Sashe 45
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ana ƙoƙarin shiga sallah Jawaad ya fito a gaggauce cikin jallabiya ruwan siminti, sai ƙamshin turaren kakansa yake mai sanyin daɗi, tare suka tafi massalaci dan Alhaji Baba yayi alwala a toilet ɗin falo. Koda aka idar sai sukai zamansu acan har isha'i, bayan sun fitone Alhaji baba yay sallama da mutane da neman gafara ga wanda ya ɓatamawa bisaga al'adarsa, dan acewarsa bai zama lallai yana cikin jerin masu tashi suga safiyar gobe ba, shiyyasa duk bayan kowacce sallar isha'i yakanyi sallama da maƙwaftansa da neman gafararsu kafin ya shige gida. Sun iske Nabeelah ta kawo masa abinci kamar kullum, tunda ta gaida Jay sau ɗaya ya amsa yay kwanciyarsa a doguwar kujera, sai hira suke ita da Alhaji Baba, zuwa takwas da rabi tai musu sallama ta tafi dan tare suke da driver dama. Tana fita Jawaad ya sakko ya shiga buɗe kulolin da aka jero cikin kwandon mai ƙyau daga gidan Ummah, tuwone kamar kullum dare da Alhaji baba ya wajabtama kansa, jay ya miƙe zuwa kicin ya ɗakko filet da cokali, tuwon alkamar ya dawo ya ɗiba da miyar ɗanyar kuɓewa, shidai Alhaji baba nata tsokanarsa da gwauro kafi tuzuru. Wani ya tanka wani yay shiru, sai kuma a hankali ya saki jikinsa sukai hira sosai kamar yanda Alhaji baba ya buƙata, cikin hikima kuma yake masa nasiha, sai wajen sha ɗaya suka kwanta, dan Jay yace anan zai kwana yau, da yayi sallar asuba sai ya wuce gida.
★★★★★★
Ƙarfe huɗu da rabi muka bar office, daga nan asibiti muka nufa, mun iske jikin aunty Shahudah kan babu daɗi, dan yanzunma dai saida tasha allurar barci. Anan muka zauna har magriba saboda kowa yana nan sannan muka tafi kamar yanda Dad ya bamu umarni. Har zuwa yanzun dai Yah Qaseem bashi da wata walwala, muna isa gida kuma kowa yay ɗakinsa, naji haushin ganin ɗakina kaca-kaca, yanda Aunty Aamilah ta tashi haka ta barminshi uwa turken jakai, gadon na fara gyarawa nai shara sannan na shiga wanka, dama gaba ɗaya a takure nake, saidai maganin da boss ya bani ya mugun taimaka mani, dan jina nake sakayau babu ciwon marar sai abinda ba'a rasaba. Kamar yanda na saba har alwala saida na ɗaura dukda ina fashin salla, sannan na fito nai shirin barci, gado na haye na buɗe data, dan munada meeting dasu Ummie akan bikin Nazifa, munyi nisa a firarmu
sosai Nazifa tai wata maganar data saka zuciyata bugawa lokaci guda, “Sisters wlhy akwai matsala, ko kunsan a daren jiya anyima jikar marka mai aikinmu fyaɗe, kuma kamar dai namu ne itama saida aka bugar da ita”. Ina gama karanta abinda Nazifa ta rubuta na saki wayar a kan gado jikina na wata irin rawa, a wani irin firgici maiban tsoro na tsinci kaina a ciki, na shiga waige-waige a cikin ɗakin tamkar mai tsoron ganin wani abu, a wani irin matsanancin ihu na shiga faɗin, “Ya isa!! Nace ya isa!!! Ya isa haka nan Pleaseeeeeee” na ƙarashe faɗa da sanyin murya ina fashewa da kuka, Aamilah Da Dad ne sukai rige-rigen shigowa ɗakin saboda jiyo sambatun Bilkisu.
Dad ya riƙo hannunta data tattare bedsheet ta matse a ciki yana faɗin, “Daughter! K daughter miya faru??”. Bilkisu ta kuma fashewa da kuka tana kallon Dad dake riƙe da hannunta, Aamilah a gefensa, “Dad dan ALLAH kuce dasu ya isa haka, su bari hakanan” ta cije baki tana zazzaro idanu cikin ficewar hayyaci ta fisge hannunta ta tashi zaune a kan gadon, ta bubbugashi da ƙarfi na alamun ɗaukar alwashi, kafin tacigaba da magana cikin kaushin murya, “Wlhy wlhy Dad, inhar basu dainaba, ni da hannuna saina kakkashesu, gunduwa-gunduwa zanyi da namansu naba karnukan office ɗinmu su cinye, kamar yanda suke bibiyarmu wlhy nima zan cigaba da bibiyarsu, subar ganina mace, duk mai hannu a ciki sai ya shiga uku a hannuna, wlhy halakashi zanyi Dad, saina halakashi” ta ƙare maganar da fashewa da kuka tana faɗawa jikin Aamilah.
