Sashe 49
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari safiyar alhamis, koda na tashi sai naci karo da abubuwa uku na farin ciki sun samemu, na farko samun sauƙin aunty Shahudah da har aka sallamo daga asibiti a daren jiya, na biyu maganar aurenta da Boss bayan ansha gumurzu ya amince da ƙyar saboda saka baki da kakansa yay a maganar, na uku tsaida maganar aurena da Yah Qaseem bayan Dad yaje wajen dangin mahaifina ya samesu ashe a jiya da rana, an tsaida aurenmu rana ɗaya dasu aunty Shahudah bayan salla ƙarama da sati biyu. Koba komai na samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya, dan nikam abubuwan dake faruwa na wannan lokacin suna matuƙar tsoratar dani da sakani firgici.
Ban ƙara tabbatar da ina son Yah Qaseem ba sai da aka tsaida ranar auren nan namu, shi kansa wani sake lallaɓani yake da ji dani a yau, dukkan abinda zai saka a gidansa kuma sanda muke tafiya wajen aiki ya nema shawarata, hakama kayan lefe saida yace na faɗi duk abinda nake buƙata, nidai kunyace ta kamani nace kawai na bashi zaɓi.
Sai dai abu mafi bani mamaki sune jama'ar gidanmu, musamman ma Momy, koda wasa ban taɓa tunanin zata goyi bayan aurena da Yah Qaseem ba, amma sai gashi koda a fuska bata nuna komaiba, saima shirye-shiryen gagarumin biki take na nunama sa'a akan babban ɗanta namiji da zata fara aurarwa. Yah Salman ne kawai da aunty Aamilah sun shafema idanunsu toka suna ƙara faɗaɗa hantarata da muguwar tsana akan ban cancanci zama matar ɗan uwansuba, ƙiri-ƙiri suke nuna hakan babu ko kara a wannan safiya, su Dad dai basu tsawatar musu ba, sannan basu goya musu bayansu ba, Yah Qaseem ne daifa da yay kansu da masifa har saida na roƙesa yayi haƙuri kafin yay shiru muka fito.
Tom nidai lamarinsu bai ɓatan rai, Alhmdllh tunda wanda zan zauna dashi yana sona, sannan iyayensama suna sona, dansu ƙannensa sunce basayi miye a ciki. A dangima dai akwai ƴan adawa, dan harda inna zainabu faɗa taitama Dad akan haɗani aure da ɗansa da yay kamar yanda Aunty Aamilah take faɗamin cikin gori da tsana, wai acewar inna Zainabu duk ƴaƴan manyan mutane masu kuɗi abokan Dad Qaseem ya rasa wadda zaiso saini? Haka taita jaraba tamkar itace ta haifi Dad ko yah Qaseem ɗin.
Duk wanda ya kalleni a office yau yasan banda wata damuwa tattare dani, dan waɗandama suke faɗin basa ganin dariyata yau sun gani harma da haƙorana, sai dai abinda ya ɗaure kaina da mamaki rai a ɓace naga Boss yau, dan koda nakai masa saƙo office baiko amsa gaisuwataba bayan sallama, sannan harna fito baice dani uffanba, idanunsa jajur, hakama jijiyar kansa duk sunyi ruɗu-ruɗu, duk sai naji babu daɗi, dan koba komai nima ranar danai ciwon mara ya bani kulawa da nuna damuwarsa a kaina, da alama kuma yau shima baida lafiyarne. Kasa zama nai waje guda nakoma office ɗinsa wai naji mike damunsa?, ‘kuji ƙarfin halifa irin nawa’ to aiko dai ban jiyota da daɗiba, dan fatattakoni yay tamakr zai gaggallamin marukama, ALLAH dai ya taimakeni na gudo. A ƙofar office ɗin mukaci karo da gimba kamar a rikice yake, nidai na bashi hanya ya shige ko gaisuwa bamuyiba, sauka nai ƙasa abina ina ƙunƙunai, ban sakebi takansaba har aka tashi aiki kuwa, sai a wajen Ummie nakejin gulmar wai taga boss ya fita ɗazun ransa a ɓace kamar zai tashi sama, ban kulataba ita da zancen nata, dan haushinsa nakeji akan abinda yaymin ɗazun..
