Sashe 87
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda safe dama mai ƙunshi tazo muka shige cikin ɗaki daga ni sai ita ta shiga zanamin na nutsuwa, zuwa azhar ya bushe yay shar kamar ka cinye dan baƙi da jaa aka ɗaɗara mani, kasancewar fashin salla nike dama sai kawai aka shigamin gyaran kai a nan gida dan Gimbiya nada dukkan kayan gyaran kai a gida da takema kanta, bayan an kammala nai wanka lokacin ƙarfe kusan uku.
Kasancewar ba sallah zanyi ba sai ban damu da kwalliyar da ake shirin tsaramin ba, ni kaina basai an faɗaba nasan ina tsaruwa dai-dai gwargwadon iko, duk da ba'aimin kwalliyar dana canja kamanni baneba amma nayi ƙyau fiye da zato. Bayan an kammala kwalliyar aka shiryani cikin atamfa lass ƴar ubansu datasha stones work ɗan gaske, sket da riga akai da suka fidda ainahin tsarin jikina dukda basu matseni tsam ba, sundai zaunamin a jiki ɗas har ni kaina ban gaji da kallon kaina ba. An min naɗin ɗan kwali mai tsari aka ƙawata adon nawa da sauran kayan ƙawata kwalliya irinsu sarƙa da sauransu. Ƙamshina kam ai har hawa kan mutane yakeyi, daka ganni kaga cikakkaiyar bahaushiya jinin Fulani, tabbas a yau na sake yarda da babu mummuna a duniya sai wanda ya munana kansa, idan har zaka tashi ka gyara kanka tofa ka wuce a kiraka mai muni, dama can rashin gata da kulawane suka dadushe sihirtaccen ƙyawuna mai cike da kwarjini.
Taron iya matane, dan acikin masarauta ma za'a yisa, su Ummah da danginsu duk sun iso masarautar, hakama danginna na ɓangaren Uwa su Inna Zainabu dasu Momy harda Aamilah, Aunty Shahudah dai ban gantaba, ƴan gidansu Boss ma kam inada tabbacin ƙwai da kwarkwata ne a wajen nan. Babu abinda da dai za'a cema UBANGIJI sai godiya a wannan al'amari, amma tabbas Bilkisu tazo da farin jini mai ban mamaki da tarin alkairi. Iyayen ƙawayenta su Ummie, matansu Aliyu, abokan aikinsu ƴan station ɗinsu, ƙawayenta na makaranta harma da waɗanda sukazo dalilin wane da wane duk suna a wajen. Sai ƙarfe huɗu da rabi Gimbiya Sarauniyar gagara badau Munayatul-muna ta fito riƙe da hannun amarya Bilkisu mai gadon zinari.
Ai a take wajen ya ɗauki ƙannan magana musamman ma ƴan gidansu Jawaad da ada suke ɗaukar Bilkisu ba komaiba saboda yanda su Momy ke munanata da ƙasƙantar da ita a garesu. Wasu sunɗan santa sama-sama wasuko sai a yau suke ganinta.
Ganin yanda ɗunbin mutane suka taru danni sai kawai naji hawaye sun zubomin a kumatu, Zuhrah ce ta duƙa gabana inda ya kasance mazaunina ta shareminsu da handkherchief tana murmushi, “Haba amarsu ai lokacin kuka baiyiba kinji, sai gobe idan ALLAH ya kaimu kina kusa da Boss, da sun zubo ya lashe kayansa”. ta ƙare maganar da kashemin ido. Hararta nayi ban iya cewa komaiba, sai dai fa maganar datai sai da naji gabana yaɗan faɗi, dana tuna kuma ma ina period saina ɗanji sauƙi a raina.
