Sashe 165
Kwai Cikin Kaya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayyana muku tashin hankalin da waɗanan mutane ke a ciki a wannan lokaci zaici tsahon lokaci bamu gamaba, komai ya sake hargitsewa da ruɗewa, dole ƴan-sandan dake a waje suka shigo cikin gidan tare da dogarawan sarki wanda shi yama rasa abin faɗa tsabar mamaki, a da gani yake babu wata ruɗaɗɗiyar rayuwa irin tasa, sai a yau yaga wadda tafi tasa muni da tashin hankali.
Da ƙyar aka iya fita dasu Dad daga gidan, suna kuka da roƙon a yafe musu amma babu wanda ya sauraresu, sai ma tsinuwa da sukesha daga bakin kowa harda ƴaƴansu kansu da matansu. An shiga ƙoƙarin yayyafama waɗanda suka suma ruwa harda Shahudah da Bilkisu, da Mama Atika. Wadda itakam da alama ma dai faɗuwar da tayi tazo da sakamakon paralysis, dan ta gaza motsa komai nata sai ido takebin mutane da shi kawai tana kuka.
______________
Komai fa ya sake rikicewa, gari ya ɗauki magana da ba'asan tayaya ta fita daga gidan Alhaji babba ba, sai daga baya aka fahimci camera aka saka jikin su Dad da ba'asan wanene ya sakaba, ta naɗe komai daya faru a gidan Alhaji babba, lokacin da aka maidasu office kuma a take aka fidda komai ta kafafen yaɗa labarai.
Lokacin da takawa ya baro gidan Alhaji babba zuwa inda ake jiransa zasuyi meeting da ƙyar suka kai saboda hargitsewar da garin yayi, matasa ta ko'ina sun fara fitowa zanga-zanga da makamai akan sufa sai an basu su Dad sun kashe. Kamar wasafa saiga zanga-zanga ta fara faɗaɗa, dan harda ƴammata da zawarawa a cewarsu suma sunabin kadin haƙƙin ƴan uwansu dasu Dad suka lalatama rayuwa ta hanyar fyaɗe. Idan ba'a basu su Uncle Nasir ba zasu bankama station ɗin da aka ajiyesu wuta.
Sai kuma rukunin magidanta da tasu zanga-zangar ta ɗauki manufa akan kisan tsohon shugabanƙasa Abdul-aziz Yousif Tafida, a cewarsu sumafa sai sunbi kadin jinin adalin shugabansu. Tofa jama'a sun fusata ainun, kowane titi ka zagaya mutane ke tittiɗowa zuwa station ɗinsu Jawaad da aka ajiye su Alhaji Kokino, tun jami'an tsaro na ƙoƙarin kwantar da tarzomar dake nemans harfa al'amarin ya nema gagararsu sai da aka kawo wasu jami'an tsaron kala-kala. Amma duk da haka al'amarin ya gagara. daga ƙarshema sai suka zagaye hall ɗin dasu Takawa sukai zaman meeting, acewarsu su fito su bada damar a fiddo musu dasu Kokino kokuma su haɗa dasu. Dan bazasu taɓa yarda sai ankai su Dad Kotu ba, su duk duniya basuga alƙalin da zai iya yima su Dad shari'a ba sam. Gara kawai su kashesu a haɗu a kotun UBANGIJI kawai.
★★★★★★★
Har dare gari yaƙi lafiya, tamkarma ƙara ƴan zanga-zangar akeyi. Jawaad na gida tare da ƴan uwansa dake cike da ruɗani da tashin hankali wannan al'amari har yanzu kira ya samesa daga office. Duk yanda yaso ƙin fitar Alhaji babba sai da ya takurashi, acewarsa babufa yanda zasuyi, wannan al'amarin su barma ALLAH kawai shine zaiyi maganin waɗannan mutanen bawai ƙarfinsuba ko dabararsu. Haka ya fita jikinsa duk babu wani daɗi, ya sumbaci goshin bilkisu daketa barci yana haɗiye hawayen da suka cika masa ido, tausayin kansu yakeji daga shi har ita, musamman ma ita da nata al'amarin yazo a yanda basuyi zato ko tsammaniba, kenan Shahudah da Bilkisu ubansu ɗaya fa kenan? Bilkisu jininsa ce, jini mafi kusanci da muhimmanci a garesu, jinin wadda take da daraja a garesa, wadda ta yarda ta rasa ranta da farin cikinta a dalilin salwantar da mahaifinsa.