Mamaki yay matuƙar kamani da muka isa gida na iske aunty Shahudahr data kwana biyu a asibiti rai a hannun ALLAH zaune suna hira mai nuni da tsare-tsaren biki, a raina nace, ‘Dama ciwon so ke damunta ashe, ta samu yanzu kunga ta miƙe harda tsara
biki kamar wani auren farko mtsoww’ na ƙare zancen cike da takaicin da bansan dalilinsaba nima. koda nai sallama basu amsaminba sai Momy kaɗai, sannunma ita kaɗai taimin hakama amsa gaisuwata, jikina duk sai yay sanyi, na wucesu ƙwalla na cikamin idanu, nasan dolene saina sake ɗaura ɗammarar haƙuri kam, dan matsalolin dama sukafi haka zasu biyo baya akan aurena da Yah Qaseem, har nai wanka na fito hawaye basu daina gudu a idanunaba, bayan sallar isha'i saima naji gidan tsitt, koda na leƙo iskewa nai duk fita sukai, daga ni sai Yah Qaseem dana iske a d/table yanacin abinci aka bari gidan da alama, zama nai mukaci tare muna ƴar hira, bayan mun kammala ya fita sashensu ni kuma na koma ɗaki nai shirin kwanciya dan barci nakeji kuma. Ina kwance har tara na dare barcin bai ɗaukeniba bankumaji motsin dawowar su Momy ba, sai naji wani tsoro na shigata a hankali, addu'a nai na kwanta ina fatan barci ya ɗaukeni mai nauyi kozan samu nutsuwa, UBANGIJI kuwa sai ya amsa roƙona barcin yay gaba dani babu zato.
‘Innalillahi...’ na ambata cikin farkin barci lokacin da abinda ya faru kwanaki huɗun da suka shuɗe dana manta shi gaba ɗaya a raina yake neman maimaita kansa a wannan daren tamkar ranarma a yau, a matuƙar gigice na farka jikina na mazarin rawa haɗe da bugawar zuciya tamkar zata faso ƙirjina ta fito, na fashe da kuka ina mutsu-mutsun fita daga jikinsa, sai dai hakan ta gagara a yau, dan yaymin riƙo bana wasaba, ga bakina an ɗaureshi da yanda bazan iya maganaba . Wata irin siririyar dariya ya saki a cikin kunnena, yauma dai muryar tamkar irin ta wancan ce, “Hhhh sannu Jaruma, yauma na dawo gareki, ranar kinyi nasarar korata ko, to kisa a ranki yau duk gudunki bazaki iya tsereminba, harke wacece da kika isa ruguzani? Nazo miki da lallami ranar amma kikaƙi saurarata, hhhhhh ke baki isa zama matar aureba yarinya saina karɓi abinda yake nawa, gashi kina a cikin yanayin danafi buƙata ma kina haila, kina bani shikenan, dan samunsa bada igiyar aure a kankiba shine yafi komai muhimmanci, bakuma zan sake bibiyarkiba dana samu cikar burina, hhhh bilkisu kece kammaluwar nasarata, kece ƙarashen nasarorina, da dukkan wahalhaluna na tsawon shekaru zan cika nasarata! Hhhh taya kike tunanin zan bari ki kufcemin, ɗaura miki igiyoyin aure tamkar ni aka ɗaure da igiyoyinne, taya zan bari hakan ta kasance ban amshi abinda yake cikamakin nasarorina ba?, abinda naketa bibiya tsahon shekaru kenan, karki yaudari kanki da tunanin ranar kin tsira yauma zaki tsiran, namiki shiri sosai a yau bilkisu, na shiryama wannan ranar, dan tana cikin damammakin da idan na rasasu babbar asarace a gareni, bana asara yarinya sai dai nasara! hhhhhhh!........”
