Sashe 36
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin barci na ringajin saukar numfashin mutum a jikina, na buɗe idanu a razane ina ambaton ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ tabbas a jikin mutum nake, na buɗe baki zan ƙwalla ƙara aka dafe bakin da hannu, cikin wata irin murya da bantaɓa jin mai itaba a gidan ake magana da shafamin jiki, “Bazan iya saduwa dake baƙya cikin hankalinkiba kamar sauran, shiyyasa na zaɓi baki damar farkawa, kiyi haƙuri ki bani haɗinkai cikin sauƙi bilkisu, samunkine kaɗai ya ragema cikar burina yanzun, karki lalatamin tanadina na tsahon shekaru, nai miki alƙawarin zan biki a sannu bazan cutar dakeba kodan son da nake miki, sannan zaki moru da tagomashi mai yawa a gareni saɓanin sauran da basu sami komaiba sai baƙin ciki, tun farko kece tsanin nasarata da na ɗauku dakon jira tsahon lokaci”.
Tsabar tashin hankalin da nake ciki sai zufa nake kwararwa dukda ac dake aiki a ɗakin, jikina wata irin muguwar rawa yake da ɗaukar azababben zafi lokaci ɗaya, gashi ya rufemin baki, hawayenma sunƙi fita daga idona sai zuciyata ke kukan, duk addu'ar da tazomin bakina yi nake da taimakon UBANGIJI na.
اَللَّهُمَّ إِنَّا نَجْعَلُكَ فِي نُحُورِهِمْ، وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شُرورِهِمْ .
“Allahumma inna naj'aluka fee nuhoorihim wana'oothu bika min shuroorihim”.
Ya ALLAH! Mu mun sanya ka a gabansu, kuma muna neman tsarinka daga sharrace-sharracensu.
اَللَّهُمَّ أَنْتَ عَضُدِي، وَأَنْتَ نَصِيرِي، بِكَ أَجُولُ وَبِكَ أَصُولُ وَبِكَ أُقَاتِلُ.
“Allahumma anta 'adudee, wa-anta naseeree, bika ajoolu wabika asoolu wabika oqatil”.
Ya ALLAH kai ne mai karfafa ni, kuma kai ne mataimakina, da karfinka ne nake yin dabarun yaki, kuma da karfinka ne nake kai hari, kuma da karfinka ne nake yin yaki.
حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ.
“Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel”.
ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro.
اَللَّهُمَّ رَبِّ السَّمَوَاتِ السَّبْعِ، وَرَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، كُنْ لِي جَارًا مِنْ (فُلاَنٍ)، وَأَحْزَابِهِ مِنْ خَلاَئِقِكَ؛ أَنْ يَفْرُطَ عَلَيَّ أَحَدٌ مِنْهُمْ أَوْ يَطْغَى، عَزَّ جَارُكَ، وَجَلَّ ثَنَاؤُكَ، وَلاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ.
“Allahumma rabba s-mawati s-sab'i wa rabba-l-'arshi-l-'azimi. Kun li jaran min (fulanin) wa ahzabihi min khala'iqika, an yafruta 'alayya ahadun minhum aw yatgha. 'Azza jaruka, wa jalla thana'uka, wa la ilaha illa anta”.
Ya Ubangijin sammai bakwai, kuma Ubangijin Al'arshi mai girma, ka kasance mai tsari gare ni daga wane dan wane, da dukkan rundunarsa daga cikin halittunka kar wani daga cikinsu ya yi gaggawar azaba a gare ni, ko ya ketare haddi, kariyarka ta buwaya, kuma babu abin bautawa da gaskiya sai kai.