Ba'a ɓata lokaci wajen fara gudanar da abinda ya tara mutane ba, komai kuma a nutse babu wata hayaniya, koda aka fara kiɗan ƙwarya ma a nutse ƴammata da matan aurenma masu jini a jika keyin rawa, ina tsakkiya nikam anata zubamin liƙi, Anum na liƙe dani wai tana gwagwaɗamin wai itama idan ta tashi aure zamuje Saudiyya da masu kiɗan su mat. Murmushi kawai nayi mata dan ta bani dariya.
komai ya tafi cikin burgewa da kwanciyar hankali, kafin a koma yin hotuna da kowa ke fatan yi da amarya da gimbiyar gagara badau. Zuwa magriba aka tashi.
Ni dai tunma kafin magriban muka bar wajen tare da Ummu da akoda yaushe tana kusa dani idanunta akan kowa da zai iya raɓata. Dan tace itafa bata wani yarda da kowa dake wajenba.
__________________
A ɓangaren su Jay suma sunacan suna nasu shagalin, sai dai su nasu sai bayan sallar isha'i suka fara, suma iyasune maza zalla a wajen abokansa, su Aryaan duk suna can dan kuwa dai sa'annine, sudai su Abdur-raheem, dasu Anuwar basu jeba kasancewar su Jay yayunsune wannan shigar ba tasu bace, suna buƙatar sakewa kuma, sunama can gidan Mami Munubiya suna shan shaftarsu hankali kwance.
Dauriya kawai Jay keyi, dan kansa ciwo yake masa matsanancin ciwo ma kuwa, amma kasancewar yasan duk ɗunbin mutanennan dan shi
suka taru sai ya daure har zuwa goma na dare kafin ya gudu ɗakin da zai kwana a hotel ɗin ya barsu, ko wanka baiyiba dan bai jima da yiba, kayansa kawai ya zame ya faɗa saman gadon ya kwanta yana sauke tagwayen ajiyar zuciya, cikin ransa ko mamakin Bilkisu ya keyi, ƙaramar yarinya da ita sai shegen jan aji da miskilanci, tunda ta tafi bata nemsaba, ta dawo ma haka. Wani ɓangare na zuciyarsa yace, ‘Kaida haƙƙin sanin lafiyarta ke a kanka ka nemeta ne?’. Kansa ya dafe kawai da lumshe idanu, kafin ya buɗe a hankali ya jawo wayarsa dan tunawa da saƙwanin da yasa a turo masa.
Kasancewar datarsa a buɗe take duk sunma buɗe kansu da kansu, harda videos. Ya sauki wani lallausan murmushi maiban mamaki daya sakani tunanin wai shin mi yake kallo hakane?................✍
Jiya kun haɗan zafi yasin, waɗanda ban ɗaga kiransu ba suyi haƙuri man kaina ne ya tsiyaye😂🚴🏼.
BARKA DA JUMA'A.
Musha weekend lafiya
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭😭🙏🏻
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya!!!
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 38
..................Shagulgulan biki sun cigaba da gudana a washe gari tamkar yanda aka tsara, su Ummah babba sunyi yinin biki suma matsayin iyayen ango, kafin zuwa la'asar su ɗunguma zuwa masarauta domin halartar walima da gimbiya ta shirya itama. Walima kam ta ƙayatar fiye da zato, amarya tasha ƙyau cikin shadda pink mai duhu. Inda malamai magada annabawa suka gudanar da wa'azi mai kashe jiki da ɓargo, bilkisu kam dai ansha kuka, idanu sun ƙara girma. Tun su Zuhrah dake zaune kusa da ita suna mata dariya har dai suka koma lallashinta suma suna sharar hawayen dan jikinsu duk sai yay sanyi ƙalau. An tashine gab da magriba, dan haka kowa yana yin salla shirin tafiya dinner ya fara. Amarya ma wanka aka sakata ta shiga.
