Sashe 21
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Assalamu alaikum.
Inason naɗanyi bayani da nake fatan a fahimceni, akan maganar aikinsu Jawaad, inason mai karatu ya fahimci wani abu anan, aikin da muka dangantasu dashi bawai yana nufin ainahin abinda ya shafi ma'aikatan zahirin bane, bamusan komai da ya shafesu ba, tayaya zamuce komai nasu sai ya shigo labarinmu, domin ba'akan hakan muke rubutu ba, da yawanmu ma idan za'a tambayemu bazamuce munsan waɗanan ma'aikatanba kai tsaye, domin su aikinsu bawai a bayyane yakeba kamar ƴan-sanda da dai sauransu da suke cikinmu ba, aikine na wanda kai kanka idan ba wani daliliba bazaka taɓa ka gansu suna yawo gama gari ba ko wani aikinsu a bayyane, so na danganta waɗanan jaruman littafine da hakan saboda mutunci da himma da ƙwazo na irin jami'anmu da mu kanmu bamu saniba, matasanmu kuma su zama masu himma dason bama ƙasarsu gudunmawa da zuciya ɗaya a kowace ƙasa suke ba lallai sai tamu ba, tom inaso ku kalli wannan kawai a matsayin labari bawai lallai abinda yake a zahiri ba, ko yake lallai mu bibiya, matsayinsu, misukeyi? Mizasuyi? Duk iyakarsa labari irin na marubuci {ƙirƙira}, bani da hurumin shiga abinda bani da lasisi a kai, domin bamma sani ba, waɗanan jami'an littafine bawai na zahiri dake aiki a ƙasarmu ba, idan kun kula sam babu wani sunan gari dake nunama a ina suke, ko a wane waje suke, musa a ranmu kawai ƙirƙirarren labari muke karantawa, ilimantarwa, nishaɗi, da faɗakarwa, ba akan kowaba, domin ba'akan kowan mukeyi ba, duk abinda zamu iya ganin yaci karo da waccan rayuwar ta zahiri to kawai fiƙira ce irin ta marubuci bawai dan inada ilimin sani ba ko bibiya balle bincika, ina fatan duk wanda ke bibiyar wannan littafi a ko'ina yake zai kasance maiyin ƙyaƙyƙyawan fahimta akan inda muka dosa, sannan abinda kake ganin na karkace ko shiga hurumin da banawaba ina fatan zakuyi gaggawar dawo dani hanya, ALLAH yasa mu dace, ALLAH kuma ya ƙarama dukkan jami'an tsaronmu lafiya da ƙwazo da nagarta a duk duniyar da suke.🙏🏻
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK TWO
Page 9
............A matsayinka na ubanwa?” cewar Qaseem a fusace.
Cike da rainin wayo Jay yace, “Lokacine zai nuna maka”.
Jabeer da ya shigo office ɗin kusan mintuna biyar da suka shuɗe, amma jaraba ta hanasu ganinsa yay gyaran murya.
Duk kallon ƙofar mukai, Cikin nuna alamun tamkar baima fahimci mike faruwa a office ɗinba ya kalleni tare da miƙamin kwalin dake a hannunsa, “Momcyn mu kikai wannan Office ɗin MM; daga nan ki wuce ƙasa naga ana nemanki”.
Kaina na ɗaga da sauri, na amsa kwalin na fice ina mai godema ALLAH da zuwan oga Jabeer da yay belina hannun waɗanan zakunan.
Babu wanda yay magana tsakanin Jawaad da Qaseem ɗin har Bilkisu ta fita, Jabeer ya maida kallonsa kansu yana ɗan murmushi, “Haba basawanmu, ya zaku saka yarinya tsakkiya kuna yaƙi? Ai saiku rikitata, miye nata a ciki tunda batasan miye tsakaninku ba?, yakamata kumata adalci, aiki take kamar yanda kuke aiki, ku sakata abinda zaku sakata matsayinku na waɗanda suke sama da ita, amma bawai ku sakata tsakkiya akan abinda ke zukatanku ba”.
Juyowa Jay yayi, kamar zaiyi magana sai kuma ya girgiza kansa kawai ya juya yana mai ɗaura hannunsa a kafaɗar Qaseem ɗin yaɗan bubbuga kaɗan ya koma mazauninsa. Binsa da kallo Qaseem yay cike da takaici da baƙin ciki, a ransa yana rayama kansa inhar Jawaad yay gigin cigaba da kutse a al'amuran Bilkisu wlhy wannan karon sai ya karta masa rashin mutuncin da bazai taɓa mantawa da shiba har ƙarshen numfashinsa, yaja tsaki tare da harar Jabeer ya fice daga office ɗin..
