Sashe 138
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Wayar da bily ta samu Jay nayi a mota wayace daga Qaseem dake a General hospital a killace, ya buƙaci ganin Jay ɗin da gaggawa, duk da hakan ya bama Jay mamaki baiyi ƙasa a gwiwa ba wajen amsawa, shiyyasa suka ajiye Bilkisu a gida ita. Barrack suka fara zuwa wajen baba ƙaura da shima tun a safiyar yau ya saka aka kirashi a waya akan yana buƙatar ganinsa. yaso suje tare da bily ne dama, to sai kuma kiran da Qaseem yay masa ya shafe hakan. Kusan mintuna talatin ya ɗauka anan sannan suka fito.
Likitoci basu bari Jawaad ya shiga wajen Qaseem ba kai tsaye sai da matakan tsaro na kare kai, ko ina na jikinsa sai da ya kasance a rufe ruf sannan aka kaisa inda Qaseem ya ke. Wajene na musamman.......
Babu wanda yasan mi suka tattauna har na tsahon mintuna hamsin da uku sannan Jay ya fito, baka isa fahintar yanayinsa ba, dan kamilar fuskarsa ta shanye komai, sai dai kumafa jijiyar kansa tai masifar miƙewa ruɗu-ruɗu, hakama idanunsa jazur suke. Sadiq da tun da ya dawo yana zaune yana jiransa ya miƙe da sauri ya buɗe masa mota ya shiga, yana zama wayarsa nayin ring, daba dan yasan kirane mai muhimmanci ba bazai ɗaga ba, yay ƙoƙarin saisaita muryarsa suka gaisa da gambiya Munaya. Bansan mi tace masa daga canba, ya ɗan dai murmusa yana gyara zamansa da ƙyau. “Ina sake roƙon alfarma dai Ummu, Please a bani ƴar damarnan nima koda sau ɗaya ne”. Idanu ya lumshe a hankali yana cigaba da saurarenta, ya sauke ajiyar zuciya yana jinjina kansa kamar yana a gabanta, saida yay mata godiya sannan ya sauke wayar daga kunnensa yana cika bakinsa da iska ya fesar.
Muna zaune a falo ni da Nabeelah ya shigo, sannu Nabeelah ta shiga jera masa, bai amsa mataba, sai dai ya ɗaga mata hannu kawai ya wuce abinsa. Da kallo muka bisa da gani har ita, na lumshe idanu da kwanciya jikin kujera ina sauke numfashi. “Shi dai Yayanmu kamar mai jinnu haka yake, yanzu zaki gansa a mutum anjima kaɗan ya koma dodo”. Nabeelah ce da wannan maganar cikin shagwaɓa, Bance da ita komaiba na miƙe, ruwa na ɗauka da kofi nabi bayansa.
Ban samesa a faloba, hakan ya sakani binsa bedroom. A gaban mirror na iskesa yana waya da cire boturan shirt ɗinsa, ido muka haɗa ta cikin mirror'n kasancewar a bayansa na tsaya daf. Ni na fara janyewa, dan nikam banason ganinsa a cikin yanayin nan tsoro nakeji, cigaba yay da yin wayarsa tamkarma bai ganni ba. duk da hakan ya sosamin rai sai na nutsu ina saurarensa, mamaki ya kamani sosai dan fahimtar wayar yana yinta ne akan Aunty Shahudah, cikin tsoro-tsoro nake kallonsa lokacin daya ajiye wayar. “Boss wai kana nufin kasan inda aunty Shahudah take dama kenan?”. Rigarsa da ya gama cirewa ya jefa saman sofa, ya fara ƙoƙarin zare belt ɗin wandonsa batare da ya kalli sashenma da nakeba balle nai tunanin samun amsa. Sai da ya gama zame komai daga shi sai boxer sannan ya raɓani ya wuce abinsa. A take jikina ya fara rawa, na shiga ambaton innalillahi..... Ina kafe ƙofar bayin da kallo kamar zai fitone ya bani amsar da nake buƙata. Bansan sanda na zube a bakin gadonba na dafe kai, ts
ahon mintuna ina a haka wayarsa kuma nata faman ring a gefena amma banko kalleta ba. A haka ya fito ya sameni, yanzun ma dai ban ishesa kalloba, ya shirya a gaggauce cikin ƙananun kaya farin wando da farar riga, sai ya ɗaura baƙar jacket a sama mara hannu. Koba'a faɗaba yayi ƙyau sosai, dan shi mutum ne da koyaya ya saka sutura sai kaga ta zauna masa a jiki tsaf tamjar danshi akai. Tsabar wulaƙanci a gabana ya sake ficewa a ɗakin bayan ya zauna ya saka takalma a ƙafarsa, bansan sanda na fashe da kuka ba nai baya a saman gadon.
