sonka ya dace ka aura kaima, boss bai kamata ace ka maida alkairi ta wannan sigarba, suɗin ƴan uwanane fa waɗanda sukaimin gatan da kowa ya gaza yimin, sune suka maidani mutum harna zama abin sha'awa ga irink.......” ruf ya rufemin baki da nashi, ya ɗagan
i cak batare daya sakimin bakiba yay bedroom dani, duk ƙoƙarin son ƙwacewar da nake ko gezau baiyi ba, dama ya kashe fitilar ɗakin sai na gefen gado kawai, dan haka sai kawai jina nai bisa gado, babu wani ɓata lokaci ya shiga juyani da zafi-zafi yanda yake so, gashi ya hana bakina damar neman ɗauki, yanda yake bi danine ya tadamin hankali, dan sam babu wani bi a hankali kamar ranar, sai dai kuma hakan bai hanashi kasancewa cikin nutsuwaba da min abinda zai gusarmin da hankali. Idan nace muku na gurzu fiye da ranar farko to ku ɗauka gurzuwa nai irin ta ƙarshen nan da faɗarta kawai takai a tausayamin, dan al'amarin ya zama kamar famine daga baƙar azabar dana sha a daren shekaranjiya. Muryata harta dasashe saboda kuka, ya kuma ƙi lallashina kosau ɗaya.
Kamar ranar yauma shine ya taimakamin na gyara jikina, ya kuma sakani a ruwan zafi sosai sannan ya maidoni saman gadon ya kwantar batare da yace dani uffan ba, yamayi tamkar baijin kukan nawa, komawa yay bayin yaje yayo wanka shima, har lokacin ina shashshekar kuka na, muryarsa a dadushe kamar mai mura yace, “ALLAH idan bakimin shiruba na hawo gadon nan saina sake banbance miki aya da tsakkuwa, daga yau kuma dan ALLAH ki sake ahiga abinda babu ruwanki kinji ko”. Yana gama faɗa ya ficewarsa a ɗakin.
Kukan na sake fashewa dashi ina danna kaina cikin filos dan karya ji, kusan mintuna goma da fitarsa naji ya dawo ɗakin, haɗiye kukan nayi na koma sauke ajiyar zuciya, bai tankaminba naji dai yanata kai kawonsa har na wasu mintuna kafin ya hawo gadon. A jikinsa ya sakani ya rungume batare da yace ƙala ba, mintuna kaɗan barci yay gaba dashi bayan yaymana addu'a, nima ajiyar zuciyata na cigaba da saukewa har barcin yay awon gaba dani.
★★★★★
Murmusa yayi ya miƙomin hannun da zaisa agogon, babu musu na fara ɗaura masa. Harma na fidda rai ga samun amsa nikam, sai da na kammala ɗaura masanne ya ranƙwafo tare da sumbatar laɓɓana, cikin ƙaramin sauti yace, “Bazaki ganeba Miemaa”. Idanuna na ɗago na kallesa, ya ɗagemin gira ɗaya yana cije leɓensa na ƙasa. “Kimin addu'a zan fita”. Duk da banason fitar haka na daure nai masa fatan alkairi da dawowa lafiya, sake ranƙwafowa yay ya sumbaci laɓɓana da cewa “Amin” sannan ya fice.
Na sauke ajiyar zuciya da tattare kayan na maidasu inda suke sannan na miƙe, gidan duk sai yamin babu daɗi, dan haka na saka silifas tare da hijjab na fito harabar gidan dan inɗan rage kaɗaici, na ɗan zazzagaya ina tsinkar flowers ɗin da aka ƙawata gidan dasu masu ƙamshi, sai gab da magriba na shige ciki, falonsa na nufa kai tsaye domin tunawa da kofunan dasu Ummah sukasha lemo ban kwasosu ba, na gama tattarewa zan fito idona ya sauka akan file daya ajiye a kan hannun kujera, ajiye kofunan nai na ɗaukesa da nufin kaimasa ɗaki dan nasan mantashi yay anan. Takardun dake ciki suka zubo ƙasa a mistake, ‘Ya salam’ na faɗa ina duƙawa na tattaro su, ido na tsirama ɗaya daga cikin takardar domin ganin sunan Dad ɓaro-ɓaro, mamaki yay matuƙar kamani, na koma na zauna a kujera ina dubawa daki-daki. Kai nane ya nema kullewa, daga gefe kuma zuciyata najin wani irin takaicinsa, waishi mutumin nan mi ya ke nufi da ƴan gidanmu ne? Na kula gaba ɗaya bayanan dake a file ɗin akan ƴan gidanne, sunan Dad, mom da yah