Sashe 9
Sarki Sameer Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ɗagowa tayi ta kalle sa duk son da takewa choculate ɗin sai taji ta fitar mata arai, dan haka sai kawai ta girgiza masa kai alamun bazata shaba, yayi mamakin hakan tunda yaga yanda ta nuna tanason sha amma yanzu kuma tace bazata shaba, ƙara miƙa mata yaƙara yi akaro na biyu,
Sai taji nauyi ta ƙara cemasa a'a sai kawai ta miƙa hannu zata karɓa badan tana soba saidan kawai kar tamayar da hannun kyauta baya, ga mamakin ta sai taga kawai ya janye daga miƙo hannun da tayi sai ya nufi bakin ta dashi, ƙin buɗe bakin tayi sai da taga ya haɗe rai yana wurga mata harara sannan ta buɗe small mouth ɗin shikuma ya saka mata abakin tana shirin gutsirar ƴar kaɗan kawai ya danna mata ita abaki gaba ɗaya,
Waro ido tayi tana ƙoƙarin cire hannun sa ta ciro ta saboda ta cika mata baki bazata taɓa iya taunawa,
Hannu yasa ya rufe mata bakin yanda bazata iya fito da iyaba, da taga dai ba sarki sai Allah haka ta shiga taunawa da ƙyar harda ƙwallar wahala haka Meer yasata ta cinye ta tas sannan ya sakar mata bakin, yana saki kuma yaƙara dauko wata yashiga ɓare ta, ai tana ganin haka tayi saurin miƙewa zata gudu saidai bataje ko ina ba ya cafkota, yana miƙewa tsaye yace "ina zaki ai sai kinyi maganar da ta kawoki kamar kuma yanda kikace mufara shanye choculate ɗin zakiyi maganar to sai ki zauna sai kin shanye su duka sannan kiyi maganar idan kinason fita daga ɗakin nan,
Zaro ido ta shiga yi tana faman rarraba ido tace Allah kuwa na ƙoshi kuma ai mungama magana daman itace ta kawo ni kuma mungama, choculate kuma kasha kayarka na ƙoshi tunfar ko da nace kaban ai rowa kamin dan haka wacce kaban da mugunta ta isheni, daman nace mug...., Da sauri tasa hannu ta toshe bakin ta, bata ƙarasa kalmar mugun ba tunawa da tayi yace kar tasake ce masa mugu,
Wani mugun kallo kawai ya watsa mata sannan ya koma ya zauna yace "dawo ki zauna,
Ganin yayi maganar serious ba wasa, yasa ta dawo da baya ta zauna a inda ta tashi................,
*************************
___________ *SAM*
Tun ranar da yaje gidan da yakai sumy akace masa ta gudu tun loƙacin baiƙara samun nutsuwa, ya dawo gida ya rasa inda zai tsoma ransa, yaji daɗi, ga shettima abokin shawarar sa tunda ya tafi gida shima bai ƙara dawowa masarautar ba, kuma yafiso suyi maganar face to face shiyasa bai kirasa ba....,
Yanzuma yana zaune akan gado ya zabga tagumi yana tunanin samun mafita da ta inda zai fara nemanta gashi kuma ƙarewa ma babu wanda yasan ya ɗauko ta, baisan ta inda zai fara tunkarar wani da maganar ba,
Jiyayi andafasa da sauri ya É—ago yazuba rinannun idanuwansa akan fuskar sa kallo É—aya kuma yayi masa ya janye saboda bayaso ya karanci halin da yake ciki,
Me yake damunka? Hamza ya jefa masa tambayar,
Batare da ya kallesaba yace ba komai kawaidai kainane yake É—anyi min ciwo, kuma nasha magani yanzu zai daina kar kadamu, yana faÉ—ar haka yaÉ—an gyara zaman sa ya kishingiÉ—a, yana dafe kansa,