Sam Dad bai fahimci komai daga zantukan Bilkisu ba dake fita a murɗe, yama fara tunanin yarinyarnan ko aljanune da ita, jiba jiya yanda suka bashi labarin an basu tsoro a gidan, kuma ita tafi kowa firgita da shiga ruɗani, ahankali ya juya ga ƙofa saboda jin motsi, Salman ne da Qaseem, Qaseem ya jiƙe sharkaf da zufa dukda fanka dake aiki a ɗakin, gashi idanunsa sun kaɗa sunyi jazur har ana iya hango yanda jijiyoyin kansa sukai ruɗu-ruɗu.
“Qaseem kaikuma mike damunka?” Dad ya faɗa da tsagwaron mamaki, Salman da shima dai jikin nasa a sanyaye yake ya kalli Qaseem tare da dafa kafaɗarsa, kallonsa Qaseem yayi shima, sai dai babu wanda ya iya cema ɗan uwansa komai, saima Qaseem ya zame hannun Salman a jikinsa ya juya ya fita daga ɗakin.
Dad ya sauke nannauyan numfashi, dan shifa al'amarin ƴaƴan nasa ya fara bashi matsanancin tsoro, shin mike faruwane haka wai?. Babu mai bashi amsa dan haka yay shiru kawai ya zubama Bilkisu dake shashshekar kuka a hankali idanu. Ita kanta Aamilah duk iskancin nan nata yau a firgice take, dan tsaf bata manta tsoratasun da akai jiyaba, hakan yasa Bilkisu na fara sambatu itace farkon jiyota.
Dad ya kamo hannun Bilkisu yana rabota da jikin Aamilah, “Bilkisu tashi ki faɗamin mike faruwa?”. Babu musu Bily ta tashi zaune, Dad ya sake cewa, “Miya farune? Jiya ance an tsorataku musamma k, yau kuma gashi mun jiyoki kinata sambatu?”. Hawayen daketa faman ziraro mata ta share.
Naɗan kalli Dad ƙaɗan na maida kaina ƙasa, cikin muryata data dishashe a yinin yau gaba ɗaya nace, “Dad fyaɗe akaima ƴar mai aikin gidansu Nazifa” shiru yay kawai yana kallona har nakusan sakanni ashirin, kafin ya girgiza kansa cikin wani yanayi yace, “To Bilkisu shine kuma kike irin wannan mahaukacin kukan?, ƴar gidan waye a cikin ƙawayen naki abin ya faru a gidansu?”. “Gidan Alhaji Sufyan magashi”. “To ALLAH ya kiyaye, ki kwantar da hankalinki shima ai zai ɗauki mataki, inake ina shiga irin wannan maganar ƴar ƙaramarki dake, sannan kuma ma k miye naki a ciki? Ai can matsalar family ɗinsuce, muma muji da tamu gatanan kinji”. Kaina kawai na ɗaga masa cikin tsantsar takaicin furucinsa, yaukam na sake girmama al'amarin Dad fiye da tunanina, miyasa shi kansa kawai ya sani sai ƴaƴansa? Yanzu da ace Aamilah ko aunty Shahudah akaimawa ai da bazaice hakaba ko, anya kuwa koda a kaina wannan abun ya faru Dad zai nuna damuwarsa kuwa?. Sosai gabana ya faɗi da zuwan wannan tunanin a cikin raina, nayi nisa sosai a tunanina har bansan lokacin dasu Dad suka bar ɗakinba, kawai juyawa nai na jini kwance a gado har an lulluɓeni da bargoma, a
unty Aamila na kwance a gefena da alama ta jima dayin barci ma, nasan badan tsoron da takejiba bazata taɓa zuwa ta raɓeniba.
