← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 145 OF 168

Sashe 145

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 2 min read

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*09044191709*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

*09033181070*

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥

Page 58

.................Muna tsaitsaye a inda aka bamu iznin tsayawa, Rose na mana bayani akan abinda zamu tunkara. Cikin takunsa na zaratan jami'ai da sukasan aikinsu ya fito Hafiz biye da shi da bullet proof jacket a hannunsa da alama ta boss ɗince, A boss ɗinsa dana fara sani yake yau, kura ga tsoro gaban tsoro, zakin da babu abinda ya sani face farauta a lokacin da yunwa ta ciyo cikinsa, gwarzon da baya alfarma ga dukkan wanda baima kansa alfarmarba, ɗaya tamkar da dubu abin buƙatar kowacce ƙasa, kowanne yanki, ko wacce zuri'a. Cike da izzarsa mai cike da tsantsar damuwa da ɓacin rai yazo gabanmu ya tsaya yana ƙare mana kallo ɗaya bayan ɗaya. Ya furzar da wani zazzafan huci daga bakinsa yana nunamu da yatsansa manuniya. “Kusa a ranku aiki zaku fita bakin rai bakin fama, sakacinku na nufin sakaci da ƙasarku, sakaci da yankinku, sakaci da garinku, sakaci da familys naku, idan kuka zama jajirtattu kun fido da martabar ƙasarku ne, yankunan ku, garinku da familys naku dama rayukanmu baki ɗaya da hukumarmu. Aikine mai cike da haɗari, ka kashe ko a kasheka wannan duk hukuncin ALLAH ne, shawarar kawai itace addu'a, ina fatan kuna faimta ta”.
       “Yes Sir!!!” muka faɗa cikin haɗa bakuna tare da buga ƙafa ƙasa mukai salute nashi. Juyawa yay ga Rose yay mata maganar da bamaji kafin ya kalli oga Hafiz shima. Shima maganar sukai suka bar wajen kuma zuwa inda su Sir Ahmad ke tsaitsaye tare da manyan jami'anmu da sojoji kusan goma sha biyar.
      Mudai muna nan tsaitsaye muna jiran umarni, a haka oga Jabeer ya zo wajen ya bamu damar zuwa mu shiga jirage masu saukar angulu (Helicopters) da za'ai tafiyar dasu. Mu matan an haɗamu ne a guda ɗaya, drivern mu ma ta kasance mace ce yarinya ƙarama da bazamu gaza sa'anni gudaba, sai baba ƙaura kaɗai daya kasance namiji a cikinmu wanda ya wuce muce masa uba kawai sai dai kakanmu. A yau babu zancen fira mu dasu Ummie, kowa addu'a ce ɗauke da bakinsa da fatan nasara, a can ƙarƙashin zuciya kuma tsorone da kowa ke ƙoƙarin dannewa. Sai da muka hangi tashin wasu jiragen kafin namu ya tashi, kusan duk sai da muka lumshe idanu kowa shi kaɗai yasan abinda ke a cikin ransa.
Chapter 145 · 0% Book details