Bai iya jan motarba sai Hafiz ne yazo har gida ya ɗaukesa, shi kansa halin da yaga garin yake ciki ba ƙaramin sake tada masa da hankali al'amarin yayiba, dare harya rufa amma mutane basu da niyya komawa gidajensu. Da ƙyar motarsu ta samu hanyar shiga station ɗinsu.
Sun sami su Sir Ahmad cikin tsananin tashin hankali da damuwa, sune sukaimasa bayanin yanda akai komai ya fita har jama'a sukayo wannan gangamin na farautar rayukan su Dad. Ajiyar zuciya kawai Jawaad keta saukewa, tausayin su Qaseem da sauran iyalan waɗanan mutane kawai yakeji, dan haka ya bada shawarar a fita dasu Dad ta ɓarauniyar hanya abar station ɗin dasu zuwa cikin prison dasu ko hakan zaisa a samu sassaucin da hankulan mutane.
Da wannan shawara ta Jawaad akai amfani, sannan D.G da kansa ya fita yayma jama'a bayani daban haƙuri akan su bari suga idan ba'a yankema su Dad hukuncin daya daceba sai su ɗauki matakin da duk sukai niyya, amma dan ALLAH yanzu su kwantar da hankulansu kodan dare.
Da ƙyar suka amince akan safiyar gobe su farka da batun shigar su Kokino kotu, kokuma su su ɗauki doka a hannunsu game dasu. Garin baiyi lafiyaba sai da aka sake baza jami'an tsaro, duk yanda su Jay sukaso kwana a gidajensu yau kam ta gagaresu, sunata kai kawo akan mutane har garin ALLAH ya waye.
_________________
Tunda na farka kallon kowa kawai nake, jinake tamkar an kwashemin ƙwaƙwalwa da zuciya an jefar gefe, kukan zuci zanyi kona zahiri? Wane kalar tunani zanyi akan wannan juyayyen al'amari ruɗaɗɗe? Iyayen dana tashi na gani ƙaddara ta juyasu sun zama ba nawa ba, waɗanda ban taɓa kawowa a tunanin hankali da ƙwaƙwalwa ba sune suka zama iyaye na gaskiya. Dad fa? Jama'a kuji wani batu tamkar a tatsuniyiyi da hikayoyin marubuta. Ashe shiyyasa nakejinsa a raina tun lokacin dana fara tozali dashi matsayin yayan innata? Shin murna ya kamata nayi shin kokuwa kuka? Baƙinciki kokuwa takaicin kasancewarsa Ubana ni jininsa? Wane hukunci ya dace dashi game da mahaifiyata da sauran al'ummar da suka cutar suka zalinta saboda son zuciya da ƙwaɗayi da burin duniya da kayan cikinta? Anya badan kalmomin bakina sunyi nauyin da zasu iya zama tuntuɓen harshe wajen aikata zunubiba da ban zazzagesu ga azzalumin uba irin nawaba kodan duniya taji tasan na tsanesa. Inama gaskiya bata fitaba na ciga da kallonsa matsayin yayan inna ba Mahaifina ba, inama ace banga wannan ranarba Mamana ta bari yayi tsafin dani nima. Inama.... Inama..... Inama.....?
Bilkisu ta faɗa a fili tana rushewa da matsanancin kuka mai cin zuciya. Rungumeta Umm-Anum tayi suka cigaba da rerawa a tare. Kowa ka gani a gidan idanunsa a kumbure babu ko ƙyan gani, su Uncle Sulaiman tun a daren jiya duk sun koma gidansu, anan su kaɗaine zuri'ar Alhaji babba sai su firdausi kuma da Maman Yara da tun jiya tana nan, ganinta ba ƙaramin daɗi yayma Umm-Anum ba, inda itama a wajen maida yanda akayi ta sake buɗe komai dangane da abinda ta sani game dasu Dad ɗin da zamanta gidan Alhaji Kokino na tsahon shekaru dan kawai ta samu damar ɗaukar tukunyar tsafin da akaima Umm-Anum. Ganota da Alhaji Kokino yayi gameda taimakon da suke bama Jawaad ita da ɗan ƴar uwarta Gimba, kashesa da sukayi da kamatan da sukayi sukaita azabartarwa, harma da wasu manya-manyan sirrikansu da taji.