Gefensa Hamza ya samu ya zauna yana kallon sa cike da nazartar sa, saboda tun loƙacin da abu yafaru sam yajasa ajiki tun bayaso har ya ɗan fara sakin jiki dashi, kuma sam yasa ya tattaro kayan sa yadawo part ɗin sa da zama amma duk da haka Hamza ba kullum yake zama ba a part ɗin kullum yana waje bayan gidan yana zagaye dan yafi son ya ringa keɓewa shikaɗai hakan yafi masa daɗi dan ko abinci ma bai fiya zama ya ciba wani loƙacin ma sai Sam yayi masa dole yake ci,
Cikin sanyin murya Hamza yace "kayi haƙuri zan shiga hurumin da banawa ba na fahimci kana cikin damuwa, bankai matsayin da zan san damuwar kaba, dan haka basai ka gaya min matsalar kaba, shawara zan baka yakamata kasamowa kanka mafita zaman ɗaki ba abun da zai haifar maka sai wani ciwon, kamata yayi kaje kasanar da mahaifiyar ka ko kasamu wanda kafi kusanci dashi kasanar dashi faɗar damuwa koda baza ayi maka maganin taba idan ka fitar da ita zaka ɗan samu sassauci akan yanda kakeji, duk wanda yaganka zai gane kana cikin matsananciyar damuwa, ba iya ciwon kai ke damunka tun ba yauba na lura dakai, dan Allah ka daure ko abokin kane ka sanar dashi matsalar ka kar kabari tayi maka illa a ɗaki, Sosai Hamza yashiga nusar dashi illar riƙe damuwa batare da ka fitar da ita ba hakan na ƙaramin cutar da ɗan adam take ba,
Kalaman sa kam sunyi aiki akan Sam sosai yaji maganar sa, kuma sai yaji ba daɗi da yace yasan baikai matsayin da zai san damuwar sa, hakan ba ƙaramin kashe mishi jiki yayi ba bayaso yaringa tunani wani iri da zai ringa sakashi damuwa shiyasa yake jansa ajiki dan ya manta da duk abun da yafaru, amma furucinsa na yanzu kwata kwata baiyi masa daɗi ba,
Dan haka yayi saurin tashi zaune yana fuskantar Hamza da kyau, yace "ko ɗaya ba abun da kake tunani bane indai har zan iya sanar da mahaifiyata ko abokina ko wanda nake da kusanci dashi to dole kaima kana cikin ɗaya daga cikin su, yanda zan ɗaukesu kaima haka zan ɗauke, Nagode da nuna kulawar ka agare ni tabbas akwai abun da yake damuna amma narasa mafita kuma bana tunanin ko na gayawa wani zai iya samamin ita, tunanin ya tsaya gaba ɗaya narasa yanda zanyi Hamza, yaƙarasa maganar cikin sanyin jiki,
Hamza ma jikin sane yayi sanyi kuma yaji daɗi sosai jin matsayin da yabasa mai girma haka duk da laifin da mahaifiyar sa ta aikata musu amma babu wani wanda yake nuna masa kyara da tsangwama, musamman Sam da yafi kowa jansa ajiki hakan ba ƙaramin daɗi yake masa ba,
A hankali shima yafara magana da cewa "indai har dagaske ne abun da kafaɗa to ina mai roƙonka da kagaya min nikuma in sha Allah zanne ma maka mafita da yardar Allah zan taimaka mana,
Ɗan murmushin yaƙe Sam tare da jinjina kai batare da yace masa komai ba, yakai wajen minti bakwai kafin yaɗanyi gyaran murya sannan ya shiga basa labarin abun da yafara tsakanin sa da sumy ɗin tundaga farkon haɗuwar su har ƙarshe, inda yakaita gidan ƙanwar kakar sa, (Ammah) yace kuma yaje amma ta sanar dashi suma tashi sukayi suka nemeta suka rasa.....,
Hamza najin haka yasaki murmushi mai ƙayatarwa da ya daɗe baiyi irinsa ba, da hakan har saida ya bawa Sam mamaki, danshi tunda suka zauna na bai taɓa ganin murmushin saba,