Gaba ɗaya jikina a sanyaye yake, tunani da fargaba duk sun cika zuciyata, yau ni Bilkisu nice za'a ɗauka akai gidan boss matsayin matarsa ta aure, aure ba yawo ba, idan naje shike nan natafi din din din, duk da nasan ba sonsa nakeba, shima kuma bason nawa ya keba na ɗaura ɗammarar masa biyyayya insha ALLAH, zanyi haƙuri tamkar yanda kowa ke faɗamin zaman aure haƙurine, zanyi biyayya a garesa matsayinsa na mijina shugabana, zanyi aiki da dukkan dabarun Umm-Anum da gambiya suka ɗorani akai domin samun zaman lafiya a gidana koda ace bazai soni ba. tausayinsa nakeji har cikin raina yanzun, dan a daren jiya munyi zama na musamman da Ummu inda muka tattauna game da kamanninsa da Anuwar harma da Umm-Anum ta abubuwa da dama. Ta tabbatar min nice ya dace nai wannan aikin na bincikar abinda ya shafesa ko tanan zasu iya fahimtar idan akwai alaƙar da duk muke zargi dan kamannin sun wuce kama akwai dangantakar jini dole, bansan komai na abinda ya shafi family nasa ba, sai ɗan abinda ba'a rasaba shima iyakarsa daga wajen su Mom ne da da rashin jituwa tsakaninsa da Yah Qaseem, amma a raina nima tunda muka haɗu da Umm-Anum nakeji abubuwa da dama nazomin a rai game da shi......... Da wannan tunane-tunanen na tsaftace jikina na fito, kasancewar ba salla zanyiba zaman min kwalliya akayi.
Tun ina jiyo hayaniyar ƙawayena dake ɗakin su Amaturrahman suna shiryawa har naji tsit, alamar dai sun fice dan zuwa yanzu har anyi sallar isha'i. Basan yaya zan musalta muku irin ƙyawun da nayiba yauma, amma na bama kowa damar ya hasasoni cikin zuciyarsa, kwalliyata ta yau ta kasance harda alƙyabar da Mommah ta bani matsayin ƙyautarta, basai an faɗaba, a gani da ido kaɗai ya isa amsa ga mai kallo cewar an sayeta da kuɗaɗe masu nauyi da darajar gaske. Suna cikin gyaramin alƙyabbar da santin ƙyawun da nayi aunty Samha ta shigo.
“Wow, masha ALLAH amaryar ƙamshi” ta faɗa tana rungumeni, ta ɗagoni tana kallona da cigaba da faɗin, “Wannan ai saiki rikita angon yace an fasa dinner ɗin”. Dariya waɗanda sukaimin kwalliyar sukayi, ni dai kaina a ƙasa ban yarda na kalleta bama dan tasa naji kunya, gashi kukane keta ƙoƙarin tasomin ina dannewa. Itace ta kama hannuna muka fice, ganin ba'a kaini wajen Ummu ba sai nayi tunanin za'a sake dawo dani nan kenan, ƙilama sai gobe idan ALLAH ya kaimu. A take naji farin ciki ya wani lulluɓeni. Ko ina ƙwanyar yake da haske a masarauta shiyyasa koda muka fito dukda kaina a ƙasa yake ina kallon inda muka nufa.
Mun tsaya dai-dai motar da na hango Oga Jabeer jingine yana waya tun fitowarmu, yana sanye da shadda ƴar ubansu ruwan madara. Yana ganin mun ƙaraso ya ajiye wayar yana murmushi da faɗin, “Aunty Samha aini da har ina shirin bin bayanku, dan naga baƙwa son bamu amaryarnan kamar”.
Murmushi tayi mai sauti tana gyaramin hular alƙyabar, “To gaskiya badan munasoba zamu baku, dan bamu gaji da ɗiyarmu ba, amma yaya muka iya, wannan shine girman”. Oga Jabeer na ƴar dariya ya buɗe ƙofar motar da cewa, “Aure yaƙin mata”. Tace, “Har mazan ma”.