Duk wannan maganganun da yakemin a cikin kunne na zama tamkar wata gawace a kwance, gangar jikina ne kawai a duniya amma numfashina da tunanina basa tare da duniyar, ba'a maganar zubar hawaye ma dan waɗanan dama ke sakasu fitowa, wata irin hasala zuciyata keyi da kumburar ɓacinrai irin wanda ban taɓa tunanin inada shiba, haka kawai yau nakejin zuciyata ta bushe dukda inajin tsoron ya samu nasarar da yake fatan kuwa, sai dai ban fasa gayama UBANGIJINA ba, addu'a nake kawai ina ƙiyasta tunanin shaidar dazan iya barma koma wanene wannan shaiɗanin, bazanyi sake irin na wancan darenba a yau insha ALLAHU, koda ace zaici galaba a kaina nima saina ribantu dashi da izinin UBANGIJINA.
Lokacin da naji ya sassauta min riƙon da yaymin yana shirin hawa kaina saina samu damar bada dukkan ƙarfina da yazomin daga mahaliccina wajen ƙoƙarin son tureshi, sam hakan bamai sauƙine a gareni, dan da alama ba ƙaramin mutum bane, danni sam kusani bana kawoshi a jerin aljanu, inada tabbacin mutum ne tamkar ni da rigar shaiɗanu. Wata sassanyar dariya maicin rai da nuna tsantsar mugunta da bushewar zuciya ya saki, tare da komawa gefena ya kwanta da faɗin, “Bara na baki damarki, kafin nai yaga-yaga dake yanda bazaki taɓa ganuwaba a safiyar gobe, na kula tausayin banza nake miki, tsaurin idonki yayi matuƙar yawa yarinyarnan”. Ya ƙare maganar da cire abinda ya ɗauremin bakina. Kukan zuci nake da babu hawaye ina kai masa du
ka ta ko ina da masa gargaɗi cikin zafin rai, “Karka cutar dani dan ALLAH, minai maka kake ƙoƙarin ɓatamin rayuwa?, kaji tausayin maraicina dan ALLAH, kobaka tsoron mahaliccinka ne? ina buƙatar zuwa da martabata gidan mijina tamkar kowacce mace mai mutunci, idan ka ketamin haddi wlhy ALLAH bazai barkaba, zan ƙare rayuwata ne wajen jifanka da munanan addu'oin da koka samu cikar burin naka saiya zame maka musiba, mugu azzalumi, ALLAH ya gagauta tona asirinka dama kosu waye kuke aikatama ƴaƴan mutane ɓarna, ALLAH ya ruguzaku sheɗanu, insha ALLAHU wutar jahannamace makomarku inhar baku tuba kun koma ga ALLAH ba tare da neman yafiyar bayin da kuke cutarwa, la'anannu masu ado da rigar musulunci suna cin dunduniyar bayin ALLAH, insha ALLAH bazaka cika burin nan nakaba koda kuwa kasamu nasara a kaina.........
Shiiiiii!!!! Ya faɗa yana dannemin baki tare da birkiceni ƙasa ya fallamin wani gigitaccen marin da komaina yay tsaye cak na wucin gadi kafin na ƙwalla ƙara, yasa hannu ya dannemin baki tare da kaina da azabar ƙarfi, kiciniya na fara dan harda hancina ya haɗa gaba ɗaya, tako ina yakushinsa nake dukda babu farce a hannuna sosai, hannunane ya sauka akan wuyansa, jin wani abu a ɗaure kamar sarƙan bit na samu damar fincikarsa da masifar ƙarfi saboda fita a hayyacina da nayi lokacin da numfashina ke gab da barin jikina................✍
Ƴan WhatsApp kuma ga naku saƙon, gaisuwa da fatan alkairi gareku baki ɗaya. Saura kuma yau naji wani yacema Yah Qaseem ko Dad kwarto🙄🚴🏼🚴🏼😍😍😍😘😘😘😍😍.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/4/2020, 2:23 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai cikin ƙaya
.
