Sashe 52
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Isowar motocin su Dad yay dai-dai da isowar motar gidan Sarki Sameer Saifudden dake ɗauke da ƴaƴansa ƴanmata a ciki, waɗanda suke cikin farin cikin samun fita yawo a wajen da basu saniba. Babu wanda ya fahimci su wanene su ɗin?, saboda kowa baya cikin hayyacinsa, ga matsananciyar hayaniyar data fiddo ƴan anguwa gaba ɗaya dake tashi daga gidan Dad.
Su Amaturrahman da kansu ke a kulle sunbi ayarin masu shiga gidan ganin shine gidan da Bilkisu ta tura musu address ɗinsa, sai dai gidan a harmutse yake har basu da damar fahimtar komaima. Isowar su Dad kuma ya sake harmutse gidan saboda ganin halin da Bilkisu da Shahudah ke ciki, ita kanta Momy bata cikin hayyacinta, ga Yah Qaseem can an wuce dashi asibiti shima, sai kawai Dad ya yanke jiki ya faɗi shima ganin ƴaƴan nasa biyu ga Qaseem kwance tamkar sun mutu.
Tashin hankali wanda ba'a saka maka rana kenan ke wanzuwa a wannan lokaci, a take aka kwashesu su uku aka fita dasu daga gidan zuwa asibiti domin ceto rayukansu, tuni suma sauran jama'a suka bisu a motoci, ƴan anguwa kuma suka shiga tattaunawa, danma anguwace ta manya kowa yana harkar dake gabansa babu ruwan wani da wani, amma a yanda lamarin yazo duk rashin shiga harkar junansu yazama dole a tattauna.
A wannan kace nace na ƴan anguwa su Amaturrahman suka fahimci wasu abubuwan, ciki kuwa harda fahimtar wadda sukazo gurintama tana cikin waɗanda aka fita dasu tamkar gawa daga gidan. Jikinsu a sanyaye suka koma mota driver ya jasu sukabar anguwar, Safah sai kuka take akan itafa subi suga wane asibiti aka kai Bilkisu, saida Amaturrahman tai kamar zata bugeta sannan ta nutsu tai musu shiru.
★★★★★
A ɓangaren su Jabeer kuwa tun dambarwar farko ta massallaci suka shiga ayarin ƴan neman Jawaad, sai dai komai kama dashima basu ganiba, bayan kuma a tare suka shigo dashi massallacin har aka tada salla, bayan an idarne suka nemesa suka rasa gaba ɗaya, a lokacin basu kawo komai a ransuba saboda ba'akai ga ɗaura aurenba, sai bayan an ɗaurane tsoro ya kamasu da tunanin kodai yanada masaniyar komai, to amma mizaisa yayi hakan kuma? Tunda sunsan halinsa sarai, suk son da yakema Bilkisu inhar babu wani dalili bazai zama mai aikata wannan abunda dake faruwaba domin kawai ya aureta, dolene su nemesa domin jin minene ke faruwa? Shine? Kokuwa shima bai saniba.
Sun fara da station, sai dai bai koma canɗinba kamar yanda kowa ya tabbatar, sannan gidansuma bai komaba, gidansa dake Abdul-aziz Yusif street nanma dai baima jeba, gaba ɗaya kuma sai kansu ya kulle ɓam akan komai.
Suna tsaitsaye a ƙofar gidansa na A.Y street ɗin saƙo ya shigo a wayar Jabeer. Jikinsa har rawa yake ya buɗe saƙon ganin Jawaad ɗinne ya turo.
“Kubar wahal da kanku wajen nemana, zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu zan bayyana, akwai aikin dana tafi yine, sannan karku zargeni akan abinda ya faru kamar yanda nasan rashin ganina anjima kaɗan zai ɗarsama wasu daga cikin ahalina, sam bani da hannu a ciki, akwai ɓoyayyen al'amarin danima ban sanshiba, lokacine ka
wai zai warwareshi. Inason kuyi duk yanda zakuyi kafin nan da awa uku a canjama Miemaa asibiti, dan nasamu labari yanzunan akwai matsalar data faru gidansu, karku barta ta kwana a asibitin da aka kaisu, karkuma wanda yasan kun ɗauketa daga asibitin har Alhaji baba”.