Daddaɗan ƙamshin turarensa da na sani daine ya fara tarbata da sallama, na shaƙa na lumshe idanu ina ƙoƙarin dai-daita bugun zuciyata da kalato yawun da zan jiƙa maƙoshina da ya bushe, sai da na zauna da ƙyau Mah-mah ta gyaramin alƙyabar sannan na tsinkayi muryarsa yana gaisheta cike da mutun tawa, sai da suka gama gaisuwar s
Kasancewar ba sallah zanyi ba sai ban damu da kwalliyar da ake shirin tsaramin ba, ni kaina basai an faɗaba nasan ina tsaruwa dai-dai gwargwadon iko, duk da ba'aimin kwalliyar dana canja kamanni baneba amma nayi ƙyau fiye da zato. Bayan an kammala kwalliyar aka shiryani cikin atamfa lass ƴar ubansu datasha stones work ɗan gaske, sket da riga akai da suka fidda ainahin tsarin jikina dukda basu matseni tsam ba, sundai zaunamin a jiki ɗas har ni kaina ban gaji da kallon kaina ba. An min naɗin ɗan kwali mai tsari aka ƙawata adon nawa da sauran kayan ƙawata kwalliya irinsu sarƙa da sauransu. Ƙamshina kam ai har hawa kan mutane yakeyi, daka ganni kaga cikakkaiyar bahaushiya jinin Fulani, tabbas a yau na sake yarda da babu mummuna a duniya sai wanda ya munana kansa, idan har zaka tashi ka gyara kanka tofa ka wuce a kiraka mai muni, dama can rashin gata da kulawane suka dadushe sihirtaccen ƙyawuna mai cike da kwarjini.
Taron iya matane, dan acikin masarauta ma za'a yisa, su Ummah da danginsu duk sun iso masarautar, hakama danginna na ɓangaren Uwa su Inna Zainabu dasu Momy harda Aamilah, Aunty Shahudah dai ban gantaba, ƴan gidansu Boss ma kam inada tabbacin ƙwai da kwarkwata ne a wajen nan. Babu abinda da dai za'a cema UBANGIJI sai godiya a wannan al'amari, amma tabbas Bilkisu tazo da farin jini mai ban mamaki da tarin alkairi. Iyayen ƙawayenta su Ummie, matansu Aliyu, abokan aikinsu ƴan station ɗinsu, ƙawayenta na makaranta harma da waɗanda sukazo dalilin wane da wane duk suna a wajen. Sai ƙarfe huɗu da rabi Gimbiya Sarauniyar gagara badau Munayatul-muna ta fito riƙe da hannun amarya Bilkisu mai gadon zinari.
Ai a take wajen ya ɗauki ƙannan magana musamman ma ƴan gidansu Jawaad da ada suke ɗaukar Bilkisu ba komaiba saboda yanda su Momy ke munanata da ƙasƙantar da ita a garesu. Wasu sunɗan santa sama-sama wasuko sai a yau suke ganinta.
Ganin yanda ɗunbin mutane suka taru danni sai kawai naji hawaye sun zubomin a kumatu, Zuhrah ce ta duƙa gabana inda ya kasance mazaunina ta shareminsu da handkherchief tana murmushi, “Haba amarsu ai lokacin kuka baiyiba kinji, sai gobe idan ALLAH ya kaimu kina kusa da Boss, da sun zubo ya lashe kayansa”. ta ƙare maganar da kashemin ido. Hararta nayi ban iya cewa komaiba, sai dai fa maganar datai sai da naji gabana yaɗan faɗi, dana tuna kuma ma ina period saina ɗanji sauƙi a raina.
Ba'a ɓata lokaci wajen fara gudanar da abinda ya tara mutane ba, komai kuma a nutse babu wata hayaniya, koda aka fara kiɗan ƙwarya ma a nutse ƴammata da matan aurenma masu jini a jika keyin rawa, ina tsakkiya nikam anata zubamin liƙi, Anum na liƙe dani wai tana gwagwaɗamin wai itama idan ta tashi aure zamuje Saudiyya da masu kiɗan su mat. Murmushi kawai nayi mata dan ta bani dariya.
komai ya tafi cikin burgewa da kwanciyar hankali, kafin a koma yin hotuna da kowa ke fatan yi da amarya da gimbiyar gagara badau. Zuwa magriba aka tashi.
