← Book details Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 168

Sashe 24

Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

       Jawaad kam a gajiye yake matuƙa. hakan yasa yana shigowa bayan yay brush da alwala yay adduar barci ya kwanta, bai wani jima da kwanciyaba barci yay gaba dashi, fitilar gefen gado ce kawai a kunne, itama ta ɓangare ɗaya, hakan yasa ɗakin yay dim babu haske sosai, bai kumayi dunɗum ba. Shahudah data murɗa ƙofar ta shigo a hankali ta sauke ajiyar zuciya tana mai shaƙar ƙamshin da ɗakin keyi, komai na Bb'n ta daban yake dana kowa, bata ganin fuskarsa, dan ya juya ma ƙofar bayane, sannan ya lulluɓa da bargo saboda uban AC'n daya ƙure ɗakin da shi, ‘ko tsoron murama bayayi’ ta faɗa tana ɗaukar remote ɗin acn ta rage ƙarfinsa.
       Jawaad da baisanma hidimar da akeba barcinsa yake hankali kwance da mafarki mai daɗi, hakan yasa yaketa faman sauke numfashi a hankali. Ya sauke ajiyar zuciya lokacin da Shahudah ta hawo gadon a hankali ta kwanto bayansa bayan ta ɗaga bargon ta shiga, itama ajiyar zuciyar ta sauke ƙwallan kewarsa na taruwar mata a idanu, jitake tamkar ta haɗiyesa ta hutama kawai. Cikin salon data shirya masa a wa

nnan dare ta fara yawo da hannunta a jikinsa, Jawaad dai bai motsaba, amma da alama jikinsa na karɓar saƙwannin Shahudah kamar yanda tai fata. Mafarkin da Jay keyi da saɓanin Shahudah yay dai-dai da abinda take masa a zahiri, hakanne yasa ta samu haɗin kan gangar jikinsa har takai ya gyara kwanciyarsa yana sake rungumeta, hakan yayma Huda daɗi kuwa, ta ƙara ƙaimi kan abinda takeyi, kamar wasa saiga tafiya tayi nisa a tsakaninsu, dan tuni ya fara maida mata murtanin sumbatarsa da takeyi.
          Yanda take sauke numfashi ne da sauri-sauri akan fuskarsa ya sakashi farkawa, dan kuwa tabbas wannan al'amarin ya wuce a mafarki kawai, a matuƙar razane ya hankaɗeta daga jikinsa yana ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihirraji'un. Wace ƴar iska ce haka ta shigomin ɗaki?”. Yay maganar yana ƙoƙarin kunna fitilar ɗakin.
       Shahudah daya jefar gefe duk da taji zafi tai ƙoƙarin tashi zaune tana sauke numfashi a gwame, hasken daya gauraye ɗakin ne ya basu damar ganin juna. Kansa ya dafe yana ƙara ambaton “Innalillahi....” Shahudah ta matso jikinsa tana neman kwantawa a kafaɗarsa ya sake tureta a fusace, “Wai ke wane irin dabbanci ne wannan? shin baki da hankaline Hudah?”. Tabbas maganganunsa sun mata zafi, amma saita daure cikin dakewa da tsiwarta tace, “Dan nazo wajen mijina zakacemin banda hankali?, to ka ɗauka ni da kai duk mun zama mahaukatan”.
      Karon farko Jawaad ya waro idanu waje, yace, “Miji!?, Hudah rashin ilimin addinin naki harya ƙara faɗaɗa haka? Kinga bani da lokacin wannan haukar tashi ki fitarmin daga sashe kafin na saɓa miki kamanni, kuma wlhy wannan yazama na farko na ƙarshe da zaki sake shigomin nan”.
       Kuka Shahudah ta saki, ta nuna kanta tana faɗin, “Yanzu nan tsanar da kaimin bb har ta kai haka? To wlhy babu inda zanje, dan inada haƙƙi a kanka ai, duk ma abinda zakayi sai kaitayi, amma ka sani niba ƴar iska bace, amma wlhy da tuni naje na nema wani namijin a waj.......”
      Mari ya kai mata tai saurin kaucewa, cikin daka tsawa yace, “Tashi ki fita a ɗakinan kafin na raba kanki da wuyanki wawuya kawai!!”. Saurin sauka tay a gadon, dan yanda ya harzuƙo ɗinan zai iya maketa, batasan ma bashi da wannan ƙarfinba a yanzu, dan ta sakashi a kwale-kwale. Da ƙyar Jawaad ya iya sakkowa a gadon saboda tashin hankalin da Shahudah ta sakashi, duk ƙoƙarin kame kansa da dauriyar da yakeyi yau ta kwanto masa liƙi, ya murzama ƙofar key ya dawo saman gadon jiki babu ƙwari. Gaba ɗaya kansa ya toshe, yama gaza yin tunani akan Shahudah.
       Duk yanda Jawaad yaso yayi barci a wannan daren ya kasa, gashi maganin da yake sha ya barsa a office saboda ya ƙare ya sayosu jiya, sai kuma ya manta bai ɗakkoba, ya watsama jikinsa ruwan sanyi yafi sau shidda kafin asuba, sosai mararsa ke masa masifar ciwo, ko sallar asuba bai fitaba a ɗaki yayi, sai bayan ya idarne barci ɓarawo ya sacesa, shima a matuƙar wahale yayisa.