Nanma dai ansha kuka mai ban tausayi, tare da jera ɗunbin godiya a gareta da addu'oin fatan alkairi. Duk yanda sukaso ganin kwanciyar hankalin bilkisu hakan ya gagara, daga ƙarshema saita fara bleeding, a matuƙar tashin hankali aka kwasheta zuwa asibiti, inda ta samu taimakon gaggawa a wajen Dr Bello. Jawaad baisan mike faruwa ba saida Nabeelah ta kirasa ta sanar masa, hankali tashe kuwa ya iso asibitin.
To cikin dai ikon ALLAH an samu damar tsaida jinin, inda Doctor yay musu albishir da cewar cikinta na nan bai zubeba, sai dai tana buƙatar samun hutu dan gaskiya ƙwaƙwalwarta da zuciyarta suna cikin tsagwaron ruɗani, har jininta yama hau, idan da bama suyi gaggawar kawota asibiti ba da ba cikin kawai za'a rasaba ita kanta zasu iyama rasatan. To amma Alhmdllh yanzu kam komai ya dai-daita, sai kawai a jira farkowarta kuma aga abinda ALLAH zaiyi..................✍
Ku dakaceni da sauran zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu idan na kammala editing😊😍😍😘🚴🏼.
ALLAH ka gafartama iyayenmu
[2/17, 7:31 AM] Suwaiba: Page 63
....................Su Jawaad basu san wainar da ake toyawaba a gari, sai iface-iface suka dingaji da tashin hayaniya, sai kuma hayaƙi daketa turnuƙe sararin samaniya a hankali. Sai sukaga kuma mutane nata fita daga asibitin.
Gaban Jay ya faɗi, ya zaro waya daga aljihu yay kiran Jabeer dan yaji ko lafiya?. “Boss wlhy akwai matsala, an fito da mutanen nan daga prison za'a kaisu kotu jama'ar gari sun tare motar sun banka mata fetur sun saka wuta. Wlhy duk yanda jami'an tsaro sukaso tsaidawa al'amarin ya gagara, harma an raunata mana ɗan sanda guda daketa ƙoƙarin basu kariya da roƙon mutane su kwantar da hankalinsu kotu za'a kaisu, kuma a yau za'a yanke musu hukunci. Amma sam basu sauraresaba, saima suka nema haɗawa dashi shima, dan acewarua shima nasune”. Innalillahi Jawaad keta ambata zufa na keto masa a duka sassan jikinsa. Dole yabar asibitin ya nufi inda al'amarin ke faruwa..
Da ƙyar aka iya fita dasu Dad daga gidan, suna kuka da roƙon a yafe musu amma babu wanda ya sauraresu, sai ma tsinuwa da sukesha daga bakin kowa harda ƴaƴansu kansu da matansu. An shiga ƙoƙarin yayyafama waɗanda suka suma ruwa harda Shahudah da Bilkisu, da Mama Atika. Wadda itakam da alama ma dai faɗuwar da tayi tazo da sakamakon paralysis, dan ta gaza motsa komai nata sai ido takebin mutane da shi kawai tana kuka.
______________
Komai fa ya sake rikicewa, gari ya ɗauki magana da ba'asan tayaya ta fita daga gidan Alhaji babba ba, sai daga baya aka fahimci camera aka saka jikin su Dad da ba'asan wanene ya sakaba, ta naɗe komai daya faru a gidan Alhaji babba, lokacin da aka maidasu office kuma a take aka fidda komai ta kafafen yaɗa labarai.
Lokacin da takawa ya baro gidan Alhaji babba zuwa inda ake jiransa zasuyi meeting da ƙyar suka kai saboda hargitsewar da garin yayi, matasa ta ko'ina sun fara fitowa zanga-zanga da makamai akan sufa sai an basu su Dad sun kashe. Kamar wasafa saiga zanga-zanga ta fara faɗaɗa, dan harda ƴammata da zawarawa a cewarsu suma sunabin kadin haƙƙin ƴan uwansu dasu Dad suka lalatama rayuwa ta hanyar fyaɗe. Idan ba'a basu su Uncle Nasir ba zasu bankama station ɗin da aka ajiyesu wuta.