Ni dai tunma kafin magriban muka bar wajen tare da Ummu da akoda yaushe tana kusa dani idanunta akan kowa da zai iya raɓata. Dan tace itafa bata wani yarda da kowa dake wajenba.
__________________
A ɓangaren su Jay suma sunacan suna nasu shagalin, sai dai su nasu sai bayan sallar isha'i suka fara, suma iyasune maza zalla a wajen abokansa, su Aryaan duk suna can dan kuwa dai sa'annine, sudai su Abdur-raheem, dasu Anuwar basu jeba kasancewar su Jay yayunsune wannan shigar ba tasu bace, suna buƙatar sakewa kuma, sunama can gidan Mami Munubiya suna shan shaftarsu hankali kwance.
Dauriya kawai Jay keyi, dan kansa ciwo yake masa matsanancin ciwo ma kuwa, amma kasancewar yasan duk ɗunbin mutanennan dan shi
suka taru sai ya daure har zuwa goma na dare kafin ya gudu ɗakin da zai kwana a hotel ɗin ya barsu, ko wanka baiyiba dan bai jima da yiba, kayansa kawai ya zame ya faɗa saman gadon ya kwanta yana sauke tagwayen ajiyar zuciya, cikin ransa ko mamakin Bilkisu ya keyi, ƙaramar yarinya da ita sai shegen jan aji da miskilanci, tunda ta tafi bata nemsaba, ta dawo ma haka. Wani ɓangare na zuciyarsa yace, ‘Kaida haƙƙin sanin lafiyarta ke a kanka ka nemeta ne?’. Kansa ya dafe kawai da lumshe idanu, kafin ya buɗe a hankali ya jawo wayarsa dan tunawa da saƙwanin da yasa a turo masa.
Kasancewar datarsa a buɗe take duk sunma buɗe kansu da kansu, harda videos. Ya sauki wani lallausan murmushi maiban mamaki daya sakani tunanin wai shin mi yake kallo hakane?................✍
Jiya kun haɗan zafi yasin, waɗanda ban ɗaga kiransu ba suyi haƙuri man kaina ne ya tsiyaye😂🚴🏼.
BARKA DA JUMA'A.
Musha weekend lafiya
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭😭🙏🏻
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya!!!
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 38
..................Shagulgulan biki sun cigaba da gudana a washe gari tamkar yanda aka tsara, su Ummah babba sunyi yinin biki suma matsayin iyayen ango, kafin zuwa la'asar su ɗunguma zuwa masarauta domin halartar walima da gimbiya ta shirya itama. Walima kam ta ƙayatar fiye da zato, amarya tasha ƙyau cikin shadda pink mai duhu. Inda malamai magada annabawa suka gudanar da wa'azi mai kashe jiki da ɓargo, bilkisu kam dai ansha kuka, idanu sun ƙara girma. Tun su Zuhrah dake zaune kusa da ita suna mata dariya har dai suka koma lallashinta suma suna sharar hawayen dan jikinsu duk sai yay sanyi ƙalau. An tashine gab da magriba, dan haka kowa yana yin salla shirin tafiya dinner ya fara. Amarya ma wanka aka sakata ta shiga.