Jabeer dake binsa da kallo ya girgiza kai kawai sannan ya juyo ga Jawaad da ya cigaba da harkar gabansa, ƙarasawa yay ya zauna yana ɗora wayarsa a tebirin Jay ɗin, “Boss dan ALLAH son yarinyarnan kakeyi ne?”.
A bazata maganar ta zoma Jawaad, dan haka babu shiri ya ɗago idanunsa da sukai sirkin jaa da ƙara girma ya watsama Jabeer ɗin wata uwar harara, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ƙasa.
Jabeer ya haɗiye dariyarsa yana gyara zamansa, “ALLAH ba wasa nakeba Jay, kuma idan hakan ta kasance wlhy zanyi murna, dan nutsuwar yarinyar na burgeni, g......”
“Motsoww! Jabeer banason shirme, wace irin banzar maganace wannan, Please banaso karka sake”.
Hannu Jabeer ya haɗe waje guda alamar ban haƙuri, Jawaad ya kuma hararsa ya ɗauke kai. Shidai Jabeer yay murmushi kawai, cikin son kauda zancen yace, “Yanzu nakeji su Sir Ahmad sun sake shiga meeting akan batunnan”.
Jawaad da kansa ke durƙushe yana aiki yace, “Basai suyi tayiba tunda basu da tunanin kansu sai abinda aka ɗorasu a kai”. Jabeer yace, “Wlhy Jay ni mamaki suke bani ma, saboda ALLAH maimakon subama yarinya ƙwarin gwiwa akan abinda ta fara sai kawai su ɓige da tsugunne-tsugune, kai yanzu mi kake tunani akan batun?”.
Kallonsa Jay yayi fuska a taɓe, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ga abinda yakeyi, “Tunanin mizanyi akan wannan shirmen Jabeer, iyakaci suce zasu dakatar da ita na wani lokaci ta huta, ko su canja mata wajen aiki ai dai ko? Tunda basu isa suce ta ajiye aikiba akan hakan”.
“To ai babu wanda ya kamata kabari ya kasance a ciki” cewar Jabeer yana kafe Jay da idanu.
Shiru Jawaad yay bai tankaba, tsahon mintuna biyu harma Jabeer ya fidda rai da samun amsa sai yaji yace, “Akanmi zan hana ni kuwa? A matsayina kuma nawa? Dukansu ogannina ne, suna sama dani nesa ba kusa ba, to mizan iya musu kona hanasu?”.
“Jay! Saboda ina ƙwaɗayin yarinyar ta shigo tawagarmu”.
“Humm” Jawaad ya faɗa a taƙaice.
Jabeer da ya fahimci amsar kenan sai ya cigaba da faɗin, “Ba ƙaramar nasara bace hakan a garemu Jay, dan inaji a raina zata ƙara kawomana nasarori, amma kadaiyi tunani akan hakan”.
Ƙin cewa komai Jawaad yayi, hakan yasa Jabeer sakin zancen shima ya ɗakko masa na aikin da suka fara yau kawai, ananne Jay ɗin kuma ya bashi dukkan attention ɗinsa suka shiga tattaunawa.
★★★★★★★
lna fitowa daga office ɗin MM naci karo da Ummie, bansan miyasa na tsinci kaina da gyara yanayinaba na sakar mata murmushi, hararata tayi ita kuwa tana fusgar hannuna mukai gaba. Masallaci muka nufa dan lokacin sallar zuhur yayi.
Bayan mun idar da sallane mun fito Ummie ke tambayata akan ina naje? Mi kuma ya sami kana?. Ban wani ja zancenba na bata labarin abinda zan iya, sai dai ban bata labarin miya faru tsakanina da yah Qaseem ba da kuma ceton da boss yay min a hannunsa yanzun.
Sosai naga mamaki a wajen Ummie tattare da labarin nawa, harna kasa haƙuri nai mata tambaya, tai ƴar dariya kawai da cewar, “Abunne da mamaki ALLAH, wannan mutum mai fuska kamar hadarin tsakkiyar damina ɗin?”.
“Ba abin mamaki bane Ummie, ni kawai na danganta lamarin da abinda ya farune ranar, ganina yake kamar wata jarumar gaske, baisan lamarin duk buge bane kawai” sosai Ummie ta kwashe da dariya cike da shaƙiyanci, nakai mata duka ta kauce tana cigaba da dariyarta, sai da tai mai isarta sannan ta dawo tana bani haƙuri muka shirya, daga haka muka cigaba da tsokanar junanmu da aikin dake gabanmu kuma.