Batare da ya daina murmushin ba yace "ashe ƙanin nawa soyayya ya faɗa, kace munkusa shan biki, macece daman tasaka gaba haka ka kama damuwa har da su rama, tokwa dole intashi tsaye karka damu zamu nemo maka ita duk inda ta shiga afaɗin duniyar nan, bare ma nasan ba wani nisa tayi, tana kusa,
Tunda yafara magana sam yake kallon sa cike da mamakin kalaman sa shi yana masa maganar serious amma shi yazo yana masa wata irin magana marar ma'ana, haushi yaje yakamasa take ya shiga yi masa wani irin kallo saida yabari yayi shiru sannan yace "kaga nifa ba abun da kake tunani bane kanajin yanda nabaka labarin yanda take rayuwa abun tausayi kuma kana min wata maganar daban inma wasa kake Please mubar wanann maganar banaso inbaza ka taimake ni dan Allah ba to kabarshi yana faɗar haka ya miƙe cike da jin haushin Hamza,
Da sauri Hamza ya miƙe yana ƙumshe dariyar sa da take shirin fitowa, sannan yace "tuba nake kayi haƙuri bazan ƙara ba, yanzudai abar ko wane zance muje neman yanzu nan basai anjima ba, amma zamu fara zuwa gidan kakar taka kuma kar kasanar da ita muje kawai yana faɗar haka ya kamo hannun sa yana ƙara cewa muje,
Sam kamar wani soko haka yake kallon Hamza cikin rashin fahimtar inda zancen sa ya dosa, yana buɗe baki zaiyi magana Hamza yayi saurin da katar dashi yace "karkace komai pls muje kawai, haka kwa Sam yayi shirun ya shiga binsa tunani fal cikin sa shiyasa ma yakasa tantance wane iri zaiyi, bashi da zaɓi da ga wuce ya bisa ɗin,
a haka suka fito daga É—akin har suka wuce falo suka fito part É—in fulani suna fitowa sukaga anfita da gudu daga cikin falon,
Ai Hamza baijira wata wata ba ya kwasa aguje yabi bayan wanda ya fita daga ciki, yana fita ya hango wata mace, ta shiga wani part ɗin, girgiza kai yayi yace "zaki ci ubanki Ubaira, duk ma wanda ya aiko ki zakiyi bayani, yana cikin wanann maganar Sam yaƙaraso gurin yace "wacece wacce ta fito ɗin ka ganta ina tayi,
Ɗan dafa kafaɗar sa yayi ya bubbuga yace "muje kawai komai yana da loƙaci yanzu ba wancen loƙacin bane, zamuyi maganar idan mungama waccen, wata mata ce kuma nasanta naganeta naga kuma inda ta shiga ai anyi mai wuyar, dan haka kar kadamu da wannan kaji da abun da yake gabanka, muje yafaɗa yana yin gaba,
Yaudai Sam ya zama ɗan kallo sai yanda Hamza yayi dashi haka, yabi bayansa har suka ƙarasa inda motar sa yake, driver yazo zai buɗe masa ƙofa Hamza ya dakatar dashi yace "yaje sannan ya buɗewa Sam motar da kansa ya shiga shikuma ya shiga driver seat yashiga tare da tayar da motar yajasu suka fice daga masarautar Sam yana masa kwatance, ahaka har suka ƙarasa unguwar abakin gate ɗin gidan Hamza yayi parking,
Sam ne ya É—ago ya kalle sa ganin yayi parking a waje yace "naga ka tsaya anan mushiga mana,
Batare da Hamza ga kallesa ba ya girgiza masa kai, sannan ya buɗe motar ya fita ya zagayo ya buɗewa Sam, shima Sam bai ƙara magana ba, ya fito kawai atare suka nufi gate ɗin gidan, suna zuwa bakin gate ɗin Hamza ya kwanƙwasa, daga ciki mai gadin yace "waye,
Hamza yace "mune,
