Sashe 110
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
..................Tsaf muka kammala komai tare da shi, kiran sallar zuhur da akayine ya sakashi fita ya barni ina ƙarasa sauran abubuwan. Nima a gurguje na ƙarasa komai na fito yin sallar. Na idar kenan ina addu'a naji ana sallama, kafin na miƙe na fita ganin wanene Nabeelah ta shigo ɗakin.
Murmushi mukaima juna, ta ƙaraso ta rungumeni tana faɗin “Amarsu ta ango mai daɗin suna, bara na faɗa a hankali kar yauma nai suɓutar baki ya jini ya markaɗa”. Dariya ta bani sosai, dan haka na shiga yi. “Hum ke dariyama abin ya baki, wlhy kaɗan daga aikinsa yamin casar gyaɗa indai yayanmu ne. Ina fata baya nan?”. Toilet na nuna mata da ahannu ina faɗin, “Yana ciki kuwa”. Sosai ta waro idanu waje da faɗin, “Na shiga Uku dan ALLAH da gaske kikeyi?”. Yanda ta rikice ɗinne ya sakani sakeyin murmushi, na ajiye abin sallar dana linke, “Wai ke kaɗai kikazo ne?”. “A'a ni da su Ummah ne fa, suna falo”. Ban bata amsaba na fito batare dana cire hijjabin ba.
Tunda na fito suka zubamin idanu har abin ya bani kunya, na ƙarasa inda suke kaina a ƙasa, har ƙasa na durƙusa inai musu sannu da zuwa. Cikin fara'a suka amsamin har suna haɗa baki wajan faɗin nazo garesu. A kunyace na kuma tashi naje gabansu dab zan sake tsugunnawa Ummah babba ta riƙoni, tsakkiyarsu ta zaunar dani tare da rungumeni jikinta tana sauke wani nannauyan numfashi daya bani mamaki matuƙar gaya, itama Ummah ƙarama saita riƙo hannuna da faɗin, “ALLAH yaymiki albarka kinji, lallai ƙaunar da muke miki da gaske ta wuce ta surukuta kawai”. Ban fahimci zancen nataba nidai, na ɗago daɗan satar kallon Ummah babba da naga kamar tana hawaye. Kaina na maida a ƙasa nace, “Bara na kawo muku ruwa”.
Ummah ƙarama da itama na ga tana share hawayen tace, “Bara mu fara yin salla ɗiyata, dan ta riskemu a hanya saboda go-slow ɗin garin nan da baya ƙarewa”. Kaina na jinjina musu tare da miƙewa nai musu jagora har cikin ɗakina. Sai da na saka musu abin salla sannan na fito dan na basu waje suyi.
Kwance na iske Nabeelah na danna waya, na zauna kujerar dake kallonta, “K bazakiyi sallarba madam?”. Wayar ta janye daga fuskarta tana tashi zaune, “Aini shehi yamin”. Nace, “Okay to acigaba da gashi”. Dariya ta sanya tana ƙoƙarin komawa ta kwanta, ni kuma na miƙe dan naje na shirya abincin a dining, harna miƙe na dawo na sake zama. “Nabeelah niko kinga abinda na gani kuwa? Saifa naga kamar su Ummah kuka sukai?”. Kallona tai tana murmushi, “Nima dai ba komai na saniba akai, amma tabbas akwai wani abu da suka sani game dake wanda na lura shine dalilin kukan nasu”. Babu shiri na koma na zauna a kujerar sosai ina faɗin, “Game dani kuma Nabeelah?”. “Lah bafa wani abu mara ƙyau bane naga kamar kin ruɗe”. Ajiyar zuciya naɗan sauke duk da bawai na gamsu da amsar tata bane, na sake miƙewa na nufi kitchen. Abincin dana shirya a kuloli na fara fiddowa, ganin hakan Nabeelah ta taso ta tayani muka shirya komai. Falon muka sake dawowa muka zauna, Nabeelah ta fara zubamin surutu, nidai nawa murmushi ne, wani gurin kuma nakan jinjina wautarta sosai. zamanmu baifi da mintuna goma ba su Ummah suka fito, miƙewa nai ina musu sannu. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka amsamin suna zama. Ina fara zuba musu ruwan dana ajiye ya shigo falon da sallama.