اَللهُ أَكْبَرْ، اَللهُ أَعَزُّ مِنْ خَلْقِهِ جَمِيعاً ، اَللهُ أَعَزُّ مِمَّا أَخَافُ وَأَحْذَرُ، أَعُوذُ بِاللهِ الَّذِي لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ، الْمُمْسِكِ السَّمَوَاتِ السَّبْعِ أَنْ يَقَعْنَ عَلَى اْلأَرْضِ إِلاَّ بِإِذْنِهِ، مِنْ شَرِّ عَبْدِكَ فُلاَنٌ، وَجُنُودِهِ وَأَتْبَاعِهِ وَأَشْيَاعِهِ، مِنَ الْجِنِّ وَاْلإِنْسِ، اَللَّهُمَّ كُنْ لِي جَاراً مِنْ شَرِّهِمْ، جَلَّ ثَنَاؤُكَ وَعَزَّ جَارُكَ، وَتَبَارَكَ اِسْمُكَ، وَلاَ إِلَهَ غَيْرُكَ " ثَلاَثَ مَرَّاتٍ.
“ALLAHU akbaru. ALLAHU a'azzu min khalqihi jami'an. ALLAHU a'azzu mimma akhfu wa ahdharu. A'udhu billahi lazee la ilaha illa huwal mumsikis samawatis s
ab'i an yaqa'na 'alal-ardi illa bi'izinihi, min sharri 'abdika (fulanin) wa junudihi wa atba'ihi wa ashya'ihi minal-jinni wal-insi. Allahumma kun li jaran min sharrihim Jalla thana'uka wa 'azza jaruka, wa tabaraka smuka, wa la ilaha ghayruka”.
ALLAH shi ne mafi girma, ALLAH shi ne mafi buwaya daga dukkanin halittarsa, shi ne mafi buwaya daga abin da nake jin tsoronsa kuma nake shayinsa. Ina neman tsarin ALLAH, wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi, mai rike sammai daga su ruguzo a kan kasa sai da izininsa, daga sharrin bawanka (ya ambai sunansa), Ya ALLAH! Ka zamo mai tsari gare ni daga sharrinsu. Yabonka ya girma, kuma kaiyarka ta buwaya, kuma alherin sunanka ya yawaita, kuma babu abin bautawa da gaskiya ba kai ba”.
Duk da na rigada na sadaƙar tawa ta ƙare ban fasa karanto addu'oinba ina faɗama ALLAH kukana, koda a wani wajen bana haɗa kalmomin dai-dai saboda ruɗani karantowa nake, wata razananniyar ƙara mukaji a dukkanin illahirin gidan, hakan ya saka koma waye sakarmin baki ya miƙe a firgice kamar yanda nima na samu damar ƙwalla tawa ƙarar saboda firgita da nayi, ɗif naji kunnuwana sun daɗe banajin motsin komai, dukda ɗakin a duhu yake dunɗum, jinai an sake rungumeni an fashe da kuka, yanzunkam a tare muka ƙwala ihu da koma wanene duk da naji jikin ya banbanta dana wancan, ɗakin sai naga yana wani irin juyamin tamkar ina cikin hajijiya, rumtse idanuna nai da ƙarfi na sake ƙwalla ƙarar da ni kaina bansan iyakar ina muryata ta tsaya ba a gidan, daga nan ban sake sanin mi duniyar ke cikiba kuma.
Duk wanda yake a cikin gidan kunnensa saida ya jiye masa ƙara maiban tashin hankali da tsoratarwa da aka ƙwala da farko a wannan dare, wadda taɗauki adadin mintuna biyar kafin ta gushe ihun bilkisu ya biyo bayanta, Aamilah da ɗakinta ke kusa dana Bilkisu ce ta fara fitowa a razane saboda kiɗimar data shiga na tsoro itama, cikin lalube ta afko ɗakin bilkisu batare data saniba itama tana ihun, fitar sautin ihun bilkisu ne ya bata damar isa inda take suka ƙanƙame juna suna kuka maiban tashin hankali. A daidai lokacin da Qaseem da Salman harma da kuku suka shigo sashen suma a razane, dan duk wanda yake gidan yaji ƙarar farko, sannan a yanzu yana jiyo ihun su Aamilah dake nuna alamar tsoratar da sukaice ta gusar musu da hankali suka tsinci kansu a yanayin. Kuku ne ya samu damar kunna fitilar ɗakin haske ya gauraye ko'ina, dukansu kansu Bilkisu sukayi, dan hakan yayi daidai da ɗaukewar numfashinta daga gangar jikinta.