Sai kuma rukunin magidanta da tasu zanga-zangar ta ɗauki manufa akan kisan tsohon shugabanƙasa Abdul-aziz Yousif Tafida, a cewarsu sumafa sai sunbi kadin jinin adalin shugabansu. Tofa jama'a sun fusata ainun, kowane titi ka zagaya mutane ke tittiɗowa zuwa station ɗinsu Jawaad da aka ajiye su Alhaji Kokino, tun jami'an tsaro na ƙoƙarin kwantar da tarzomar dake nemans harfa al'amarin ya nema gagararsu sai da aka kawo wasu jami'an tsaron kala-kala. Amma duk da haka al'amarin ya gagara. daga ƙarshema sai suka zagaye hall ɗin dasu Takawa sukai zaman meeting, acewarsu su fito su bada damar a fiddo musu dasu Kokino kokuma su haɗa dasu. Dan bazasu taɓa yarda sai ankai su Dad Kotu ba, su duk duniya basuga alƙalin da zai iya yima su Dad shari'a ba sam. Gara kawai su kashesu a haɗu a kotun UBANGIJI kawai.
★★★★★★★
Har dare gari yaƙi lafiya, tamkarma ƙara ƴan zanga-zangar akeyi. Jawaad na gida tare da ƴan uwansa dake cike da ruɗani da tashin hankali wannan al'amari har yanzu kira ya samesa daga office. Duk yanda yaso ƙin fitar Alhaji babba sai da ya takurashi, acewarsa babufa yanda zasuyi, wannan al'amarin su barma ALLAH kawai shine zaiyi maganin waɗannan mutanen bawai ƙarfinsuba ko dabararsu. Haka ya fita jikinsa duk babu wani daɗi, ya sumbaci goshin bilkisu daketa barci yana haɗiye hawayen da suka cika masa ido, tausayin kansu yakeji daga shi har ita, musamman ma ita da nata al'amarin yazo a yanda basuyi zato ko tsammaniba, kenan Shahudah da Bilkisu ubansu ɗaya fa kenan? Bilkisu jininsa ce, jini mafi kusanci da muhimmanci a garesu, jinin wadda take da daraja a garesa, wadda ta yarda ta rasa ranta da farin cikinta a dalilin salwantar da mahaifinsa.
Bai iya jan motarba sai Hafiz ne yazo har gida ya ɗaukesa, shi kansa halin da yaga garin yake ciki ba ƙaramin sake tada masa da hankali al'amarin yayiba, dare harya rufa amma mutane basu da niyya komawa gidajensu. Da ƙyar motarsu ta samu hanyar shiga station ɗinsu.
Sun sami su Sir Ahmad cikin tsananin tashin hankali da damuwa, sune sukaimasa bayanin yanda akai komai ya fita har jama'a sukayo wannan gangamin na farautar rayukan su Dad. Ajiyar zuciya kawai Jawaad keta saukewa, tausayin su Qaseem da sauran iyalan waɗanan mutane kawai yakeji, dan haka ya bada shawarar a fita dasu Dad ta ɓarauniyar hanya abar station ɗin dasu zuwa cikin prison dasu ko hakan zaisa a samu sassaucin da hankulan mutane.
Da wannan shawara ta Jawaad akai amfani, sannan D.G da kansa ya fita yayma jama'a bayani daban haƙuri akan su bari suga idan ba'a yankema su Dad hukuncin daya daceba sai su ɗauki matakin da duk sukai niyya, amma dan ALLAH yanzu su kwantar da hankulansu kodan dare.
Da ƙyar suka amince akan safiyar gobe su farka da batun shigar su Kokino kotu, kokuma su su ɗauki doka a hannunsu game dasu. Garin baiyi lafiyaba sai da aka sake baza jami'an tsaro, duk yanda su Jay sukaso kwana a gidajensu yau kam ta gagaresu, sunata kai kawo akan mutane har garin ALLAH ya waye.