Tsokanarsa suka shigayi da faɗin ga ango ga ango. Yay murmushi mai sauti cike da girmamawa yace, “Sannunku da zuwa Ummahs, har ina tunanin kiranku a waya sai kuma na duba naga nama bar wayar a gida”.
Ummah ƙarama tace, “Wlhy Go-slow ne ya riƙemu Son, amma da tuni mun iso ai”. Ledar hannunsa na amsa ina masa sannu murya ƙasa-ƙasa, ban jira amsarsaba ko kallonsa nabar wajen.
Jay daya ɗan bita da kallo ya zauna yana amsa gaisuwar da Nabeelah ke masa, kafin ya gaida iyayen nasa da keta tsokanarsa yayi ƙiba a kwana uku kacal. Shidai murmushi kawai yake musu bai iya cewa komai.
Nabeelah data san halin kayanta kuwa tuni ta miƙe tabi bayan Bilkisu dake kitchen tana wanke fruits ɗin daya shigo dashi. Tare suka ƙarasa suka fito.
Koda nazo na sanar musu cewar ga abinci sai Ummah babba ta hau faɗa akan miyasa zan
fara girki, ai sai nayi sati biyu sannan. Murmushi nidai nakeyi kawai kaina a ƙasa, shima dai banji yace wani abu ba. Sai da ta gama faɗanne sannan naji ya bata haƙuri da cewar, “Ummah karki damu ai gara tayi, dan bazai yuwu muyita wahal dake ba”. Ummah tace, “Minene wani abin wahala anan, aida nasan zatai girkin dana kira nace karma ta fara”.
Shidai ya lallaɓasu akan suzo suci abinci, daga baya saita cigaba da faɗan. Dariya Ummah ƙarama da Nabeelah sukayi jin furcinsa, nima dai saida na murmusa. Ni da Nabeelah muka zuzzuba musu abincin yanda kowa yake buƙata, Nabeelah ma ta zuba nata ta zauna, niko sai nai ƙoƙarin barin wajen, hannuna Ummah ta kamo ta zaunar dani a kujerar kusa da ita, “Maza zauna kici abinci, kina nufin mu kaɗai zakima wannan wahalar”. Kaina a ƙasa nace, “Ummah ai na ƙoshi, in ALLAH ya kaimu anjima zanci”. Bata saurareni ba ta hau ɗiba da cokalinta ta fara bani, bazan iya mata musu ba, dan haka dole na ringa amsa a kunyace, Nabeelah nata mana dariya ƙasa-ƙasa dan tana tsoron yi yaci ƙaniyarta. Dana ɗago saina kamashi yana kallonmu, hakan yasa na ƙara takura sosai. Ummah bata barniba saida ta tabbatar cikina yayi ƙat da abincin nan, suma sukaci sosai suna santi da sakamin albarka da yaba ƙoƙari na.
Bayan mun kammala Nabeelah ta tayani gyara wajen, shi kuma ya zagaya dasu lungu da saƙo na gidan, inajin yanda suketa yaba gidan da jinjina halin girma irin nasu Ummu, a yanda suka hidimtamin babu dangin iya babu na baba sun cancanci yabawa mai girman gaske da ƙyaƙyƙyawar addu'a.
A falon Jawaad su Umma suka yada zango, inda suka shiga tattaunawa akan batun Bilkisu da kuma kamannin Anuwar dana Jay. su Ummah sun dage akan cikin satin nan zasuje saudia domin ganin Umm-Anum, dan sunce lallai sunaji a jikinsu kamaninsa da Anuwar yafi ƙarfin kamanni, sunce zasu sanarma Alhaji babba dan su ɗunguma gaba ɗaya su tafi.