Book Two
.
Billyn Abdul:
Page 22
Ban ƙara tabbatar da ina son Yah Qaseem ba sai da aka tsaida ranar auren nan namu, shi kansa wani sake lallaɓani yake da ji dani a yau, dukkan abinda zai saka a gidansa kuma sanda muke tafiya wajen aiki ya nema shawarata, hakama kayan lefe saida yace na faɗi duk abinda nake buƙata, nidai kunyace ta kamani nace kawai na bashi zaɓi.
Sai dai abu mafi bani mamaki sune jama'ar gidanmu, musamman ma Momy, koda wasa ban taɓa tunanin zata goyi bayan aurena da Yah Qaseem ba, amma sai gashi koda a fuska bata nuna komaiba, saima shirye-shiryen gagarumin biki take na nunama sa'a akan babban ɗanta namiji da zata fara aurarwa. Yah Salman ne kawai da aunty Aamilah sun shafema idanunsu toka suna ƙara faɗaɗa hantarata da muguwar tsana akan ban cancanci zama matar ɗan uwansuba, ƙiri-ƙiri suke nuna hakan babu ko kara a wannan safiya, su Dad dai basu tsawatar musu ba, sannan basu goya musu bayansu ba, Yah Qaseem ne daifa da yay kansu da masifa har saida na roƙesa yayi haƙuri kafin yay shiru muka fito.
Tom nidai lamarinsu bai ɓatan rai, Alhmdllh tunda wanda zan zauna dashi yana sona, sannan iyayensama suna sona, dansu ƙannensa sunce basayi miye a ciki. A dangima dai akwai ƴan adawa, dan harda inna zainabu faɗa taitama Dad akan haɗani aure da ɗansa da yay kamar yanda Aunty Aamilah take faɗamin cikin gori da tsana, wai acewar inna Zainabu duk ƴaƴan manyan mutane masu kuɗi abokan Dad Qaseem ya rasa wadda zaiso saini? Haka taita jaraba tamkar itace ta haifi Dad ko yah Qaseem ɗin.
Duk wanda ya kalleni a office yau yasan banda wata damuwa tattare dani, dan waɗandama suke faɗin basa ganin dariyata yau sun gani harma da haƙorana, sai dai abinda ya ɗaure kaina da mamaki rai a ɓace naga Boss yau, dan koda nakai masa saƙo office baiko amsa gaisuwataba bayan sallama, sannan harna fito baice dani uffanba, idanunsa jajur, hakama jijiyar kansa duk sunyi ruɗu-ruɗu, duk sai naji babu daɗi, dan koba komai nima ranar danai ciwon mara ya bani kulawa da nuna damuwarsa a kaina, da alama kuma yau shima baida lafiyarne. Kasa zama nai waje guda nakoma office ɗinsa wai naji mike damunsa?, ‘kuji ƙarfin halifa irin nawa’ to aiko dai ban jiyota da daɗiba, dan fatattakoni yay tamakr zai gaggallamin marukama, ALLAH dai ya taimakeni na gudo. A ƙofar office ɗin mukaci karo da gimba kamar a rikice yake, nidai na bashi hanya ya shige ko gaisuwa bamuyiba, sauka nai ƙasa abina ina ƙunƙunai, ban sakebi takansaba har aka tashi aiki kuwa, sai a wajen Ummie nakejin gulmar wai taga boss ya fita ɗazun ransa a ɓace kamar zai tashi sama, ban kulataba ita da zancen nata, dan haushinsa nakeji akan abinda yaymin ɗazun..