Qaseem yafi na kowa fitowa ma, maidawa nai na dangwarar da file ɗin na ɗauka kofinan na fita ina ƙunƙuni, ko wankesu ban tsaya yiba na ajiyesu a kicin ɗin na fito. Ɗakina na shiga raina duk babu daɗi, Dad ya wuce duk yanda yake zato a gareni daga shi har zuri'arsa baki ɗaya, Dad yaymin abinda sauran dangina suka gaza yimin, Dad ya tallafi maraicina a lokacin da rayuwata ke walagigin ƙila wakala, ta sanadin gatan da Dad yay minne har shiɗin ya sameni ya aura, lokaci yayi da yakamata nasan komai dangane da aurenmu da shi da yanda akai na koma hannunsa ba Yah Qaseem ba, inason sanin ina Yah Qaseem yake ne shin? Miya faru ne ranar ɗaurin aurenmu har aka ɗauramin aure da boss?’. da wannan tunane-tunanen na shiga bayi, wanka nayo da alwala raina duk a dagule, na shafa mai sama-sama tare da zira siket da riga marasa nauyi a jikina waɗanda sam basu kamamin jiki ba. Hoda naɗan shafa kaɗan da lipsgloss na saka turare sannan na tada salla, bayan an idar ban tashi daga saman abin sallar ba na ɗauka Al-Qurani nahau karatu, har saida aka kira sallar isha'i sannan na tashi nayi har shafa'i da wutiri dan yanda nakejin idanuna na bauri nasan kwanciyar wuri zanyi yau.
Koda na fito saina shiga k
icin na ɗauraye kofunan sannan nai zaman gyara masa fruit duk da raina a dagule yake, na shirya tambayoyi fal ina jiran ya dawo na shiga yi masa su. Nayi nisa a tunani har bansan ya shigo kicin ɗinba, ƙamshinsa da alamar mutum da najine ya sakani ɗagowa da sauri. Ajiyar zuciya naɗan sauke dan baƙaramin tsorata naiba da farko, nace, “Ni ALLAH kaban tsoro”.
“Ai ke komai abin tsorone a wajenki daman” ya faɗa yana juyawa ya fita a kicin ɗin. Ɓata fuska nayi na cigaba da aikina, sai da na kammala tsaf na ɗoro akan tray tare da ruwa da lemo sannan na fito. Ganin baya babban falo saina nufi parlorn sa. Nanma baya nan, na ajiye tray ɗin na nema waje na zauna jiransa ya fito danna amayar da abinda ke a raina, duk da tsoron da nakeji kuwa. Kusan zaman mintuna talatin nayi sannan ya fito, ya canja kayansa zuwa wando da riga farare tas masu taushi alamar yayi wanka. Yanda ya kalleni na kula baiyi tunanin ganina a nanba, amma sai ya basar ya zauna yana ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya kamar wani saraki. “Bani remote ɗin can”. Miƙewa nai na ɗakko masa. Inata dai danne abinda ke raina dan son yin koyi da nasiha da dabarun da Umm-Anum ta koyamin. Sai da ya kunna television ɗin sannan yace, “Sun wuce”.
Kallonsa nayi nace, “Su wanene?”. Kamar bazai tankaba ya maida hankalinsa ga labaran, harma na fidda rai sai naji yace, “Daga masarauta nake”. Duk da na fahimci waɗanda yake nufin sai nace, “Wai kana nufin su Anuwar?”. Kansa kawai ya ɗagamin. Na fahimci ransa a jagule yake, amma duk da haka banji zan iya haƙuri ban masa maganar su Dad ba. Ruwan dana tsiyaya na miƙa masa, ya amsa tare da haɗewa da hannuna, ɗagowa nai mukaima juna kallon ido cikin ido, murya a sanyaye yace, “Jibi idan ALLAH ya kaimu zan wuce saudia”. “Nidai dan ALLAH mu tafi tare, kuma ma ai ni ta sani ba kaiba”. Karon farko datun shigowarsa naga yayi fra'a, ya ɗan murmusa da zare kofin daga hannuna ya kai bakinsa, sai da yasha ruwan sosai ya ajiye kofin sannan ya sake dubana, “Kinada kuɗin jirgine?”. Da sauri nace, “Eh” cikin karsashi da ƙarfin gwiwa. Yace, “Yayi ƙyau hajjaju”. Yay maganar da buɗe plate ɗin dana rufe fruit dana yayyanko a cikin bowl ɗin glass. Cokali mai yatsu dana haɗo da shi ya ɗauka ya fara sha hankalin kwance kamar nace nasane🙄😒.