Babu mai iya musalta tashin hankalin da suke ciki a wannan dare, kan kowa ya kulle daga abinda ya faru, cikin ƙarfin hali Salman ya ɗakko ruwa ya miƙama Qaseem dake taya Aamilah jijjiga Bilkisu, bai tsaya yayyafa mataba ya bulbule matashi kawai a fuska, wani nannauyan numfashi Bily ta kawo, sai dai jikinta babu alamun ƙarfi, ta buɗe idanu a hankali ta kalli kowa sai kuma ta maida ta lumshesu hawayen da bata samu yiba ɗazun suna ziraro mata a kumatu masu ɗumi.
Sama-sama nake iya jiyo muryar yah Qaseem daketa jeramin sannu shida Aamilah da Kuku, bandaiji muryar Salman ba sai daga baya, tsahon wasu mintuna muna a haka kafin barci yaɗan fara fisgata, addu'a nake buƙatar ko yaya wani ya dinga karantowa yana tofamin kozanji sauƙin abinda nakeji a jikina tamkar ana kunna garwashin wuta, sai dai nasan ba samu zanba, dan duk waɗanda suke a kaina babu mai irin wannan tunanin. nesa-nesa nake jiyo maganar Yah Qaseem dake cewa Aunty Aamilah mutashi muje mu kwanta, da taimakonta na koma saman gado, sai daifa tace itama anan zata kwana bazata koma ɗakintaba, sannan suma dan ALLAH su kwanta anan ɓangaren basai sun koma nasuba. Bansan amsar da suka bataba saboda idona ya rufe ruf da barci.
★★★
Kiran sallar farko na asubahi na farka, sai dai abin mamaki da al'ajabi na mance kaso mafi yawa na abinda ya faru jiya a gidan, na tashi zaune ina kallon Aunty Aamilah dake mamuƙe dani alamar a tsorace tai barci, ajiyar zuciya na sauke a hankali inason tuno koda wani abune kaɗan, sai dai sam ƙwaƙwalwata ta gaza aiki, tamkar ansa murfi an toshe bututun dake kai saƙo tsaka
nin ƙwaƙwalwa da zuciyata, addu'a na shiga karantowa kozan sami sassaucin da nakeji dangane da ƙuncin da zuciyata ta shiga da zafin da nakeji a cikinta.
اَللَّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُوفَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِي طَرْفَةَ عَيْن، وَأَصْلِحْ لِي شَأْنِي كُلَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أنْتَ.
“Allahumma rahmataka arjoo fala takilnee ila nafsee tarfata 'ayn, wa-aslih lee sha'nee kullah, la ilaha illa ant”.
Ya ALLAH! Rahamarka nake kauna, don haka kar ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma ka kyautata mini sha'ainina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai kai.
Sai da aka fara kiran salla ta biyu sannan na samu ƙarfin sakkowa daga gadon, banda ƙuncin zuciya babu abinda nakeji a jikina, sai kaina dake ɗan ciwo kaɗan-kaɗan da marata, ban ɗauki hakan komaiba, dan nasan hakan alamun zuwan period ɗinane, da sam bana ciwon mara idan zanyi al'ada, amma a shekararnan gaba ɗaya haka nake fama dukda bawai yanamin tsanani baneba. Saida na duba na tabbatar babu alamar zuwansa ciwon mararne kawai sannan nai wanka dan na samu ƙwarin jikina, daga nan nayo alwala na fito. Nayi ƙoƙarin tada aunty Aamilah amma sam taƙi koda motsi, haka na haƙura na barta nai sallata ganin nima lokaci na neman ƙwace mani. Bayan nayi azkar karatun alkur'ani nayi har zuwa 7am sannan na tashi, shirin office nayi abina, harna kammala aunty Aamilah batako motsaba har lokacin, nakuma ƙoƙarin tadata salla amma taƙi tashi, ƙyaleta nayi na fita kicin danna samu koɗan tea na sha dukda banajin cin komai.