Har lokacin tashi yayi ban sake saka boss da yah Qaseem a idanunaba, dama bai zama lallai na gansunba kasancewar bani da hurumin hakan sai idan sune sukaso, haɗuwarmu a inuwa ɗaya dama sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Haka kawai na tsinci kaina da tsoron bin yah Qaseem, sai kawai nabi Ummie ta saukeni a gida
Inason naɗanyi bayani da nake fatan a fahimceni, akan maganar aikinsu Jawaad, inason mai karatu ya fahimci wani abu anan, aikin da muka dangantasu dashi bawai yana nufin ainahin abinda ya shafi ma'aikatan zahirin bane, bamusan komai da ya shafesu ba, tayaya zamuce komai nasu sai ya shigo labarinmu, domin ba'akan hakan muke rubutu ba, da yawanmu ma idan za'a tambayemu bazamuce munsan waɗanan ma'aikatanba kai tsaye, domin su aikinsu bawai a bayyane yakeba kamar ƴan-sanda da dai sauransu da suke cikinmu ba, aikine na wanda kai kanka idan ba wani daliliba bazaka taɓa ka gansu suna yawo gama gari ba ko wani aikinsu a bayyane, so na danganta waɗanan jaruman littafine da hakan saboda mutunci da himma da ƙwazo na irin jami'anmu da mu kanmu bamu saniba, matasanmu kuma su zama masu himma dason bama ƙasarsu gudunmawa da zuciya ɗaya a kowace ƙasa suke ba lallai sai tamu ba, tom inaso ku kalli wannan kawai a matsayin labari bawai lallai abinda yake a zahiri ba, ko yake lallai mu bibiya, matsayinsu, misukeyi? Mizasuyi? Duk iyakarsa labari irin na marubuci {ƙirƙira}, bani da hurumin shiga abinda bani da lasisi a kai, domin bamma sani ba, waɗanan jami'an littafine bawai na zahiri dake aiki a ƙasarmu ba, idan kun kula sam babu wani sunan gari dake nunama a ina suke, ko a wane waje suke, musa a ranmu kawai ƙirƙirarren labari muke karantawa, ilimantarwa, nishaɗi, da faɗakarwa, ba akan kowaba, domin ba'akan kowan mukeyi ba, duk abinda zamu iya ganin yaci karo da waccan rayuwar ta zahiri to kawai fiƙira ce irin ta marubuci bawai dan inada ilimin sani ba ko bibiya balle bincika, ina fatan duk wanda ke bibiyar wannan littafi a ko'ina yake zai kasance maiyin ƙyaƙyƙyawan fahimta akan inda muka dosa, sannan abinda kake ganin na karkace ko shiga hurumin da banawaba ina fatan zakuyi gaggawar dawo dani hanya, ALLAH yasa mu dace, ALLAH kuma ya ƙarama dukkan jami'an tsaronmu lafiya da ƙwazo da nagarta a duk duniyar da suke.🙏🏻
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK TWO
Page 9
............A matsayinka na ubanwa?” cewar Qaseem a fusace.
Cike da rainin wayo Jay yace, “Lokacine zai nuna maka”.
Jabeer da ya shigo office ɗin kusan mintuna biyar da suka shuɗe, amma jaraba ta hanasu ganinsa yay gyaran murya.
Duk kallon ƙofar mukai, Cikin nuna alamun tamkar baima fahimci mike faruwa a office ɗinba ya kalleni tare da miƙamin kwalin dake a hannunsa, “Momcyn mu kikai wannan Office ɗin MM; daga nan ki wuce ƙasa naga ana nemanki”.
Kaina na ɗaga da sauri, na amsa kwalin na fice ina mai godema ALLAH da zuwan oga Jabeer da yay belina hannun waɗanan zakunan.
Babu wanda yay magana tsakanin Jawaad da Qaseem ɗin har Bilkisu ta fita, Jabeer ya maida kallonsa kansu yana ɗan murmushi, “Haba basawanmu, ya zaku saka yarinya tsakkiya kuna yaƙi? Ai saiku rikitata, miye nata a ciki tunda batasan miye tsakaninku ba?, yakamata kumata adalci, aiki take kamar yanda kuke aiki, ku sakata abinda zaku sakata matsayinku na waɗanda suke sama da ita, amma bawai ku sakata tsakkiya akan abinda ke zukatanku ba”.
Juyowa Jay yayi, kamar zaiyi magana sai kuma ya girgiza kansa kawai ya juya yana mai ɗaura hannunsa a kafaɗar Qaseem ɗin yaɗan bubbuga kaɗan ya koma mazauninsa. Binsa da kallo Qaseem yay cike da takaici da baƙin ciki, a ransa yana rayama kansa inhar Jawaad yay gigin cigaba da kutse a al'amuran Bilkisu wlhy wannan karon sai ya karta masa rashin mutuncin da bazai taɓa mantawa da shiba har ƙarshen numfashinsa, yaja tsaki tare da harar Jabeer ya fice daga office ɗin..
Jabeer dake binsa da kallo ya girgiza kai kawai sannan ya juyo ga Jawaad da ya cigaba da harkar gabansa, ƙarasawa yay ya zauna yana ɗora wayarsa a tebirin Jay ɗin, “Boss dan ALLAH son yarinyarnan kakeyi ne?”.