Dad kam koda suka fita a falonsa na sama ya iske Qaseem zaune yana jiransa, da mamaki ya kallesa. “Kana nufin dama ba zuwa kai ka kwantaba?”. Kai Yah Qaseem ya jinjina alamar eh. Dad ya zauna kusa dashi cikin kulawa yace, “Mike faruwa?”. Kallonsa Qaseem yayi, murya a sanyaye yace, “Dad inason a saka ranar aurenmu ni da Bilkisu”. Shiru Dad yay kawai yana kallon Qaseem tamkar yaune ya fara ganinsa, kusan mintuna biyu kafin ya jinjina kansa, yace, “Shikenan za'ayi hakan, to amma ita kaji ra'ayinta akan ta shirya aure yanzun?”. Kai Qaseem ya jinjina, yace, “Munyi magana da ita ranar, dama dawowarka nake jira Dad, banason asa bikin da nisa kuma, karya wuce wata ɗaya”. Dad yay murmushi cike da tsokana yace, “A lallai wannan angon a shirye yake, yanzu dai kaga Ramadan baifi saura kwana goma sha uku ba ya rage mana, lokaci yazo a ƙure kenan, saimu saka bikin bayan salla kenan kamar da sati biyu, zan fara nemar dangin mahaifinta muyi magana dan wannan huruminsune dukda sun wofantar da al'amarinta, kaga sai a haɗa tare dana mamana kawai ayi a huta”. Fuskar Qaseem ɗauke da murmushi yace, “Shikenan Dad nagode sosai, ALLAH ya ƙara lafiya da nisan kwana”. “Amin ya rabbi” Dad ya faɗa yana mamaki a ransa yau Qaseem ya masa godiya akan abu, lallai kusanci da Bilkisu ya kawo cigaba a wani ɓangare na rayuwar yaransa, dan shikam bazai iya tuna randa yayma Qaseem abu yaymasa godiyaba balle akai ga addu'a ma baki ɗaya. Sallama Qaseem yay masa ya sakko, sai da ya leƙa ɗakin Bilkisu yaga sunyi barci ita da Aamilah sannan ya wuce sashensu zuciyarsa najin daɗin ya kusa mallakar bilynsa.
★★★★★★
A ɓangaren Jawaad kuwa bayan an idar da sallar asuba yanayin azkar ya fita daga massalacin, motsa jiki yaɗan zagayo ya koma gidan Alhaji baba, a falo ya iske tsohon zaune yana duba wani littafin addini, Jay ya gaidashi da girmamawa kafin su koma tsokanar juna, ganin lokaci yaja ya miƙe yana faɗin, “Bara nai wanka nazo naje gida na shirya daga can na wuce office”. Cikin zolaya Alhaji baba yace, “To agogo sarkin aiki”. Dariya Jay yayi yana miƙewa da faɗin, “Nikam sunayen da kake jeramin sun isa hakanan”. Alhaji baba yace, “To gwauro na daina”. Juyowa Jawaad yay zai bashi amsa hannunsa ya tanƙwaɓi ɗaya daga cikin hotunan da Alhaji baba ya jera saman wata ƙyaƙyƙyawar drawer dake hanyar shiga bedroom. A take hoton ya kifo ƙasa ya shiga bada ƙarar fashewa................✍
Gaisuwa da tarin fatan alkairi a gareku ƴan wattpad, wannan page ɗin yau nakune ku kaɗai, kuyi birgima a ciki ku more😂😘😘😘😍😍😍.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/2/2020, 6:24 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya
.
BOOK TWO
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 20
★★★★★★
Ƙarfe huɗu da rabi muka bar office, daga nan asibiti muka nufa, mun iske jikin aunty Shahudah kan babu daɗi, dan yanzunma dai saida tasha allurar barci. Anan muka zauna har magriba saboda kowa yana nan sannan muka tafi kamar yanda Dad ya bamu umarni. Har zuwa yanzun dai Yah Qaseem bashi da wata walwala, muna isa gida kuma kowa yay ɗakinsa, naji haushin ganin ɗakina kaca-kaca, yanda Aunty Aamilah ta tashi haka ta barminshi uwa turken jakai, gadon na fara gyarawa nai shara sannan na shiga wanka, dama gaba ɗaya a takure nake, saidai maganin da boss ya bani ya mugun taimaka mani, dan jina nake sakayau babu ciwon marar sai abinda ba'a rasaba. Kamar yanda na saba har alwala saida na ɗaura dukda ina fashin salla, sannan na fito nai shirin barci, gado na haye na buɗe data, dan munada meeting dasu Ummie akan bikin Nazifa, munyi nisa a firarmu
sosai Nazifa tai wata maganar data saka zuciyata bugawa lokaci guda, “Sisters wlhy akwai matsala, ko kunsan a daren jiya anyima jikar marka mai aikinmu fyaɗe, kuma kamar dai namu ne itama saida aka bugar da ita”. Ina gama karanta abinda Nazifa ta rubuta na saki wayar a kan gado jikina na wata irin rawa, a wani irin firgici maiban tsoro na tsinci kaina a ciki, na shiga waige-waige a cikin ɗakin tamkar mai tsoron ganin wani abu, a wani irin matsanancin ihu na shiga faɗin, “Ya isa!! Nace ya isa!!! Ya isa haka nan Pleaseeeeeee” na ƙarashe faɗa da sanyin murya ina fashewa da kuka, Aamilah Da Dad ne sukai rige-rigen shigowa ɗakin saboda jiyo sambatun Bilkisu.