★★★★★★★
Tunda suka shigo gidan daga asibiti daƙyar ya iya dauriyar yin wanka saboda barcin da yakeji, ya samu yay shafa'i da wutiri a daddafe ya haye gadonsa, ya fara addu'a, amma bashi da tabbacin ya kammalata barci yay awan gaba dashi. Can tsakkiyar dare ya farka a matuƙar razane saboda mummunan mafarkin da yayi.
‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’.
أَعُوذُ بِكَلِمَاتِ اللَّهِ التَّامَّاتِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ، وَشَرِّ عِبَادِهِ وَمِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ وَأَنْ يَحْضُرُونَ.
“A'oozu bikalimatil-lahit-tammat min ghadabih,wa'iqabih, washarri 'ibadih, wamin hamazatish-shayateen, wa-an yahduroon”.
Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga fushinsa, da ukubarsa, da sharrin bayinsa, da kuma wasuwasin shaidanu, da kuma kada su zo mini (a cikin al'amurana).
أَعُوذُ بِاللهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ ثَلاَثٍ مَرَّاتٍ.
a'uzu bi-l-lahi mina shaytani r-rajeem’. ya faɗa sau uku, yay addu'a ya tofa gefen haggunsa da dama sau uku, sannan ya sauka a gadon, alwala yayo yazo yay salla raka'a biyu saboda idonsa cike yake da barci, yay addu'a sama-sama ya koma saman gadon ya kwanta, sai dai ya canja sashen da yay mafarkin dashi ɗazun. Babu jimawa barcin ya sake awan gaba dashi.
Ana kiran sallar shiga massalaci ya farka, hakan ya sakashi ɗaura al'wala ya fita massalaci dan har an tada sallah. Koda aka idar bai wuce motsa jikiba yau sai ya shigo gida duk da yana buƙata saboda jikinsa yayi nauyi, gyara ɗakinsa yay ya shiga wanka, bayan ya fito yay shirin office. Ƙarfe bakwai da kwata Gimba ya ɗaukesa suka fice daga gidan..............✍
Tsabar tashin hankalin da nake ciki sai zufa nake kwararwa dukda ac dake aiki a ɗakin, jikina wata irin muguwar rawa yake da ɗaukar azababben zafi lokaci ɗaya, gashi ya rufemin baki, hawayenma sunƙi fita daga idona sai zuciyata ke kukan, duk addu'ar da tazomin bakina yi nake da taimakon UBANGIJI na.
اَللَّهُمَّ إِنَّا نَجْعَلُكَ فِي نُحُورِهِمْ، وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شُرورِهِمْ .
“Allahumma inna naj'aluka fee nuhoorihim wana'oothu bika min shuroorihim”.
Ya ALLAH! Mu mun sanya ka a gabansu, kuma muna neman tsarinka daga sharrace-sharracensu.
اَللَّهُمَّ أَنْتَ عَضُدِي، وَأَنْتَ نَصِيرِي، بِكَ أَجُولُ وَبِكَ أَصُولُ وَبِكَ أُقَاتِلُ.
“Allahumma anta 'adudee, wa-anta naseeree, bika ajoolu wabika asoolu wabika oqatil”.
Ya ALLAH kai ne mai karfafa ni, kuma kai ne mataimakina, da karfinka ne nake yin dabarun yaki, kuma da karfinka ne nake kai hari, kuma da karfinka ne nake yin yaki.
حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ.
“Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel”.
ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro.