Mamaki yay matuƙar kamani da muka isa gida na iske aunty Shahudahr data kwana biyu a asibiti rai a hannun ALLAH zaune suna hira mai nuni da tsare-tsaren biki, a raina nace, ‘Dama ciwon so ke damunta ashe, ta samu yanzu kunga ta miƙe harda tsara
biki kamar wani auren farko mtsoww’ na ƙare zancen cike da takaicin da bansan dalilinsaba nima. koda nai sallama basu amsaminba sai Momy kaɗai, sannunma ita kaɗai taimin hakama amsa gaisuwata, jikina duk sai yay sanyi, na wucesu ƙwalla na cikamin idanu, nasan dolene saina sake ɗaura ɗammarar haƙuri kam, dan matsalolin dama sukafi haka zasu biyo baya akan aurena da Yah Qaseem, har nai wanka na fito hawaye basu daina gudu a idanunaba, bayan sallar isha'i saima naji gidan tsitt, koda na leƙo iskewa nai duk fita sukai, daga ni sai Yah Qaseem dana iske a d/table yanacin abinci aka bari gidan da alama, zama nai mukaci tare muna ƴar hira, bayan mun kammala ya fita sashensu ni kuma na koma ɗaki nai shirin kwanciya dan barci nakeji kuma. Ina kwance har tara na dare barcin bai ɗaukeniba bankumaji motsin dawowar su Momy ba, sai naji wani tsoro na shigata a hankali, addu'a nai na kwanta ina fatan barci ya ɗaukeni mai nauyi kozan samu nutsuwa, UBANGIJI kuwa sai ya amsa roƙona barcin yay gaba dani babu zato.
‘Innalillahi...’ na ambata cikin farkin barci lokacin da abinda ya faru kwanaki huɗun da suka shuɗe dana manta shi gaba ɗaya a raina yake neman maimaita kansa a wannan daren tamkar ranarma a yau, a matuƙar gigice na farka jikina na mazarin rawa haɗe da bugawar zuciya tamkar zata faso ƙirjina ta fito, na fashe da kuka ina mutsu-mutsun fita daga jikinsa, sai dai hakan ta gagara a yau, dan yaymin riƙo bana wasaba, ga bakina an ɗaureshi da yanda bazan iya maganaba . Wata irin siririyar dariya ya saki a cikin kunnena, yauma dai muryar tamkar irin ta wancan ce, “Hhhh sannu Jaruma, yauma na dawo gareki, ranar kinyi nasarar korata ko, to kisa a ranki yau duk gudunki bazaki iya tsereminba, harke wacece da kika isa ruguzani? Nazo miki da lallami ranar amma kikaƙi saurarata, hhhhhh ke baki isa zama matar aureba yarinya saina karɓi abinda yake nawa, gashi kina a cikin yanayin danafi buƙata ma kina haila, kina bani shikenan, dan samunsa bada igiyar aure a kankiba shine yafi komai muhimmanci, bakuma zan sake bibiyarkiba dana samu cikar burina, hhhh bilkisu kece kammaluwar nasarata, kece ƙarashen nasarorina, da dukkan wahalhaluna na tsawon shekaru zan cika nasarata! Hhhh taya kike tunanin zan bari ki kufcemin, ɗaura miki igiyoyin aure tamkar ni aka ɗaure da igiyoyinne, taya zan bari hakan ta kasance ban amshi abinda yake cikamakin nasarorina ba?, abinda naketa bibiya tsahon shekaru kenan, karki yaudari kanki da tunanin ranar kin tsira yauma zaki tsiran, namiki shiri sosai a yau bilkisu, na shiryama wannan ranar, dan tana cikin damammakin da idan na rasasu babbar asarace a gareni, bana asara yarinya sai dai nasara! hhhhhhh!........”