Kallan kallo aka komayi tsakanin Jabeer da Hafiz da Aliyu akan wannan saƙo na Jawaad da ya kuma ɗaure kansu akan wannan al'marin............✍
Yau dai gashinan na muku words 3700😲 kuci ku ƙoshi har safiyar litinin.😉👌🏼
Barkanku da juma'a, kar a manta da saka bayin ALLAH a addu'a dan ALLAH.
Ƴan facebook kuma ga naku saƙon, gaisuwa da fatan alkairi a gareku a duk duniyar da kuke.
Asha weekend lafiya my sweet fans, banda taƙaddama kuma.😂😂😘😘😘😍👍🏻👌🏼
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/7/2020, 6:52 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya
.
Book Two
.
Billyn Abdul:
Page 23
...............Tunkan su isa asibiti Dad ya farfaɗo, lokacin kuma da suka iso sun iske shima Qaseem ya farfaɗo, duk yanda Doctor yaso yayma Qaseem ɗin allurar barci danya huta yaƙi yarda, hakama Dad bai yarda ko dubashi ayiba, cayay babu damuwa su barshi. Bilkisu da Shahudah kawai aka shiga bama taimakon gaggawa, wanda daga farko Momy da catai baza'a duba Bilkisu ba, sai da Dad ya nuna mata ɓacin ransa a fili sannan ta nutsu, sai dai tanata ƙananun magana akan hakan.
Haka suma sauran family dake harabar asibitin saboda yawan da suke dashi aka tsaidasu nan kowa nata tofa albarkacin bakinsa, saidai mafi yawan kalamansu suna ɗora laifinne akan Bilkisu ce tai asiri. Yanda suke jifanta da mugayen kalamai dolene kaji tausayin Bilkisu, dan zaka ɗauka akan wata uwar mata suke maida yanda akayin. Hayaniyarsu ce ta saka Uncle Nasir cewa duk su wuce gida domin zamansu anan ɗin bashi da wani amfani. Badan sunso hakanba sukabi umarninsa.
Motocinsu na cikin fita su Jabeer suka iso asibitin suma domin cika umarnin Jawaad, mamakine yay masifar kamasu ganin wannan uwar gayya tamkar anan ake bikin. Shi Hafiz ma abin haushi ya bashi, ya buga tsaki cikin magana ƙasa-ƙasa yace, “Mutanen nan suna bani mamaki da al'amarinsu, to wannan gayyar kuma ta miye?”. Aliyu dake jinsa yace, “Kaima dai ka faɗa”.
Fitowa sukai a motar suka isa inda su Uncle Nasir ke tsaitsaye shi da Dad, da Uncle Sulaiman, sai Qaseem dake zaune cikin mota, Salman kuma yana zaune a saman motarne yanata latse-latse a waya tamkar baida wata damuwa a duniya. Gaishesu suka shigayi cikin girmamawa, tare da musu jajen abinda ya faru. Cike da kulawa suma suka amsa musu, Uncle Sulaiman yace, “Ina Jawaad ɗin shi yake? Tun ɗazun sai neman wayarsa muke taƙi shiga”. Duk kasa cewa komai sukai, dan kuwa suma dai basusan amsar daya dace ace sun basuba akan inda Jay yake, tunda suma basu saniba.
Uncle Nasir ya buɗe baki zaiyi magana ya fasa saboda shigowar motar Jawaad harabar asibitin, duk bin motar sukai da kallo harsu Jabeer, cike da mamaki suka tsatstsareshi da idanu lokacin daya fito a motar, yana sanye cikin wata dakakkiyar shadda ƴar ubansu ruwan zuma, sai maiƙo take, sosai ɗinkin ya zauna masa a jiki cif. Kosu kansu su Uncle Nasir ɗin ya musu ƙyau, dan kafin kaga Jawaad da manyan kaya akan daɗe saboda yanayin aiki, shiyyasa idan ya saka ɗin sai ya zama na musamman. Nufowa yay inda suke fuskarsa sam babu walwala, Qaseem da babu wanda ya lura da fitowarsa a mota yasha gabansa.