Murmushi Jay yay yana gyara zama da fuskantar iyayen nasa. “Ummah banƙi ta takuba kam, amma sai nake ganin kamar dai kubari na fara zuwa tukunna, dan kunga bamu da tabbas hasashe kawai mukeyi, shima baba karmu sanar masa tukunna, yana a shekarun da baya buƙatar irin wannan ruɗanin a halin yanzun, yanzu haka da kunga yanda hankalinsa ke a tashe akan zancen Miemaa da zakusha mamaki, yana dannewane kawai, to kunga abin zai haɗe masa biyu. Insha ALLAH zanje masarauta nima anjima domin sakejin bayani dangane dasu yaran, duk da dai Miemaa tamin bayanin abubuwa da dama game da mamansun”.
Duk sun gamsu da jawabinsa, sun kuma yi masa addu'ar fatan nasara, amma ita Ummah babba ma tariga ta tabbatar musu da tanaji a ranta kamanin nan bazasu zama kamanni na haka nanba, ita wlhy jima take kamar tai tsuntsuwa ta ganta a saudia. Shi dai Jay ya cigaba da lallaɓasu dan yanason abi komai a sannu kodan maganar Bilkisu data sanar masa tana zargin akwai sihiri a cikin al'amarin.
Sun cigaba da tattanawa har zuwa la'asar, Jay ya fita salla su kuma sukai tasu a gida. Ƙyaututtukan da duk suka kawoma Bilkisu duk suka bata, kafin suyi shirin komawa.
Godiya naita musu dukda bansan mike a cikiba har sai da Ummah tace ya isa haka nan, da ya dawo daga salla shima na sanar masa, shima dai godiyar yayi.
Har bakin mota nai musu rakkiya da bama fadila nima tsarabar dana haɗa musu ta turaren wuta da fruits ɗin da basu sha ba sai kajin dana gasa guda uku na naɗesu batare da shima ya sani ba. Sai da suka fice daga gidan sannan muka koma cikin gida. Hannuna ya kama ya zaunar dani a kusa da shi yana faɗin, “Sannu da ƙoƙari Miemaa, nagode sosai da yanda kika karrama ahalina”. Murmushi nai masa, nace, “Nima ai ahalina ne yanzun, dan ƴan uwanka nawane, iyayena ne yazama dole a gareni na girmamasu, dan haka ka dainamin godiya dan ALLAH”. Baice komaiba sai jawoni da yay na haye saman jikinsa, ya sauke siririyar ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa. luf na kwanta nima ina shaƙar ƙamshinsa, gashi daman barci nakeji sosai, ai tuni na fara lumshe idanu.
Ɗagoni yay yana kallon fuskata, ya saka hannunsa ya shafi kumatuna, “Badai barciba ko?”. Buɗe idanun nawa nayi kaɗan na kallesa, g
anin ni yake kallo saina maidasu ƙasa da yunƙurin tashi daga jikin nasa, “ALLAH barci nakeji”. Zamansa ya gyara sosai yana kallona, sai dai yaƙi cewa komai, jinai idanun nasa sunmin yawa, dan haka nace, “Ko zaka ƙara cin abinci ne”. “Uhm, amma ba wancan ba” ya faɗa yana nuna Dining. Da mamaki na kallesa sosai, “To wanne? Ko wani za'a dafa maka?”. Hannuna ya kamo ya matso dani jikinsa sosai, a hankali kamar baya son yin magana yace, “Zona faɗa miki wanda nake so”. Yay maganar yana ɗaura kansa saman wuyana, yanda yake busan iskar numfashinsa a saman wuyan ya saka tsigar jikina tashi, na cije bakina da haɗiye yawu da ƙyar, abinda ya gwargwaɗa min a cikin kune ne ya sakani zabura naɗan kallesa, sai kawai na miƙe nabar wajen da ɗan gudu.