         Shahudah kuwa da kuka rurus tabar sashen zuwa sashen mama Atika, a falo ta zube tacigaba da kukanta har barci ɓarawo ya saceta.

_______________________________

                       Yau ma har muka fito Office banga kowa a cikin ƴan gidanba, cikin nishaɗi muke ƴar firarmu da Yah Qaseem har muka iso, saida na rakashi har office da tarkacensa sannan na fito nima zuwa namu.
       Ummie bata isoba, hakan yasa na zauna bayan mun gaisa da waɗanda na tarar, ƴan abubuwan da baza'a rasaba na shiga yi, gefe ɗaya kuma ina amsa hirarsu Dawood sama-sama akan aiki, a hankali mukaita ƙaruwa har kowa ya gama isowa, Ummie ta zauna saman tebirina tana faɗin, “Bily gulma da ɗumi-ɗuminta fa”.
         Kallonta nai ina faɗin, “Ƴar sa ido mikika samo mana?”. Ƙaramar dariya tayi da sauke murya ƙasa tace, “Ankawo kuɗin Nazifa”. “Dan ALLAH da gaske?” nai maganar cikin waro ido waje bakina washe da fara'a. Ummie tace, “Wlhy da gaske nake, kema tace ta kiraki bai shigaba, amma ta tura miki saƙo ai”. Wayata na ɗauka ina faɗin, “Kashewa nai da zan kwanta, tunda na tashi kuma ban buɗe data ba, oh ni su Nazifa an mana wayo, da Al-mustaphan dai?”. “Shi kuwa” cewar Ummie tana dariya.
       Fita mukai zuwa can baya nai

kiran Nazifa a waya, bugu biyu ta ɗauka tana faɗin, “Inba gulmaba Bily miye na kirana da farar safiyarnan?”. Dariya mukai ni da Ummie, nace, “Ai gara dai muci gulmar da ɗuminta basai ta huceba, yarinyarnan da gaske dai kin dage aure kikeso?”. “Ban isa bane?” Nazifa ta faɗa tana dariya. “Kin isa kuwa tsaf” Ummie ta bata amsa. Haka muka cigaba da hira cikin so da ƙaunar juna har bamusan lokaci yaja ba.
           Daƙyar muka iya katse hirar muka koma office gudun kar'a nememu.