اَللَّهُمَّ رَبِّ السَّمَوَاتِ السَّبْعِ، وَرَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، كُنْ لِي جَارًا مِنْ (فُلاَنٍ)، وَأَحْزَابِهِ مِنْ خَلاَئِقِكَ؛ أَنْ يَفْرُطَ عَلَيَّ أَحَدٌ مِنْهُمْ أَوْ يَطْغَى، عَزَّ جَارُكَ، وَجَلَّ ثَنَاؤُكَ، وَلاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ.
“Allahumma rabba s-mawati s-sab'i wa rabba-l-'arshi-l-'azimi. Kun li jaran min (fulanin) wa ahzabihi min khala'iqika, an yafruta 'alayya ahadun minhum aw yatgha. 'Azza jaruka, wa jalla thana'uka, wa la ilaha illa anta”.
Ya Ubangijin sammai bakwai, kuma Ubangijin Al'arshi mai girma, ka kasance mai tsari gare ni daga wane dan wane, da dukkan rundunarsa daga cikin halittunka kar wani daga cikinsu ya yi gaggawar azaba a gare ni, ko ya ketare haddi, kariyarka ta buwaya, kuma babu abin bautawa da gaskiya sai kai.
اَللهُ أَكْبَرْ، اَللهُ أَعَزُّ مِنْ خَلْقِهِ جَمِيعاً ، اَللهُ أَعَزُّ مِمَّا أَخَافُ وَأَحْذَرُ، أَعُوذُ بِاللهِ الَّذِي لاَ إِلَهَ إِلاَّ هُوَ، الْمُمْسِكِ السَّمَوَاتِ السَّبْعِ أَنْ يَقَعْنَ عَلَى اْلأَرْضِ إِلاَّ بِإِذْنِهِ، مِنْ شَرِّ عَبْدِكَ فُلاَنٌ، وَجُنُودِهِ وَأَتْبَاعِهِ وَأَشْيَاعِهِ، مِنَ الْجِنِّ وَاْلإِنْسِ، اَللَّهُمَّ كُنْ لِي جَاراً مِنْ شَرِّهِمْ، جَلَّ ثَنَاؤُكَ وَعَزَّ جَارُكَ، وَتَبَارَكَ اِسْمُكَ، وَلاَ إِلَهَ غَيْرُكَ " ثَلاَثَ مَرَّاتٍ.
“ALLAHU akbaru. ALLAHU a'azzu min khalqihi jami'an. ALLAHU a'azzu mimma akhfu wa ahdharu. A'udhu billahi lazee la ilaha illa huwal mumsikis samawatis s
ab'i an yaqa'na 'alal-ardi illa bi'izinihi, min sharri 'abdika (fulanin) wa junudihi wa atba'ihi wa ashya'ihi minal-jinni wal-insi. Allahumma kun li jaran min sharrihim Jalla thana'uka wa 'azza jaruka, wa tabaraka smuka, wa la ilaha ghayruka”.
ALLAH shi ne mafi girma, ALLAH shi ne mafi buwaya daga dukkanin halittarsa, shi ne mafi buwaya daga abin da nake jin tsoronsa kuma nake shayinsa. Ina neman tsarin ALLAH, wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi, mai rike sammai daga su ruguzo a kan kasa sai da izininsa, daga sharrin bawanka (ya ambai sunansa), Ya ALLAH! Ka zamo mai tsari gare ni daga sharrinsu. Yabonka ya girma, kuma kaiyarka ta buwaya, kuma alherin sunanka ya yawaita, kuma babu abin bautawa da gaskiya ba kai ba”.