Lumshe idanu Jay yay yana wani sassanyan murmushi, yabi hanyar falonta da kallo yana sauke ajiyar zuciya, ganin idan ya cigaba da zama a gidan jikinsa zai cigaba da mutuwa sai ya miƙe, ɗakinsa ya shiga, mintuna kusan goma ya fito ya nufi nata.
Murmushi mukaima juna, ta ƙaraso ta rungumeni tana faɗin “Amarsu ta ango mai daɗin suna, bara na faɗa a hankali kar yauma nai suɓutar baki ya jini ya markaɗa”. Dariya ta bani sosai, dan haka na shiga yi. “Hum ke dariyama abin ya baki, wlhy kaɗan daga aikinsa yamin casar gyaɗa indai yayanmu ne. Ina fata baya nan?”. Toilet na nuna mata da ahannu ina faɗin, “Yana ciki kuwa”. Sosai ta waro idanu waje da faɗin, “Na shiga Uku dan ALLAH da gaske kikeyi?”. Yanda ta rikice ɗinne ya sakani sakeyin murmushi, na ajiye abin sallar dana linke, “Wai ke kaɗai kikazo ne?”. “A'a ni da su Ummah ne fa, suna falo”. Ban bata amsaba na fito batare dana cire hijjabin ba.
Tunda na fito suka zubamin idanu har abin ya bani kunya, na ƙarasa inda suke kaina a ƙasa, har ƙasa na durƙusa inai musu sannu da zuwa. Cikin fara'a suka amsamin har suna haɗa baki wajan faɗin nazo garesu. A kunyace na kuma tashi naje gabansu dab zan sake tsugunnawa Ummah babba ta riƙoni, tsakkiyarsu ta zaunar dani tare da rungumeni jikinta tana sauke wani nannauyan numfashi daya bani mamaki matuƙar gaya, itama Ummah ƙarama saita riƙo hannuna da faɗin, “ALLAH yaymiki albarka kinji, lallai ƙaunar da muke miki da gaske ta wuce ta surukuta kawai”. Ban fahimci zancen nataba nidai, na ɗago daɗan satar kallon Ummah babba da naga kamar tana hawaye. Kaina na maida a ƙasa nace, “Bara na kawo muku ruwa”.
Ummah ƙarama da itama na ga tana share hawayen tace, “Bara mu fara yin salla ɗiyata, dan ta riskemu a hanya saboda go-slow ɗin garin nan da baya ƙarewa”. Kaina na jinjina musu tare da miƙewa nai musu jagora har cikin ɗakina. Sai da na saka musu abin salla sannan na fito dan na basu waje suyi.
Kwance na iske Nabeelah na danna waya, na zauna kujerar dake kallonta, “K bazakiyi sallarba madam?”. Wayar ta janye daga fuskarta tana tashi zaune, “Aini shehi yamin”. Nace, “Okay to acigaba da gashi”. Dariya ta sanya tana ƙoƙarin komawa ta kwanta, ni kuma na miƙe dan naje na shirya abincin a dining, harna miƙe na dawo na sake zama. “Nabeelah niko kinga abinda na gani kuwa? Saifa naga kamar su Ummah kuka sukai?”. Kallona tai tana murmushi, “Nima dai ba komai na saniba akai, amma tabbas akwai wani abu da suka sani game dake wanda na lura shine dalilin kukan nasu”. Babu shiri na koma na zauna a kujerar sosai ina faɗin, “Game dani kuma Nabeelah?”. “Lah bafa wani abu mara ƙyau bane naga kamar kin ruɗe”. Ajiyar zuciya naɗan sauke duk da bawai na gamsu da amsar tata bane, na sake miƙewa na nufi kitchen. Abincin dana shirya a kuloli na fara fiddowa, ganin hakan Nabeelah ta taso ta tayani muka shirya komai. Falon muka sake dawowa muka zauna, Nabeelah ta fara zubamin surutu, nidai nawa murmushi ne, wani gurin kuma nakan jinjina wautarta sosai. zamanmu baifi da mintuna goma ba su Ummah suka fito, miƙewa nai ina musu sannu. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka amsamin suna zama. Ina fara zuba musu ruwan dana ajiye ya shigo falon da sallama.