Dad ya riƙo hannunta data tattare bedsheet ta matse a ciki yana faɗin, “Daughter! K daughter miya faru??”. Bilkisu ta kuma fashewa da kuka tana kallon Dad dake riƙe da hannunta, Aamilah a gefensa, “Dad dan ALLAH kuce dasu ya isa haka, su bari hakanan” ta cije baki tana zazzaro idanu cikin ficewar hayyaci ta fisge hannunta ta tashi zaune a kan gadon, ta bubbugashi da ƙarfi na alamun ɗaukar alwashi, kafin tacigaba da magana cikin kaushin murya, “Wlhy wlhy Dad, inhar basu dainaba, ni da hannuna saina kakkashesu, gunduwa-gunduwa zanyi da namansu naba karnukan office ɗinmu su cinye, kamar yanda suke bibiyarmu wlhy nima zan cigaba da bibiyarsu, subar ganina mace, duk mai hannu a ciki sai ya shiga uku a hannuna, wlhy halakashi zanyi Dad, saina halakashi” ta ƙare maganar da fashewa da kuka tana faɗawa jikin Aamilah.
Sam Dad bai fahimci komai daga zantukan Bilkisu ba dake fita a murɗe, yama fara tunanin yarinyarnan ko aljanune da ita, jiba jiya yanda suka bashi labarin an basu tsoro a gidan, kuma ita tafi kowa firgita da shiga ruɗani, ahankali ya juya ga ƙofa saboda jin motsi, Salman ne da Qaseem, Qaseem ya jiƙe sharkaf da zufa dukda fanka dake aiki a ɗakin, gashi idanunsa sun kaɗa sunyi jazur har ana iya hango yanda jijiyoyin kansa sukai ruɗu-ruɗu.
“Qaseem kaikuma mike damunka?” Dad ya faɗa da tsagwaron mamaki, Salman da shima dai jikin nasa a sanyaye yake ya kalli Qaseem tare da dafa kafaɗarsa, kallonsa Qaseem yayi shima, sai dai babu wanda ya iya cema ɗan uwansa komai, saima Qaseem ya zame hannun Salman a jikinsa ya juya ya fita daga ɗakin.
Dad ya sauke nannauyan numfashi, dan shifa al'amarin ƴaƴan nasa ya fara bashi matsanancin tsoro, shin mike faruwane haka wai?. Babu mai bashi amsa dan haka yay shiru kawai ya zubama Bilkisu dake shashshekar kuka a hankali idanu. Ita kanta Aamilah duk iskancin nan nata yau a firgice take, dan tsaf bata manta tsoratasun da akai jiyaba, hakan yasa Bilkisu na fara sambatu itace farkon jiyota.
Dad ya kamo hannun Bilkisu yana rabota da jikin Aamilah, “Bilkisu tashi ki faɗamin mike faruwa?”. Babu musu Bily ta tashi zaune, Dad ya sake cewa, “Miya farune? Jiya ance an tsorataku musamma k, yau kuma gashi mun jiyoki kinata sambatu?”. Hawayen daketa faman ziraro mata ta share.