Gudu sosai Jawaad ya saka Sadiq shararawa dan jirgin su Umm-Anum harya sauka bisa ƙasa, duk da gimbiya ta sanar masa Takawa ya aika motocin da zasu tarosu hakan bai hanashi jin ɗokin son zuwa ya tarbo mahaifiyarsa da kansa ba, shi kaɗai yasan a yanayin da wannan ranar tazo masa, tazo masa da abubuwa kashi-kashi masu yawa, ruɗani daban al'ajabi da matsanancin farincikin dawowar mahaifiyarsa duniyarsa cikin ƙasar haihuwarta.
Suna isowa su Umm-Anum na fitowa a jirgi Anuwar riƙe da hannunta. Da gudu Anum ta ƙaraso gaban Jay da tun tana sakkowa ta hangosa, jikinsa ta faɗa ta rungumesa. Duk da damuwar da yake ciki da yanayinsa na rashin son shiga harkar yara bai gaza karɓar ƴar ƙanwar tasaba kamar yanda taso, ya shafa kanta yana ɗan murmushi kafin ya janyeta a jikinsa ya nufi Umm-Anum. Haɗata yay ita da Anuwar ɗin ya rungumesu gaba ɗa yana maijin a yau babu tamkarsa duk faɗin duniyar nan. Kasan cewar yasan umm-Anum na fama da matsalar kafa bai tsaya ɓata lokaciba suka nufi inda Sadiq ya faka motarsa kusa da motocin masarauta guda uku da sukazo tarbarsu. “Ummuna Abbu fa?”. “Sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zasu taho suma insha ALLAHU, nima dan bazan iya haƙurin kaiwa goben bane shiyyasa”. Murmushi ya saki mai sanyi yana taimaka mata ta shiga motarsa da Sadig ya buɗe. Anuwar da Anum kuma suka shiga motar masarauta ɗaya badan sun so hakanba.
Sai da ya tabbatar komai yayi dai-dai sannan ya zagaya inda Sadiq ya buɗe masa kusa da Umm-Anum shima ya shiga, ya riƙo hannunta ya sumbata, “Amsiyatul sa'iidah. Marhaban biki Ummuna”. Fuskarta ɗauke da murmushi da hawaye tace, “N: Kaifa anta Jay-p na”. Idanu ya lumshe a hankali yana haɗiye nauyin da ƙirjinsa yay masa da sake damƙe hannunta cikin nashi kamar mai gudun a ƙwace masa ita yace, “Ana bikhairin Ummuna”. Ta shafa kansa tana murmushi da faɗin, “Alhamdulillahi ala kulli halin Noorul Ayn”. Ɗagowa yay idanu jazur ya kalleta da sake sumbar hannunta ya ɗaura kansa saman kafadanrta yana sake lumshe idanu. “Ummuna nayi kewarki”. “Nima haka Muhammad Jawaad”. Ta faɗa tana sumbatar goshinsa.
Cikin nutsuwa motocin suka fice daga airport ɗin, ta Jay ce gaba shi da Umm-Anum, sai kuma wadda su Anuwar ke ciki shi da Anum, sai ɗaya da babu kowa a ciki, ta ƙarshe kuma dogaraine.
___________________
Daga kukan da ya barni inayi sai barci ya kwasheni, cikin barci naji ana knocking ƙofar, na buɗe ido a hankali da tashi zaune dan nasan bazai wuci Nabeelah bace, bayi na fara shiga na wanko fuskata da hawaye suka bushe, sannan na fita. Nabeelah tai saurin riƙo hannuna tana faɗin, “Baƙinfa sun iso inaga, dan naji ƙarar buɗe gate”. Bata jira amsata ba taja hannuna muka fito babban falo. Kiciɓis mukai da Anum data fara shigowa. Ta daka wani uban tsalle ta ɗareni, tuni naji duk wani ɓacin ran da Boss ya barni da shi ya gudu, na rungumeta nima cike da tsantsar farin ciki.
Anuwar ne na biyun shigowa, ya fara sauke idanunsa akan Nabeelah da ke tsaye tana kallon su bily da dariya, kafin ya maida ga su Bilkisun yana ɗan ɓata fuska. “Lallaima Aunty, ni baki ganniba sai wannan yarinyar”. “Tuba nake Yah Anuwar ” na faɗa ina sakin Anum.