Duk da na rigada na sadaƙar tawa ta ƙare ban fasa karanto addu'oinba ina faɗama ALLAH kukana, koda a wani wajen bana haɗa kalmomin dai-dai saboda ruɗani karantowa nake, wata razananniyar ƙara mukaji a dukkanin illahirin gidan, hakan ya saka koma waye sakarmin baki ya miƙe a firgice kamar yanda nima na samu damar ƙwalla tawa ƙarar saboda firgita da nayi, ɗif naji kunnuwana sun daɗe banajin motsin komai, dukda ɗakin a duhu yake dunɗum, jinai an sake rungumeni an fashe da kuka, yanzunkam a tare muka ƙwala ihu da koma wanene duk da naji jikin ya banbanta dana wancan, ɗakin sai naga yana wani irin juyamin tamkar ina cikin hajijiya, rumtse idanuna nai da ƙarfi na sake ƙwalla ƙarar da ni kaina bansan iyakar ina muryata ta tsaya ba a gidan, daga nan ban sake sanin mi duniyar ke cikiba kuma.
Duk wanda yake a cikin gidan kunnensa saida ya jiye masa ƙara maiban tashin hankali da tsoratarwa da aka ƙwala da farko a wannan dare, wadda taɗauki adadin mintuna biyar kafin ta gushe ihun bilkisu ya biyo bayanta, Aamilah da ɗakinta ke kusa dana Bilkisu ce ta fara fitowa a razane saboda kiɗimar data shiga na tsoro itama, cikin lalube ta afko ɗakin bilkisu batare data saniba itama tana ihun, fitar sautin ihun bilkisu ne ya bata damar isa inda take suka ƙanƙame juna suna kuka maiban tashin hankali. A daidai lokacin da Qaseem da Salman harma da kuku suka shigo sashen suma a razane, dan duk wanda yake gidan yaji ƙarar farko, sannan a yanzu yana jiyo ihun su Aamilah dake nuna alamar tsoratar da sukaice ta gusar musu da hankali suka tsinci kansu a yanayin. Kuku ne ya samu damar kunna fitilar ɗakin haske ya gauraye ko'ina, dukansu kansu Bilkisu sukayi, dan hakan yayi daidai da ɗaukewar numfashinta daga gangar jikinta.
Babu mai iya musalta tashin hankalin da suke ciki a wannan dare, kan kowa ya kulle daga abinda ya faru, cikin ƙarfin hali Salman ya ɗakko ruwa ya miƙama Qaseem dake taya Aamilah jijjiga Bilkisu, bai tsaya yayyafa mataba ya bulbule matashi kawai a fuska, wani nannauyan numfashi Bily ta kawo, sai dai jikinta babu alamun ƙarfi, ta buɗe idanu a hankali ta kalli kowa sai kuma ta maida ta lumshesu hawayen da bata samu yiba ɗazun suna ziraro mata a kumatu masu ɗumi.
Sama-sama nake iya jiyo muryar yah Qaseem daketa jeramin sannu shida Aamilah da Kuku, bandaiji muryar Salman ba sai daga baya, tsahon wasu mintuna muna a haka kafin barci yaɗan fara fisgata, addu'a nake buƙatar ko yaya wani ya dinga karantowa yana tofamin kozanji sauƙin abinda nakeji a jikina tamkar ana kunna garwashin wuta, sai dai nasan ba samu zanba, dan duk waɗanda suke a kaina babu mai irin wannan tunanin. nesa-nesa nake jiyo maganar Yah Qaseem dake cewa Aunty Aamilah mutashi muje mu kwanta, da taimakonta na koma saman gado, sai daifa tace itama anan zata kwana bazata koma ɗakintaba, sannan suma dan ALLAH su kwanta anan ɓangaren basai sun koma nasuba. Bansan amsar da suka bataba saboda idona ya rufe ruf da barci.
★★★
Kiran sallar farko na asubahi na farka, sai dai abin mamaki da al'ajabi na mance kaso mafi yawa na abinda ya faru jiya a gidan, na tashi zaune ina kallon Aunty Aamilah dake mamuƙe dani alamar a tsorace tai barci, ajiyar zuciya na sauke a hankali inason tuno koda wani abune kaɗan, sai dai sam ƙwaƙwalwata ta gaza aiki, tamkar ansa murfi an toshe bututun dake kai saƙo tsaka
nin ƙwaƙwalwa da zuciyata, addu'a na shiga karantowa kozan sami sassaucin da nakeji dangane da ƙuncin da zuciyata ta shiga da zafin da nakeji a cikinta.
اَللَّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُوفَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِي طَرْفَةَ عَيْن، وَأَصْلِحْ لِي شَأْنِي كُلَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أنْتَ.
“Allahumma rahmataka arjoo fala takilnee ila nafsee tarfata 'ayn, wa-aslih lee sha'nee kullah, la ilaha illa ant”.
Ya ALLAH! Rahamarka nake kauna, don haka kar ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma ka kyautata mini sha'ainina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai kai.
Sai da aka fara kiran salla ta biyu sannan na samu ƙarfin sakkowa daga gadon, banda ƙuncin zuciya babu abinda nakeji a jikina, sai kaina dake ɗan ciwo kaɗan-kaɗan da marata, ban ɗauki hakan komaiba, dan nasan hakan alamun zuwan period ɗinane, da sam bana ciwon mara idan zanyi al'ada, amma a shekararnan gaba ɗaya haka nake fama dukda bawai yanamin tsanani baneba. Saida na duba na tabbatar babu alamar zuwansa ciwon mararne kawai sannan nai wanka dan na samu ƙwarin jikina, daga nan nayo alwala na fito. Nayi ƙoƙarin tada aunty Aamilah amma sam taƙi koda motsi, haka na haƙura na barta nai sallata ganin nima lokaci na neman ƙwace mani. Bayan nayi azkar karatun alkur'ani nayi har zuwa 7am sannan na tashi, shirin office nayi abina, harna kammala aunty Aamilah batako motsaba har lokacin, nakuma ƙoƙarin tadata salla amma taƙi tashi, ƙyaleta nayi na fita kicin danna samu koɗan tea na sha dukda banajin cin komai.
★★★★★★★
Tunda suka shigo gidan daga asibiti daƙyar ya iya dauriyar yin wanka saboda barcin da yakeji, ya samu yay shafa'i da wutiri a daddafe ya haye gadonsa, ya fara addu'a, amma bashi da tabbacin ya kammalata barci yay awan gaba dashi. Can tsakkiyar dare ya farka a matuƙar razane saboda mummunan mafarkin da yayi.
‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’.
أَعُوذُ بِكَلِمَاتِ اللَّهِ التَّامَّاتِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ، وَشَرِّ عِبَادِهِ وَمِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ وَأَنْ يَحْضُرُونَ.
“A'oozu bikalimatil-lahit-tammat min ghadabih,wa'iqabih, washarri 'ibadih, wamin hamazatish-shayateen, wa-an yahduroon”.
Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga fushinsa, da ukubarsa, da sharrin bayinsa, da kuma wasuwasin shaidanu, da kuma kada su zo mini (a cikin al'amurana).
أَعُوذُ بِاللهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ ثَلاَثٍ مَرَّاتٍ.
a'uzu bi-l-lahi mina shaytani r-rajeem’. ya faɗa sau uku, yay addu'a ya tofa gefen haggunsa da dama sau uku, sannan ya sauka a gadon, alwala yayo yazo yay salla raka'a biyu saboda idonsa cike yake da barci, yay addu'a sama-sama ya koma saman gadon ya kwanta, sai dai ya canja sashen da yay mafarkin dashi ɗazun. Babu jimawa barcin ya sake awan gaba dashi.
Ana kiran sallar shiga massalaci ya farka, hakan ya sakashi ɗaura al'wala ya fita massalaci dan har an tada sallah. Koda aka idar bai wuce motsa jikiba yau sai ya shigo gida duk da yana buƙata saboda jikinsa yayi nauyi, gyara ɗakinsa yay ya shiga wanka, bayan ya fito yay shirin office. Ƙarfe bakwai da kwata Gimba ya ɗaukesa suka fice daga gidan..............✍