Shiru falon yayi sai tv daketa subaɗi, saida ya sha kusan quarter sannan ya juyo ya kalleni, “Zo nan naji mike damunki ne?”. Mamaki ya kamani, ya akai ya fahimta? Saurin gyara yanayina nai da cewa, “Babu abinda ke damuna sai barci”. yaɗan tsuramin idanu sannan ya janye, “Tunda yau na fara saninki ko?. Taso nace”. Tashi nai zuwa inda yake ina kumbura fuska, ya fisgoni da ƙarfi na faɗa saman cinyarsa, ƴar ƙara na saki wadda ni kaina nasan ta shagwaɓace, “Shiiii” ya faɗa yana saka kankana a baki, bakinsa ya ɗora kan nawa ya sakamin kankanar dake bakin nasa cikin nawa. Na yamutse fuska kaɗan a raina ina faɗin ‘ƙazanta’. Ɗallar bakina da yay ya sakani sake ɓata fuska dan naji zafi, ya ɗage gira ɗaya da faɗin, “Nasan ai gulmata kikai a zuciyarki”. Saida na shanye sannan nace, “Nidai nasan banyiba ai”. Bai tanka minba ya cigaba da bani fruit ɗin shima yana sha, saida nace masa na ƙoshi sannan ya barni. Zameni yay na kwanta a kujerar kaina na saman cinyarsa, wannan damar dana samuce ta bani damar faɗin, “boss wai dan ALLAH wane laifi Dad yay makane?”. Kallona yay cikin ido ya watsar, ya maidama hankakinsa ga kallon labaransa hankali kwance. Iya kaiwa ƙarshe nakai da haushi, hakan yasa na sake maimaita tambayar kozai fusata ya bani amsa, amma nanma saiya shareni, aifa nakai ƙarshen harzuƙa, na fashe masa da kuka, “Wai miye laifin Dad ne da Yah Qaseem a gareka? Bayan tarin ƙauna da kulawa da suka nuna maka dagasu har Momy, ƴa fa suka ɗauka sukutum suka baka ka aura, basu ji komaiba suka sake bakani duk da kuwa ɗansu jininsune ya dace na aura, sannan ƴarsu da ke tsananin sonka ya dace ka aura kaima, boss bai kamata ace ka maida alkairi ta wannan sigarba, suɗin ƴan uwanane fa waɗanda sukaimin gatan da kowa ya gaza yimin, sune suka maidani mutum harna zama abin sha'awa ga irink.......” ruf ya rufemin baki da nashi, ya ɗagan
i cak batare daya sakimin bakiba yay bedroom dani, duk ƙoƙarin son ƙwacewar da nake ko gezau baiyi ba, dama ya kashe fitilar ɗakin sai na gefen gado kawai, dan haka sai kawai jina nai bisa gado, babu wani ɓata lokaci ya shiga juyani da zafi-zafi yanda yake so, gashi ya hana bakina damar neman ɗauki, yanda yake bi danine ya tadamin hankali, dan sam babu wani bi a hankali kamar ranar, sai dai kuma hakan bai hanashi kasancewa cikin nutsuwaba da min abinda zai gusarmin da hankali. Idan nace muku na gurzu fiye da ranar farko to ku ɗauka gurzuwa nai irin ta ƙarshen nan da faɗarta kawai takai a tausayamin, dan al'amarin ya zama kamar famine daga baƙar azabar dana sha a daren shekaranjiya. Muryata harta dasashe saboda kuka, ya kuma ƙi lallashina kosau ɗaya.
Kamar ranar yauma shine ya taimakamin na gyara jikina, ya kuma sakani a ruwan zafi sosai sannan ya maidoni saman gadon ya kwantar batare da yace dani uffan ba, yamayi tamkar baijin kukan nawa, komawa yay bayin yaje yayo wanka shima, har lokacin ina shashshekar kuka na, muryarsa a dadushe kamar mai mura yace, “ALLAH idan bakimin shiruba na hawo gadon nan saina sake banbance miki aya da tsakkuwa, daga yau kuma dan ALLAH ki sake ahiga abinda babu ruwanki kinji ko”. Yana gama faɗa ya ficewarsa a ɗakin.
Kukan na sake fashewa dashi ina danna kaina cikin filos dan karya ji, kusan mintuna goma da fitarsa naji ya dawo ɗakin, haɗiye kukan nayi na koma sauke ajiyar zuciya, bai tankaminba naji dai yanata kai kawonsa har na wasu mintuna kafin ya hawo gadon. A jikinsa ya sakani ya rungume batare da yace ƙala ba, mintuna kaɗan barci yay gaba dashi bayan yaymana addu'a, nima ajiyar zuciyata na cigaba da saukewa har barcin yay awon gaba dani.
★★★★★