A bazata maganar ta zoma Jawaad, dan haka babu shiri ya ɗago idanunsa da sukai sirkin jaa da ƙara girma ya watsama Jabeer ɗin wata uwar harara, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ƙasa.
Jabeer ya haɗiye dariyarsa yana gyara zamansa, “ALLAH ba wasa nakeba Jay, kuma idan hakan ta kasance wlhy zanyi murna, dan nutsuwar yarinyar na burgeni, g......”
“Motsoww! Jabeer banason shirme, wace irin banzar maganace wannan, Please banaso karka sake”.
Hannu Jabeer ya haɗe waje guda alamar ban haƙuri, Jawaad ya kuma hararsa ya ɗauke kai. Shidai Jabeer yay murmushi kawai, cikin son kauda zancen yace, “Yanzu nakeji su Sir Ahmad sun sake shiga meeting akan batunnan”.
Jawaad da kansa ke durƙushe yana aiki yace, “Basai suyi tayiba tunda basu da tunanin kansu sai abinda aka ɗorasu a kai”. Jabeer yace, “Wlhy Jay ni mamaki suke bani ma, saboda ALLAH maimakon subama yarinya ƙwarin gwiwa akan abinda ta fara sai kawai su ɓige da tsugunne-tsugune, kai yanzu mi kake tunani akan batun?”.
Kallonsa Jay yayi fuska a taɓe, sai kuma yaja tsaki ya maida kansa ga abinda yakeyi, “Tunanin mizanyi akan wannan shirmen Jabeer, iyakaci suce zasu dakatar da ita na wani lokaci ta huta, ko su canja mata wajen aiki ai dai ko? Tunda basu isa suce ta ajiye aikiba akan hakan”.
“To ai babu wanda ya kamata kabari ya kasance a ciki” cewar Jabeer yana kafe Jay da idanu.
Shiru Jawaad yay bai tankaba, tsahon mintuna biyu harma Jabeer ya fidda rai da samun amsa sai yaji yace, “Akanmi zan hana ni kuwa? A matsayina kuma nawa? Dukansu ogannina ne, suna sama dani nesa ba kusa ba, to mizan iya musu kona hanasu?”.
“Jay! Saboda ina ƙwaɗayin yarinyar ta shigo tawagarmu”.
“Humm” Jawaad ya faɗa a taƙaice.
Jabeer da ya fahimci amsar kenan sai ya cigaba da faɗin, “Ba ƙaramar nasara bace hakan a garemu Jay, dan inaji a raina zata ƙara kawomana nasarori, amma kadaiyi tunani akan hakan”.
Ƙin cewa komai Jawaad yayi, hakan yasa Jabeer sakin zancen shima ya ɗakko masa na aikin da suka fara yau kawai, ananne Jay ɗin kuma ya bashi dukkan attention ɗinsa suka shiga tattaunawa.
★★★★★★★
lna fitowa daga office ɗin MM naci karo da Ummie, bansan miyasa na tsinci kaina da gyara yanayinaba na sakar mata murmushi, hararata tayi ita kuwa tana fusgar hannuna mukai gaba. Masallaci muka nufa dan lokacin sallar zuhur yayi.
Bayan mun idar da sallane mun fito Ummie ke tambayata akan ina naje? Mi kuma ya sami kana?. Ban wani ja zancenba na bata labarin abinda zan iya, sai dai ban bata labarin miya faru tsakanina da yah Qaseem ba da kuma ceton da boss yay min a hannunsa yanzun.
Sosai naga mamaki a wajen Ummie tattare da labarin nawa, harna kasa haƙuri nai mata tambaya, tai ƴar dariya kawai da cewar, “Abunne da mamaki ALLAH, wannan mutum mai fuska kamar hadarin tsakkiyar damina ɗin?”.
“Ba abin mamaki bane Ummie, ni kawai na danganta lamarin da abinda ya farune ranar, ganina yake kamar wata jarumar gaske, baisan lamarin duk buge bane kawai” sosai Ummie ta kwashe da dariya cike da shaƙiyanci, nakai mata duka ta kauce tana cigaba da dariyarta, sai da tai mai isarta sannan ta dawo tana bani haƙuri muka shirya, daga haka muka cigaba da tsokanar junanmu da aikin dake gabanmu kuma.
Har lokacin tashi yayi ban sake saka boss da yah Qaseem a idanunaba, dama bai zama lallai na gansunba kasancewar bani da hurumin hakan sai idan sune sukaso, haɗuwarmu a inuwa ɗaya dama sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Haka kawai na tsinci kaina da tsoron bin yah Qaseem, sai kawai nabi Ummie ta saukeni a gida