A waje kam Jay ya taimakama Umm-Anum ta fito daga motar, ƙafafunta duk sunyi fushi saboda zaman jirgi, ga kuma dama ƙafarta na mata ciwo. Wani irin kallo take bin gidan da shi dan bazata taɓa mantawa da shi ba koda a magagin mutuwa take, gidan da yazama tushen komai na maida mijinta wane, gidan da yazama harsashin ginin ɗaukaka ga abin sonta, gidan da zata iya a
Likitoci basu bari Jawaad ya shiga wajen Qaseem ba kai tsaye sai da matakan tsaro na kare kai, ko ina na jikinsa sai da ya kasance a rufe ruf sannan aka kaisa inda Qaseem ya ke. Wajene na musamman.......
Babu wanda yasan mi suka tattauna har na tsahon mintuna hamsin da uku sannan Jay ya fito, baka isa fahintar yanayinsa ba, dan kamilar fuskarsa ta shanye komai, sai dai kumafa jijiyar kansa tai masifar miƙewa ruɗu-ruɗu, hakama idanunsa jazur suke. Sadiq da tun da ya dawo yana zaune yana jiransa ya miƙe da sauri ya buɗe masa mota ya shiga, yana zama wayarsa nayin ring, daba dan yasan kirane mai muhimmanci ba bazai ɗaga ba, yay ƙoƙarin saisaita muryarsa suka gaisa da gambiya Munaya. Bansan mi tace masa daga canba, ya ɗan dai murmusa yana gyara zamansa da ƙyau. “Ina sake roƙon alfarma dai Ummu, Please a bani ƴar damarnan nima koda sau ɗaya ne”. Idanu ya lumshe a hankali yana cigaba da saurarenta, ya sauke ajiyar zuciya yana jinjina kansa kamar yana a gabanta, saida yay mata godiya sannan ya sauke wayar daga kunnensa yana cika bakinsa da iska ya fesar.
Muna zaune a falo ni da Nabeelah ya shigo, sannu Nabeelah ta shiga jera masa, bai amsa mataba, sai dai ya ɗaga mata hannu kawai ya wuce abinsa. Da kallo muka bisa da gani har ita, na lumshe idanu da kwanciya jikin kujera ina sauke numfashi. “Shi dai Yayanmu kamar mai jinnu haka yake, yanzu zaki gansa a mutum anjima kaɗan ya koma dodo”. Nabeelah ce da wannan maganar cikin shagwaɓa, Bance da ita komaiba na miƙe, ruwa na ɗauka da kofi nabi bayansa.
Ban samesa a faloba, hakan ya sakani binsa bedroom. A gaban mirror na iskesa yana waya da cire boturan shirt ɗinsa, ido muka haɗa ta cikin mirror'n kasancewar a bayansa na tsaya daf. Ni na fara janyewa, dan nikam banason ganinsa a cikin yanayin nan tsoro nakeji, cigaba yay da yin wayarsa tamkarma bai ganni ba. duk da hakan ya sosamin rai sai na nutsu ina saurarensa, mamaki ya kamani sosai dan fahimtar wayar yana yinta ne akan Aunty Shahudah, cikin tsoro-tsoro nake kallonsa lokacin daya ajiye wayar. “Boss wai kana nufin kasan inda aunty Shahudah take dama kenan?”. Rigarsa da ya gama cirewa ya jefa saman sofa, ya fara ƙoƙarin zare belt ɗin wandonsa batare da ya kalli sashenma da nakeba balle nai tunanin samun amsa. Sai da ya gama zame komai daga shi sai boxer sannan ya raɓani ya wuce abinsa. A take jikina ya fara rawa, na shiga ambaton innalillahi..... Ina kafe ƙofar bayin da kallo kamar zai fitone ya bani amsar da nake buƙata. Bansan sanda na zube a bakin gadonba na dafe kai, ts
ahon mintuna ina a haka wayarsa kuma nata faman ring a gefena amma banko kalleta ba. A haka ya fito ya sameni, yanzun ma dai ban ishesa kalloba, ya shirya a gaggauce cikin ƙananun kaya farin wando da farar riga, sai ya ɗaura baƙar jacket a sama mara hannu. Koba'a faɗaba yayi ƙyau sosai, dan shi mutum ne da koyaya ya saka sutura sai kaga ta zauna masa a jiki tsaf tamjar danshi akai. Tsabar wulaƙanci a gabana ya sake ficewa a ɗakin bayan ya zauna ya saka takalma a ƙafarsa, bansan sanda na fashe da kuka ba nai baya a saman gadon.