_________________
Tunda na farka kallon kowa kawai nake, jinake tamkar an kwashemin ƙwaƙwalwa da zuciya an jefar gefe, kukan zuci zanyi kona zahiri? Wane kalar tunani zanyi akan wannan juyayyen al'amari ruɗaɗɗe? Iyayen dana tashi na gani ƙaddara ta juyasu sun zama ba nawa ba, waɗanda ban taɓa kawowa a tunanin hankali da ƙwaƙwalwa ba sune suka zama iyaye na gaskiya. Dad fa? Jama'a kuji wani batu tamkar a tatsuniyiyi da hikayoyin marubuta. Ashe shiyyasa nakejinsa a raina tun lokacin dana fara tozali dashi matsayin yayan innata? Shin murna ya kamata nayi shin kokuwa kuka? Baƙinciki kokuwa takaicin kasancewarsa Ubana ni jininsa? Wane hukunci ya dace dashi game da mahaifiyata da sauran al'ummar da suka cutar suka zalinta saboda son zuciya da ƙwaɗayi da burin duniya da kayan cikinta? Anya badan kalmomin bakina sunyi nauyin da zasu iya zama tuntuɓen harshe wajen aikata zunubiba da ban zazzagesu ga azzalumin uba irin nawaba kodan duniya taji tasan na tsanesa. Inama gaskiya bata fitaba na ciga da kallonsa matsayin yayan inna ba Mahaifina ba, inama ace banga wannan ranarba Mamana ta bari yayi tsafin dani nima. Inama.... Inama..... Inama.....?
Bilkisu ta faɗa a fili tana rushewa da matsanancin kuka mai cin zuciya. Rungumeta Umm-Anum tayi suka cigaba da rerawa a tare. Kowa ka gani a gidan idanunsa a kumbure babu ko ƙyan gani, su Uncle Sulaiman tun a daren jiya duk sun koma gidansu, anan su kaɗaine zuri'ar Alhaji babba sai su firdausi kuma da Maman Yara da tun jiya tana nan, ganinta ba ƙaramin daɗi yayma Umm-Anum ba, inda itama a wajen maida yanda akayi ta sake buɗe komai dangane da abinda ta sani game dasu Dad ɗin da zamanta gidan Alhaji Kokino na tsahon shekaru dan kawai ta samu damar ɗaukar tukunyar tsafin da akaima Umm-Anum. Ganota da Alhaji Kokino yayi gameda taimakon da suke bama Jawaad ita da ɗan ƴar uwarta Gimba, kashesa da sukayi da kamatan da sukayi sukaita azabartarwa, harma da wasu manya-manyan sirrikansu da taji.
Nanma dai ansha kuka mai ban tausayi, tare da jera ɗunbin godiya a gareta da addu'oin fatan alkairi. Duk yanda sukaso ganin kwanciyar hankalin bilkisu hakan ya gagara, daga ƙarshema saita fara bleeding, a matuƙar tashin hankali aka kwasheta zuwa asibiti, inda ta samu taimakon gaggawa a wajen Dr Bello. Jawaad baisan mike faruwa ba saida Nabeelah ta kirasa ta sanar masa, hankali tashe kuwa ya iso asibitin.
To cikin dai ikon ALLAH an samu damar tsaida jinin, inda Doctor yay musu albishir da cewar cikinta na nan bai zubeba, sai dai tana buƙatar samun hutu dan gaskiya ƙwaƙwalwarta da zuciyarta suna cikin tsagwaron ruɗani, har jininta yama hau, idan da bama suyi gaggawar kawota asibiti ba da ba cikin kawai za'a rasaba ita kanta zasu iyama rasatan. To amma Alhmdllh yanzu kam komai ya dai-daita, sai kawai a jira farkowarta kuma aga abinda ALLAH zaiyi..................✍
Ku dakaceni da sauran zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu idan na kammala editing😊😍😍😘🚴🏼.
ALLAH ka gafartama iyayenmu
[2/17, 7:31 AM] Suwaiba: Page 63
....................Su Jawaad basu san wainar da ake toyawaba a gari, sai iface-iface suka dingaji da tashin hayaniya, sai kuma hayaƙi daketa turnuƙe sararin samaniya a hankali. Sai sukaga kuma mutane nata fita daga asibitin.
Gaban Jay ya faɗi, ya zaro waya daga aljihu yay kiran Jabeer dan yaji ko lafiya?. “Boss wlhy akwai matsala, an fito da mutanen nan daga prison za'a kaisu kotu jama'ar gari sun tare motar sun banka mata fetur sun saka wuta. Wlhy duk yanda jami'an tsaro sukaso tsaidawa al'amarin ya gagara, harma an raunata mana ɗan sanda guda daketa ƙoƙarin basu kariya da roƙon mutane su kwantar da hankalinsu kotu za'a kaisu, kuma a yau za'a yanke musu hukunci. Amma sam basu sauraresaba, saima suka nema haɗawa dashi shima, dan acewarua shima nasune”. Innalillahi Jawaad keta ambata zufa na keto masa a duka sassan jikinsa. Dole yabar asibitin ya nufi inda al'amarin ke faruwa..