Duk wannan maganganun da yakemin a cikin kunne na zama tamkar wata gawace a kwance, gangar jikina ne kawai a duniya amma numfashina da tunanina basa tare da duniyar, ba'a maganar zubar hawaye ma dan waɗanan dama ke sakasu fitowa, wata irin hasala zuciyata keyi da kumburar ɓacinrai irin wanda ban taɓa tunanin inada shiba, haka kawai yau nakejin zuciyata ta bushe dukda inajin tsoron ya samu nasarar da yake fatan kuwa, sai dai ban fasa gayama UBANGIJINA ba, addu'a nake kawai ina ƙiyasta tunanin shaidar dazan iya barma koma wanene wannan shaiɗanin, bazanyi sake irin na wancan darenba a yau insha ALLAHU, koda ace zaici galaba a kaina nima saina ribantu dashi da izinin UBANGIJINA.
Lokacin da naji ya sassauta min riƙon da yaymin yana shirin hawa kaina saina samu damar bada dukkan ƙarfina da yazomin daga mahaliccina wajen ƙoƙarin son tureshi, sam hakan bamai sauƙine a gareni, dan da alama ba ƙaramin mutum bane, danni sam kusani bana kawoshi a jerin aljanu, inada tabbacin mutum ne tamkar ni da rigar shaiɗanu. Wata sassanyar dariya maicin rai da nuna tsantsar mugunta da bushewar zuciya ya saki, tare da komawa gefena ya kwanta da faɗin, “Bara na baki damarki, kafin nai yaga-yaga dake yanda bazaki taɓa ganuwaba a safiyar gobe, na kula tausayin banza nake miki, tsaurin idonki yayi matuƙar yawa yarinyarnan”. Ya ƙare maganar da cire abinda ya ɗauremin bakina. Kukan zuci nake da babu hawaye ina kai masa du
ka ta ko ina da masa gargaɗi cikin zafin rai, “Karka cutar dani dan ALLAH, minai maka kake ƙoƙarin ɓatamin rayuwa?, kaji tausayin maraicina dan ALLAH, kobaka tsoron mahaliccinka ne? ina buƙatar zuwa da martabata gidan mijina tamkar kowacce mace mai mutunci, idan ka ketamin haddi wlhy ALLAH bazai barkaba, zan ƙare rayuwata ne wajen jifanka da munanan addu'oin da koka samu cikar burin naka saiya zame maka musiba, mugu azzalumi, ALLAH ya gagauta tona asirinka dama kosu waye kuke aikatama ƴaƴan mutane ɓarna, ALLAH ya ruguzaku sheɗanu, insha ALLAHU wutar jahannamace makomarku inhar baku tuba kun koma ga ALLAH ba tare da neman yafiyar bayin da kuke cutarwa, la'anannu masu ado da rigar musulunci suna cin dunduniyar bayin ALLAH, insha ALLAH bazaka cika burin nan nakaba koda kuwa kasamu nasara a kaina.........
Shiiiiii!!!! Ya faɗa yana dannemin baki tare da birkiceni ƙasa ya fallamin wani gigitaccen marin da komaina yay tsaye cak na wucin gadi kafin na ƙwalla ƙara, yasa hannu ya dannemin baki tare da kaina da azabar ƙarfi, kiciniya na fara dan harda hancina ya haɗa gaba ɗaya, tako ina yakushinsa nake dukda babu farce a hannuna sosai, hannunane ya sauka akan wuyansa, jin wani abu a ɗaure kamar sarƙan bit na samu damar fincikarsa da masifar ƙarfi saboda fita a hayyacina da nayi lokacin da numfashina ke gab da barin jikina................✍
Ƴan WhatsApp kuma ga naku saƙon, gaisuwa da fatan alkairi gareku baki ɗaya. Saura kuma yau naji wani yacema Yah Qaseem ko Dad kwarto🙄🚴🏼🚴🏼😍😍😍😘😘😘😍😍.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/4/2020, 2:23 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai cikin ƙaya
.
Book Two
.
Billyn Abdul:
Page 22