Gudu sosai Jawaad ya saka Sadiq shararawa dan jirgin su Umm-Anum harya sauka bisa ƙasa, duk da gimbiya ta sanar masa Takawa ya aika motocin da zasu tarosu hakan bai hanashi jin ɗokin son zuwa ya tarbo mahaifiyarsa da kansa ba, shi kaɗai yasan a yanayin da wannan ranar tazo masa, tazo masa da abubuwa kashi-kashi masu yawa, ruɗani daban al'ajabi da matsanancin farincikin dawowar mahaifiyarsa duniyarsa cikin ƙasar haihuwarta.
Suna isowa su Umm-Anum na fitowa a jirgi Anuwar riƙe da hannunta. Da gudu Anum ta ƙaraso gaban Jay da tun tana sakkowa ta hangosa, jikinsa ta faɗa ta rungumesa. Duk da damuwar da yake ciki da yanayinsa na rashin son shiga harkar yara bai gaza karɓar ƴar ƙanwar tasaba kamar yanda taso, ya shafa kanta yana ɗan murmushi kafin ya janyeta a jikinsa ya nufi Umm-Anum. Haɗata yay ita da Anuwar ɗin ya rungumesu gaba ɗa yana maijin a yau babu tamkarsa duk faɗin duniyar nan. Kasan cewar yasan umm-Anum na fama da matsalar kafa bai tsaya ɓata lokaciba suka nufi inda Sadiq ya faka motarsa kusa da motocin masarauta guda uku da sukazo tarbarsu. “Ummuna Abbu fa?”. “Sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zasu taho suma insha ALLAHU, nima dan bazan iya haƙurin kaiwa goben bane shiyyasa”. Murmushi ya saki mai sanyi yana taimaka mata ta shiga motarsa da Sadig ya buɗe. Anuwar da Anum kuma suka shiga motar masarauta ɗaya badan sun so hakanba.
Sai da ya tabbatar komai yayi dai-dai sannan ya zagaya inda Sadiq ya buɗe masa kusa da Umm-Anum shima ya shiga, ya riƙo hannunta ya sumbata, “Amsiyatul sa'iidah. Marhaban biki Ummuna”. Fuskarta ɗauke da murmushi da hawaye tace, “N: Kaifa anta Jay-p na”. Idanu ya lumshe a hankali yana haɗiye nauyin da ƙirjinsa yay masa da sake damƙe hannunta cikin nashi kamar mai gudun a ƙwace masa ita yace, “Ana bikhairin Ummuna”. Ta shafa kansa tana murmushi da faɗin, “Alhamdulillahi ala kulli halin Noorul Ayn”. Ɗagowa yay idanu jazur ya kalleta da sake sumbar hannunta ya ɗaura kansa saman kafadanrta yana sake lumshe idanu. “Ummuna nayi kewarki”. “Nima haka Muhammad Jawaad”. Ta faɗa tana sumbatar goshinsa.
Cikin nutsuwa motocin suka fice daga airport ɗin, ta Jay ce gaba shi da Umm-Anum, sai kuma wadda su Anuwar ke ciki shi da Anum, sai ɗaya da babu kowa a ciki, ta ƙarshe kuma dogaraine.
___________________
Daga kukan da ya barni inayi sai barci ya kwasheni, cikin barci naji ana knocking ƙofar, na buɗe ido a hankali da tashi zaune dan nasan bazai wuci Nabeelah bace, bayi na fara shiga na wanko fuskata da hawaye suka bushe, sannan na fita. Nabeelah tai saurin riƙo hannuna tana faɗin, “Baƙinfa sun iso inaga, dan naji ƙarar buɗe gate”. Bata jira amsata ba taja hannuna muka fito babban falo. Kiciɓis mukai da Anum data fara shigowa. Ta daka wani uban tsalle ta ɗareni, tuni naji duk wani ɓacin ran da Boss ya barni da shi ya gudu, na rungumeta nima cike da tsantsar farin ciki.
Anuwar ne na biyun shigowa, ya fara sauke idanunsa akan Nabeelah da ke tsaye tana kallon su bily da dariya, kafin ya maida ga su Bilkisun yana ɗan ɓata fuska. “Lallaima Aunty, ni baki ganniba sai wannan yarinyar”. “Tuba nake Yah Anuwar ” na faɗa ina sakin Anum.
A waje kam Jay ya taimakama Umm-Anum ta fito daga motar, ƙafafunta duk sunyi fushi saboda zaman jirgi, ga kuma dama ƙafarta na mata ciwo. Wani irin kallo take bin gidan da shi dan bazata taɓa mantawa da shi ba koda a magagin mutuwa take, gidan da yazama tushen komai na maida mijinta wane, gidan da yazama harsashin ginin ɗaukaka ga abin sonta, gidan da zata iya a