Kallonsa kawai Jay ya tsayayi batare daya iya cewa dashi komaiba, cike da ɓacin rai Qaseem yakai hannu zai shaƙosa, da sauri Jawaad ya ɗaga masa hannu, da watsa masa wani irin kallo mai razani dake gauraye da ɓacin rai, “Qaseem bani hanya”. “Anƙi a baka ɗin” Qaseem ya faɗa a zafafe. Jawaad baice komaiba ya raɓashi zai wuce, sake shan gabansa Qaseem yayi, Jawaad yay wani murmushi mai ciwo idanunsa na sake ƙanƙancewa tsabar masifar dake cin zuciyarsa, cikin wata irin muryar data bama Qaseem mamaki Jawaad yace, “Qassem ka riƙe girmanka, banason ka kaini bangon da zan sakaka dana sani mara amfani”. Kafin Qaseem yace wani Abu Uncle Sadiq ya ƙaraso wajen. “Ku wane irin shashancine haka kukem mutane anan?”. Jawaad baice komaiba, sai Qaseem ne ya bama Uncle Sadiq amsa da, “Uncle bazaka ganeba, wannan yaron munafukine, wlhy ko rantsuwa nai babu kaffara nasan yanada hannu akan wannan abun daya faru, kuma wlhy dolene ka saki Bilkisu a yau ɗin nan basai gobeba”. Murmushi Jawaad yay cikin taɓe baki ya raɓasu ya wuce batare da yace komaiba.
Ƙarasawa yay wajen su Uncle Nasir ya gaishesu, Uncle Nasir yace, “Kaikuwa ina kaje anta nemanka tun ɗazun Jawaad?”. “Amin afuwa Uncle, naje wani wajene”. “To amma saika kashe wayarka? Minene amfanin hakan?”. Jawaad dai baice komaiba.
Uncle Uwaisu yace, “Amma dai kasan miya faru a wajen ɗaurin aure ko?”. Cikin nuna halin ko in kula Jawaad yace, “Uhmmm na sani”. Ran Uncle Nasir a ɓace yace, “Ka sani? Amma shine dan wulaƙanci katafi wani waje ka barmu da nemanka?”.
Kafin Jawaad yace wani abu Uncle Sadiq yace, “Ya
ya nikam inaga wannan ba maganar nan bace, kamata yay muyi haƙuri yaranan su dawo cikin hayyacinsu sai ayi maganar a nutse a gida kamar zaifi, sannan kuma mu maida hankali wajen neman shi wancan angon da aka ɗaurama Shahudah aure dashi da ita Azeema take kowa”. Duk sunyi na'am da hakan, Jay ya kalli Uncle Nasir a wani yanayi, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru kawai.
Su Amaturrahman da kansu ke a kulle sunbi ayarin masu shiga gidan ganin shine gidan da Bilkisu ta tura musu address ɗinsa, sai dai gidan a harmutse yake har basu da damar fahimtar komaima. Isowar su Dad kuma ya sake harmutse gidan saboda ganin halin da Bilkisu da Shahudah ke ciki, ita kanta Momy bata cikin hayyacinta, ga Yah Qaseem can an wuce dashi asibiti shima, sai kawai Dad ya yanke jiki ya faɗi shima ganin ƴaƴan nasa biyu ga Qaseem kwance tamkar sun mutu.
Tashin hankali wanda ba'a saka maka rana kenan ke wanzuwa a wannan lokaci, a take aka kwashesu su uku aka fita dasu daga gidan zuwa asibiti domin ceto rayukansu, tuni suma sauran jama'a suka bisu a motoci, ƴan anguwa kuma suka shiga tattaunawa, danma anguwace ta manya kowa yana harkar dake gabansa babu ruwan wani da wani, amma a yanda lamarin yazo duk rashin shiga harkar junansu yazama dole a tattauna.
A wannan kace nace na ƴan anguwa su Amaturrahman suka fahimci wasu abubuwan, ciki kuwa harda fahimtar wadda sukazo gurintama tana cikin waɗanda aka fita dasu tamkar gawa daga gidan. Jikinsu a sanyaye suka koma mota driver ya jasu sukabar anguwar, Safah sai kuka take akan itafa subi suga wane asibiti aka kai Bilkisu, saida Amaturrahman tai kamar zata bugeta sannan ta nutsu tai musu shiru.