JAWAAD

     Kamar da wasa ƙaramar magana ta zama babba, dan kuwa dai daga kwanciyar da Jawaad yay bayan sallar asuba sai zazzaɓi mai azabar zafi ya rufesa, duk yanda yaso ƙoƙarin tashi yay shirin office lamarin ya gagara. Wani wahalallen barcin nema ya sake awan gaba dashi bayan ya koma saman gado yaja bargo.

       Gimba yay shiri da wuri kamar yanda yasan suna sammakon fita, sai dai yafi tsayuwar awa guda wajensu baba maigadi babu alamar boss ɗin nashi, dama kuma bai gansa a massallaci ba yau da asuba. Bai dai tambayi kowaba ya cigaba da jira har zuwa ƙarfe tara, zuwa lokacin dai kam abin ya fara bashi mamaki, abinda zai riƙe boss har ƙarfe tara bai fita office ba to lallai dole ya saka kokwanto a zuciyar duk wanda yake tare da shi, wayarsa yay kira har sau uku ba'a amsaba, ya sake daurewa dai ya zauna awa ɗaya ta kuma shuɗewa goma tayi. Yanzu kam tilas ya miƙe ya nufi sashen, yay knocking har kusan sau goma baiji motsin kowaba, hakan yasashi murɗa ƙofar, cikin sa'a kuwa ta buɗe, sai dai koda ya shiga babu kowa a falon, babuma alamar wani ya fito cikinsa. Nan kawai yake da hurumin shiga dan haka bai ƙara gaba ba ya juya ya fita. Yabar wayarsa a mota har baisan su Oga Aliyu nata kiransaba suma jin Boss baizo office ba, sun kuma kira wayoyinsa duka babu wacce ya ɗaga, shine suke kiran Gimban suji ko wani waje sukaje? Amma shima kuma bai amsa musu ba.
           Misalin sha ɗaya da wasu mintuna sai ga Nabeelah da Ummansu sunzo gidan domin sake yima mama Zainab gaisuwa, dan rabonsu da gidan tun ranar rasuwar. Bayan sun shiga sashen mama zainab sun fito sai suka shiga wajen mama Badiyya don su gaisheta da jiki, basu jimaba suka fito zuwa sashen mama Atika, ananne suka iske Shahudah babu lafiya, tana kwance cikin doguwar kujera lulluɓe da bargo, sun mata addu'ar samun lafiya suka miƙe zasu tafi amma sai mama Atika ta tsaidasu da zancen auren Jawaad, murmushi Ummah tayi kawai, tabama mama Atika haƙuri akan zasu masa magana, baki kawai mama Atika ta taɓe, su Umma kuma suka fito abinsu Nabeelah nata ƙunƙuni akan ansama yayansu ido. Basuyi zaton samun Jawaad a gidaba, dan haka sukai yunƙurin barin gidan, Gimba daketa dakon jiran fitowarsu yay azamar isowa garesu yana gaida Umma, da mamaki ta amsa masa, “A'a gimba baku fita office bane ko dawowa kayi kai?”.
       “Wlhy mama bamu fitaba, har yanzu boss bai fitoba, bansan ko lafiya ba? Nai knocking na kirashi amma duk babu wani amsa”.
     Shiru Ummah tayi na wasu sakanni, sai kuma ta fasa shiga motar ta nufi sashen Jay, Nabeelah ma data tuƙosu harta shiga mota ta kunna ta kashe ta fito tabi bayan Ummah.

________________________________

             kasancewar  juma'a ce yau ɗin bayan an sakko salla mun fito zamu fita neman abinci saboda yunwar da nakeji mukaci karo da Oga Jabeer zai shiga mota, har mun gaishesa munwuce sai kuma yay kirana. Dawowa nai ina amsa masa da girmamawa, yace, “Shigo mota ki rakani wani waje”.
     Duk da banso ba sai ban masa musuba na shiga Ummie kuma ta wuce tana min dariyar mugunta............✍

“Saura muji wani yace Hudah🙄 ehe😏.

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.

Bilyn Abdull 📚:
Page 11
Chapter 24 · 0% Book details