Tsokanarsa suka shigayi da faɗin ga ango ga ango. Yay murmushi mai sauti cike da girmamawa yace, “Sannunku da zuwa Ummahs, har ina tunanin kiranku a waya sai kuma na duba naga nama bar wayar a gida”.
Ummah ƙarama tace, “Wlhy Go-slow ne ya riƙemu Son, amma da tuni mun iso ai”. Ledar hannunsa na amsa ina masa sannu murya ƙasa-ƙasa, ban jira amsarsaba ko kallonsa nabar wajen.
Jay daya ɗan bita da kallo ya zauna yana amsa gaisuwar da Nabeelah ke masa, kafin ya gaida iyayen nasa da keta tsokanarsa yayi ƙiba a kwana uku kacal. Shidai murmushi kawai yake musu bai iya cewa komai.
Nabeelah data san halin kayanta kuwa tuni ta miƙe tabi bayan Bilkisu dake kitchen tana wanke fruits ɗin daya shigo dashi. Tare suka ƙarasa suka fito.
Koda nazo na sanar musu cewar ga abinci sai Ummah babba ta hau faɗa akan miyasa zan
fara girki, ai sai nayi sati biyu sannan. Murmushi nidai nakeyi kawai kaina a ƙasa, shima dai banji yace wani abu ba. Sai da ta gama faɗanne sannan naji ya bata haƙuri da cewar, “Ummah karki damu ai gara tayi, dan bazai yuwu muyita wahal dake ba”. Ummah tace, “Minene wani abin wahala anan, aida nasan zatai girkin dana kira nace karma ta fara”.
Shidai ya lallaɓasu akan suzo suci abinci, daga baya saita cigaba da faɗan. Dariya Ummah ƙarama da Nabeelah sukayi jin furcinsa, nima dai saida na murmusa. Ni da Nabeelah muka zuzzuba musu abincin yanda kowa yake buƙata, Nabeelah ma ta zuba nata ta zauna, niko sai nai ƙoƙarin barin wajen, hannuna Ummah ta kamo ta zaunar dani a kujerar kusa da ita, “Maza zauna kici abinci, kina nufin mu kaɗai zakima wannan wahalar”. Kaina a ƙasa nace, “Ummah ai na ƙoshi, in ALLAH ya kaimu anjima zanci”. Bata saurareni ba ta hau ɗiba da cokalinta ta fara bani, bazan iya mata musu ba, dan haka dole na ringa amsa a kunyace, Nabeelah nata mana dariya ƙasa-ƙasa dan tana tsoron yi yaci ƙaniyarta. Dana ɗago saina kamashi yana kallonmu, hakan yasa na ƙara takura sosai. Ummah bata barniba saida ta tabbatar cikina yayi ƙat da abincin nan, suma sukaci sosai suna santi da sakamin albarka da yaba ƙoƙari na.
Bayan mun kammala Nabeelah ta tayani gyara wajen, shi kuma ya zagaya dasu lungu da saƙo na gidan, inajin yanda suketa yaba gidan da jinjina halin girma irin nasu Ummu, a yanda suka hidimtamin babu dangin iya babu na baba sun cancanci yabawa mai girman gaske da ƙyaƙyƙyawar addu'a.
A falon Jawaad su Umma suka yada zango, inda suka shiga tattaunawa akan batun Bilkisu da kuma kamannin Anuwar dana Jay. su Ummah sun dage akan cikin satin nan zasuje saudia domin ganin Umm-Anum, dan sunce lallai sunaji a jikinsu kamaninsa da Anuwar yafi ƙarfin kamanni, sunce zasu sanarma Alhaji babba dan su ɗunguma gaba ɗaya su tafi.