Naɗan kalli Dad ƙaɗan na maida kaina ƙasa, cikin muryata data dishashe a yinin yau gaba ɗaya nace, “Dad fyaɗe akaima ƴar mai aikin gidansu Nazifa” shiru yay kawai yana kallona har nakusan sakanni ashirin, kafin ya girgiza kansa cikin wani yanayi yace, “To Bilkisu shine kuma kike irin wannan mahaukacin kukan?, ƴar gidan waye a cikin ƙawayen naki abin ya faru a gidansu?”. “Gidan Alhaji Sufyan magashi”. “To ALLAH ya kiyaye, ki kwantar da hankalinki shima ai zai ɗauki mataki, inake ina shiga irin wannan maganar ƴar ƙaramarki dake, sannan kuma ma k miye naki a ciki? Ai can matsalar family ɗinsuce, muma muji da tamu gatanan kinji”. Kaina kawai na ɗaga masa cikin tsantsar takaicin furucinsa, yaukam na sake girmama al'amarin Dad fiye da tunanina, miyasa shi kansa kawai ya sani sai ƴaƴansa? Yanzu da ace Aamilah ko aunty Shahudah akaimawa ai da bazaice hakaba ko, anya kuwa koda a kaina wannan abun ya faru Dad zai nuna damuwarsa kuwa?. Sosai gabana ya faɗi da zuwan wannan tunanin a cikin raina, nayi nisa sosai a tunanina har bansan lokacin dasu Dad suka bar ɗakinba, kawai juyawa nai na jini kwance a gado har an lulluɓeni da bargoma, a
unty Aamila na kwance a gefena da alama ta jima dayin barci ma, nasan badan tsoron da takejiba bazata taɓa zuwa ta raɓeniba.
Dad kam koda suka fita a falonsa na sama ya iske Qaseem zaune yana jiransa, da mamaki ya kallesa. “Kana nufin dama ba zuwa kai ka kwantaba?”. Kai Yah Qaseem ya jinjina alamar eh. Dad ya zauna kusa dashi cikin kulawa yace, “Mike faruwa?”. Kallonsa Qaseem yayi, murya a sanyaye yace, “Dad inason a saka ranar aurenmu ni da Bilkisu”. Shiru Dad yay kawai yana kallon Qaseem tamkar yaune ya fara ganinsa, kusan mintuna biyu kafin ya jinjina kansa, yace, “Shikenan za'ayi hakan, to amma ita kaji ra'ayinta akan ta shirya aure yanzun?”. Kai Qaseem ya jinjina, yace, “Munyi magana da ita ranar, dama dawowarka nake jira Dad, banason asa bikin da nisa kuma, karya wuce wata ɗaya”. Dad yay murmushi cike da tsokana yace, “A lallai wannan angon a shirye yake, yanzu dai kaga Ramadan baifi saura kwana goma sha uku ba ya rage mana, lokaci yazo a ƙure kenan, saimu saka bikin bayan salla kenan kamar da sati biyu, zan fara nemar dangin mahaifinta muyi magana dan wannan huruminsune dukda sun wofantar da al'amarinta, kaga sai a haɗa tare dana mamana kawai ayi a huta”. Fuskar Qaseem ɗauke da murmushi yace, “Shikenan Dad nagode sosai, ALLAH ya ƙara lafiya da nisan kwana”. “Amin ya rabbi” Dad ya faɗa yana mamaki a ransa yau Qaseem ya masa godiya akan abu, lallai kusanci da Bilkisu ya kawo cigaba a wani ɓangare na rayuwar yaransa, dan shikam bazai iya tuna randa yayma Qaseem abu yaymasa godiyaba balle akai ga addu'a ma baki ɗaya. Sallama Qaseem yay masa ya sakko, sai da ya leƙa ɗakin Bilkisu yaga sunyi barci ita da Aamilah sannan ya wuce sashensu zuciyarsa najin daɗin ya kusa mallakar bilynsa.
★★★★★★
A ɓangaren Jawaad kuwa bayan an idar da sallar asuba yanayin azkar ya fita daga massalacin, motsa jiki yaɗan zagayo ya koma gidan Alhaji baba, a falo ya iske tsohon zaune yana duba wani littafin addini, Jay ya gaidashi da girmamawa kafin su koma tsokanar juna, ganin lokaci yaja ya miƙe yana faɗin, “Bara nai wanka nazo naje gida na shirya daga can na wuce office”. Cikin zolaya Alhaji baba yace, “To agogo sarkin aiki”. Dariya Jay yayi yana miƙewa da faɗin, “Nikam sunayen da kake jeramin sun isa hakanan”. Alhaji baba yace, “To gwauro na daina”. Juyowa Jawaad yay zai bashi amsa hannunsa ya tanƙwaɓi ɗaya daga cikin hotunan da Alhaji baba ya jera saman wata ƙyaƙyƙyawar drawer dake hanyar shiga bedroom. A take hoton ya kifo ƙasa ya shiga bada ƙarar fashewa................✍
Gaisuwa da tarin fatan alkairi a gareku ƴan wattpad, wannan page ɗin yau nakune ku kaɗai, kuyi birgima a ciki ku more😂😘😘😘😍😍😍.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/2/2020, 6:24 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya
.
BOOK TWO
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 20