★★★★★
A ɓangaren su Jabeer kuwa tun dambarwar farko ta massallaci suka shiga ayarin ƴan neman Jawaad, sai dai komai kama dashima basu ganiba, bayan kuma a tare suka shigo dashi massallacin har aka tada salla, bayan an idarne suka nemesa suka rasa gaba ɗaya, a lokacin basu kawo komai a ransuba saboda ba'akai ga ɗaura aurenba, sai bayan an ɗaurane tsoro ya kamasu da tunanin kodai yanada masaniyar komai, to amma mizaisa yayi hakan kuma? Tunda sunsan halinsa sarai, suk son da yakema Bilkisu inhar babu wani dalili bazai zama mai aikata wannan abunda dake faruwaba domin kawai ya aureta, dolene su nemesa domin jin minene ke faruwa? Shine? Kokuwa shima bai saniba.
Sun fara da station, sai dai bai koma canɗinba kamar yanda kowa ya tabbatar, sannan gidansuma bai komaba, gidansa dake Abdul-aziz Yusif street nanma dai baima jeba, gaba ɗaya kuma sai kansu ya kulle ɓam akan komai.
Suna tsaitsaye a ƙofar gidansa na A.Y street ɗin saƙo ya shigo a wayar Jabeer. Jikinsa har rawa yake ya buɗe saƙon ganin Jawaad ɗinne ya turo.
“Kubar wahal da kanku wajen nemana, zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu zan bayyana, akwai aikin dana tafi yine, sannan karku zargeni akan abinda ya faru kamar yanda nasan rashin ganina anjima kaɗan zai ɗarsama wasu daga cikin ahalina, sam bani da hannu a ciki, akwai ɓoyayyen al'amarin danima ban sanshiba, lokacine ka
wai zai warwareshi. Inason kuyi duk yanda zakuyi kafin nan da awa uku a canjama Miemaa asibiti, dan nasamu labari yanzunan akwai matsalar data faru gidansu, karku barta ta kwana a asibitin da aka kaisu, karkuma wanda yasan kun ɗauketa daga asibitin har Alhaji baba”.
Kallan kallo aka komayi tsakanin Jabeer da Hafiz da Aliyu akan wannan saƙo na Jawaad da ya kuma ɗaure kansu akan wannan al'marin............✍
Yau dai gashinan na muku words 3700😲 kuci ku ƙoshi har safiyar litinin.😉👌🏼
Barkanku da juma'a, kar a manta da saka bayin ALLAH a addu'a dan ALLAH.
Ƴan facebook kuma ga naku saƙon, gaisuwa da fatan alkairi a gareku a duk duniyar da kuke.
Asha weekend lafiya my sweet fans, banda taƙaddama kuma.😂😂😘😘😘😍👍🏻👌🏼
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/7/2020, 6:52 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Ƙwai Cikin Ƙaya
.
Book Two
.
Billyn Abdul:
Page 23
...............Tunkan su isa asibiti Dad ya farfaɗo, lokacin kuma da suka iso sun iske shima Qaseem ya farfaɗo, duk yanda Doctor yaso yayma Qaseem ɗin allurar barci danya huta yaƙi yarda, hakama Dad bai yarda ko dubashi ayiba, cayay babu damuwa su barshi. Bilkisu da Shahudah kawai aka shiga bama taimakon gaggawa, wanda daga farko Momy da catai baza'a duba Bilkisu ba, sai da Dad ya nuna mata ɓacin ransa a fili sannan ta nutsu, sai dai tanata ƙananun magana akan hakan.
Haka suma sauran family dake harabar asibitin saboda yawan da suke dashi aka tsaidasu nan kowa nata tofa albarkacin bakinsa, saidai mafi yawan kalamansu suna ɗora laifinne akan Bilkisu ce tai asiri. Yanda suke jifanta da mugayen kalamai dolene kaji tausayin Bilkisu, dan zaka ɗauka akan wata uwar mata suke maida yanda akayin. Hayaniyarsu ce ta saka Uncle Nasir cewa duk su wuce gida domin zamansu anan ɗin bashi da wani amfani. Badan sunso hakanba sukabi umarninsa.
Motocinsu na cikin fita su Jabeer suka iso asibitin suma domin cika umarnin Jawaad, mamakine yay masifar kamasu ganin wannan uwar gayya tamkar anan ake bikin. Shi Hafiz ma abin haushi ya bashi, ya buga tsaki cikin magana ƙasa-ƙasa yace, “Mutanen nan suna bani mamaki da al'amarinsu, to wannan gayyar kuma ta miye?”. Aliyu dake jinsa yace, “Kaima dai ka faɗa”.