Gaba ɗaya jikina a sanyaye yake, tunani da fargaba duk sun cika zuciyata, yau ni Bilkisu nice za'a ɗauka akai gidan boss matsayin matarsa ta aure, aure ba yawo ba, idan naje shike nan natafi din din din, duk da nasan ba sonsa nakeba, shima kuma bason nawa ya keba na ɗaura ɗammarar masa biyyayya insha ALLAH, zanyi haƙuri tamkar yanda kowa ke faɗamin zaman aure haƙurine, zanyi biyayya a garesa matsayinsa na mijina shugabana, zanyi aiki da dukkan dabarun Umm-Anum da gambiya suka ɗorani akai domin samun zaman lafiya a gidana koda ace bazai soni ba. tausayinsa nakeji har cikin raina yanzun, dan a daren jiya munyi zama na musamman da Ummu inda muka tattauna game da kamanninsa da Anuwar harma da Umm-Anum ta abubuwa da dama. Ta tabbatar min nice ya dace nai wannan aikin na bincikar abinda ya shafesa ko tanan zasu iya fahimtar idan akwai alaƙar da duk muke zargi dan kamannin sun wuce kama akwai dangantakar jini dole, bansan komai na abinda ya shafi family nasa ba, sai ɗan abinda ba'a rasaba shima iyakarsa daga wajen su Mom ne da da rashin jituwa tsakaninsa da Yah Qaseem, amma a raina nima tunda muka haɗu da Umm-Anum nakeji abubuwa da dama nazomin a rai game da shi......... Da wannan tunane-tunanen na tsaftace jikina na fito, kasancewar ba salla zanyiba zaman min kwalliya akayi.
Tun ina jiyo hayaniyar ƙawayena dake ɗakin su Amaturrahman suna shiryawa har naji tsit, alamar dai sun fice dan zuwa yanzu har anyi sallar isha'i. Basan yaya zan musalta muku irin ƙyawun da nayiba yauma, amma na bama kowa damar ya hasasoni cikin zuciyarsa, kwalliyata ta yau ta kasance harda alƙyabar da Mommah ta bani matsayin ƙyautarta, basai an faɗaba, a gani da ido kaɗai ya isa amsa ga mai kallo cewar an sayeta da kuɗaɗe masu nauyi da darajar gaske. Suna cikin gyaramin alƙyabbar da santin ƙyawun da nayi aunty Samha ta shigo.
“Wow, masha ALLAH amaryar ƙamshi” ta faɗa tana rungumeni, ta ɗagoni tana kallona da cigaba da faɗin, “Wannan ai saiki rikita angon yace an fasa dinner ɗin”. Dariya waɗanda sukaimin kwalliyar sukayi, ni dai kaina a ƙasa ban yarda na kalleta bama dan tasa naji kunya, gashi kukane keta ƙoƙarin tasomin ina dannewa. Itace ta kama hannuna muka fice, ganin ba'a kaini wajen Ummu ba sai nayi tunanin za'a sake dawo dani nan kenan, ƙilama sai gobe idan ALLAH ya kaimu. A take naji farin ciki ya wani lulluɓeni. Ko ina ƙwanyar yake da haske a masarauta shiyyasa koda muka fito dukda kaina a ƙasa yake ina kallon inda muka nufa.
Mun tsaya dai-dai motar da na hango Oga Jabeer jingine yana waya tun fitowarmu, yana sanye da shadda ƴar ubansu ruwan madara. Yana ganin mun ƙaraso ya ajiye wayar yana murmushi da faɗin, “Aunty Samha aini da har ina shirin bin bayanku, dan naga baƙwa son bamu amaryarnan kamar”.
Murmushi tayi mai sauti tana gyaramin hular alƙyabar, “To gaskiya badan munasoba zamu baku, dan bamu gaji da ɗiyarmu ba, amma yaya muka iya, wannan shine girman”. Oga Jabeer na ƴar dariya ya buɗe ƙofar motar da cewa, “Aure yaƙin mata”. Tace, “Har mazan ma”.
Daddaɗan ƙamshin turarensa da na sani daine ya fara tarbata da sallama, na shaƙa na lumshe idanu ina ƙoƙarin dai-daita bugun zuciyata da kalato yawun da zan jiƙa maƙoshina da ya bushe, sai da na zauna da ƙyau Mah-mah ta gyaramin alƙyabar sannan na tsinkayi muryarsa yana gaisheta cike da mutun tawa, sai da suka gama gaisuwar s