Murmushi Jay yay yana gyara zama da fuskantar iyayen nasa. “Ummah banƙi ta takuba kam, amma sai nake ganin kamar dai kubari na fara zuwa tukunna, dan kunga bamu da tabbas hasashe kawai mukeyi, shima baba karmu sanar masa tukunna, yana a shekarun da baya buƙatar irin wannan ruɗanin a halin yanzun, yanzu haka da kunga yanda hankalinsa ke a tashe akan zancen Miemaa da zakusha mamaki, yana dannewane kawai, to kunga abin zai haɗe masa biyu. Insha ALLAH zanje masarauta nima anjima domin sakejin bayani dangane dasu yaran, duk da dai Miemaa tamin bayanin abubuwa da dama game da mamansun”.
Duk sun gamsu da jawabinsa, sun kuma yi masa addu'ar fatan nasara, amma ita Ummah babba ma tariga ta tabbatar musu da tanaji a ranta kamanin nan bazasu zama kamanni na haka nanba, ita wlhy jima take kamar tai tsuntsuwa ta ganta a saudia. Shi dai Jay ya cigaba da lallaɓasu dan yanason abi komai a sannu kodan maganar Bilkisu data sanar masa tana zargin akwai sihiri a cikin al'amarin.
Sun cigaba da tattanawa har zuwa la'asar, Jay ya fita salla su kuma sukai tasu a gida. Ƙyaututtukan da duk suka kawoma Bilkisu duk suka bata, kafin suyi shirin komawa.
Godiya naita musu dukda bansan mike a cikiba har sai da Ummah tace ya isa haka nan, da ya dawo daga salla shima na sanar masa, shima dai godiyar yayi.
Har bakin mota nai musu rakkiya da bama fadila nima tsarabar dana haɗa musu ta turaren wuta da fruits ɗin da basu sha ba sai kajin dana gasa guda uku na naɗesu batare da shima ya sani ba. Sai da suka fice daga gidan sannan muka koma cikin gida. Hannuna ya kama ya zaunar dani a kusa da shi yana faɗin, “Sannu da ƙoƙari Miemaa, nagode sosai da yanda kika karrama ahalina”. Murmushi nai masa, nace, “Nima ai ahalina ne yanzun, dan ƴan uwanka nawane, iyayena ne yazama dole a gareni na girmamasu, dan haka ka dainamin godiya dan ALLAH”. Baice komaiba sai jawoni da yay na haye saman jikinsa, ya sauke siririyar ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa. luf na kwanta nima ina shaƙar ƙamshinsa, gashi daman barci nakeji sosai, ai tuni na fara lumshe idanu.
Ɗagoni yay yana kallon fuskata, ya saka hannunsa ya shafi kumatuna, “Badai barciba ko?”. Buɗe idanun nawa nayi kaɗan na kallesa, g
anin ni yake kallo saina maidasu ƙasa da yunƙurin tashi daga jikin nasa, “ALLAH barci nakeji”. Zamansa ya gyara sosai yana kallona, sai dai yaƙi cewa komai, jinai idanun nasa sunmin yawa, dan haka nace, “Ko zaka ƙara cin abinci ne”. “Uhm, amma ba wancan ba” ya faɗa yana nuna Dining. Da mamaki na kallesa sosai, “To wanne? Ko wani za'a dafa maka?”. Hannuna ya kamo ya matso dani jikinsa sosai, a hankali kamar baya son yin magana yace, “Zona faɗa miki wanda nake so”. Yay maganar yana ɗaura kansa saman wuyana, yanda yake busan iskar numfashinsa a saman wuyan ya saka tsigar jikina tashi, na cije bakina da haɗiye yawu da ƙyar, abinda ya gwargwaɗa min a cikin kune ne ya sakani zabura naɗan kallesa, sai kawai na miƙe nabar wajen da ɗan gudu.
Lumshe idanu Jay yay yana wani sassanyan murmushi, yabi hanyar falonta da kallo yana sauke ajiyar zuciya, ganin idan ya cigaba da zama a gidan jikinsa zai cigaba da mutuwa sai ya miƙe, ɗakinsa ya shiga, mintuna kusan goma ya fito ya nufi nata.