Fitowa sukai a motar suka isa inda su Uncle Nasir ke tsaitsaye shi da Dad, da Uncle Sulaiman, sai Qaseem dake zaune cikin mota, Salman kuma yana zaune a saman motarne yanata latse-latse a waya tamkar baida wata damuwa a duniya. Gaishesu suka shigayi cikin girmamawa, tare da musu jajen abinda ya faru. Cike da kulawa suma suka amsa musu, Uncle Sulaiman yace, “Ina Jawaad ɗin shi yake? Tun ɗazun sai neman wayarsa muke taƙi shiga”. Duk kasa cewa komai sukai, dan kuwa suma dai basusan amsar daya dace ace sun basuba akan inda Jay yake, tunda suma basu saniba.
Uncle Nasir ya buɗe baki zaiyi magana ya fasa saboda shigowar motar Jawaad harabar asibitin, duk bin motar sukai da kallo harsu Jabeer, cike da mamaki suka tsatstsareshi da idanu lokacin daya fito a motar, yana sanye cikin wata dakakkiyar shadda ƴar ubansu ruwan zuma, sai maiƙo take, sosai ɗinkin ya zauna masa a jiki cif. Kosu kansu su Uncle Nasir ɗin ya musu ƙyau, dan kafin kaga Jawaad da manyan kaya akan daɗe saboda yanayin aiki, shiyyasa idan ya saka ɗin sai ya zama na musamman. Nufowa yay inda suke fuskarsa sam babu walwala, Qaseem da babu wanda ya lura da fitowarsa a mota yasha gabansa.
Kallonsa kawai Jay ya tsayayi batare daya iya cewa dashi komaiba, cike da ɓacin rai Qaseem yakai hannu zai shaƙosa, da sauri Jawaad ya ɗaga masa hannu, da watsa masa wani irin kallo mai razani dake gauraye da ɓacin rai, “Qaseem bani hanya”. “Anƙi a baka ɗin” Qaseem ya faɗa a zafafe. Jawaad baice komaiba ya raɓashi zai wuce, sake shan gabansa Qaseem yayi, Jawaad yay wani murmushi mai ciwo idanunsa na sake ƙanƙancewa tsabar masifar dake cin zuciyarsa, cikin wata irin muryar data bama Qaseem mamaki Jawaad yace, “Qassem ka riƙe girmanka, banason ka kaini bangon da zan sakaka dana sani mara amfani”. Kafin Qaseem yace wani Abu Uncle Sadiq ya ƙaraso wajen. “Ku wane irin shashancine haka kukem mutane anan?”. Jawaad baice komaiba, sai Qaseem ne ya bama Uncle Sadiq amsa da, “Uncle bazaka ganeba, wannan yaron munafukine, wlhy ko rantsuwa nai babu kaffara nasan yanada hannu akan wannan abun daya faru, kuma wlhy dolene ka saki Bilkisu a yau ɗin nan basai gobeba”. Murmushi Jawaad yay cikin taɓe baki ya raɓasu ya wuce batare da yace komaiba.
Ƙarasawa yay wajen su Uncle Nasir ya gaishesu, Uncle Nasir yace, “Kaikuwa ina kaje anta nemanka tun ɗazun Jawaad?”. “Amin afuwa Uncle, naje wani wajene”. “To amma saika kashe wayarka? Minene amfanin hakan?”. Jawaad dai baice komaiba.
Uncle Uwaisu yace, “Amma dai kasan miya faru a wajen ɗaurin aure ko?”. Cikin nuna halin ko in kula Jawaad yace, “Uhmmm na sani”. Ran Uncle Nasir a ɓace yace, “Ka sani? Amma shine dan wulaƙanci katafi wani waje ka barmu da nemanka?”.
Kafin Jawaad yace wani abu Uncle Sadiq yace, “Ya
ya nikam inaga wannan ba maganar nan bace, kamata yay muyi haƙuri yaranan su dawo cikin hayyacinsu sai ayi maganar a nutse a gida kamar zaifi, sannan kuma mu maida hankali wajen neman shi wancan angon da aka ɗaurama Shahudah aure dashi da ita Azeema take kowa”. Duk sunyi na'am da hakan, Jay ya kalli Uncle Nasir a wani yanayi, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru kawai.