Buɗe ƙofar akayi, mai gadin yana ganin Sam ya washe baki yana gaida su bayan sun amsa yabasu guri suka shiga,
Sai taji nauyi ta ƙara cemasa a'a sai kawai ta miƙa hannu zata karɓa badan tana soba saidan kawai kar tamayar da hannun kyauta baya, ga mamakin ta sai taga kawai ya janye daga miƙo hannun da tayi sai ya nufi bakin ta dashi, ƙin buɗe bakin tayi sai da taga ya haɗe rai yana wurga mata harara sannan ta buɗe small mouth ɗin shikuma ya saka mata abakin tana shirin gutsirar ƴar kaɗan kawai ya danna mata ita abaki gaba ɗaya,
Waro ido tayi tana ƙoƙarin cire hannun sa ta ciro ta saboda ta cika mata baki bazata taɓa iya taunawa,
Hannu yasa ya rufe mata bakin yanda bazata iya fito da iyaba, da taga dai ba sarki sai Allah haka ta shiga taunawa da ƙyar harda ƙwallar wahala haka Meer yasata ta cinye ta tas sannan ya sakar mata bakin, yana saki kuma yaƙara dauko wata yashiga ɓare ta, ai tana ganin haka tayi saurin miƙewa zata gudu saidai bataje ko ina ba ya cafkota, yana miƙewa tsaye yace "ina zaki ai sai kinyi maganar da ta kawoki kamar kuma yanda kikace mufara shanye choculate ɗin zakiyi maganar to sai ki zauna sai kin shanye su duka sannan kiyi maganar idan kinason fita daga ɗakin nan,
Zaro ido ta shiga yi tana faman rarraba ido tace Allah kuwa na ƙoshi kuma ai mungama magana daman itace ta kawo ni kuma mungama, choculate kuma kasha kayarka na ƙoshi tunfar ko da nace kaban ai rowa kamin dan haka wacce kaban da mugunta ta isheni, daman nace mug...., Da sauri tasa hannu ta toshe bakin ta, bata ƙarasa kalmar mugun ba tunawa da tayi yace kar tasake ce masa mugu,
Wani mugun kallo kawai ya watsa mata sannan ya koma ya zauna yace "dawo ki zauna,
Ganin yayi maganar serious ba wasa, yasa ta dawo da baya ta zauna a inda ta tashi................,
*************************
___________ *SAM*
Tun ranar da yaje gidan da yakai sumy akace masa ta gudu tun loƙacin baiƙara samun nutsuwa, ya dawo gida ya rasa inda zai tsoma ransa, yaji daɗi, ga shettima abokin shawarar sa tunda ya tafi gida shima bai ƙara dawowa masarautar ba, kuma yafiso suyi maganar face to face shiyasa bai kirasa ba....,
Yanzuma yana zaune akan gado ya zabga tagumi yana tunanin samun mafita da ta inda zai fara nemanta gashi kuma ƙarewa ma babu wanda yasan ya ɗauko ta, baisan ta inda zai fara tunkarar wani da maganar ba,
Jiyayi andafasa da sauri ya É—ago yazuba rinannun idanuwansa akan fuskar sa kallo É—aya kuma yayi masa ya janye saboda bayaso ya karanci halin da yake ciki,
Me yake damunka? Hamza ya jefa masa tambayar,
Batare da ya kallesaba yace ba komai kawaidai kainane yake É—anyi min ciwo, kuma nasha magani yanzu zai daina kar kadamu, yana faÉ—ar haka yaÉ—an gyara zaman sa ya kishingiÉ—a, yana dafe kansa,
Gefensa Hamza ya samu ya zauna yana kallon sa cike da nazartar sa, saboda tun loƙacin da abu yafaru sam yajasa ajiki tun bayaso har ya ɗan fara sakin jiki dashi, kuma sam yasa ya tattaro kayan sa yadawo part ɗin sa da zama amma duk da haka Hamza ba kullum yake zama ba a part ɗin kullum yana waje bayan gidan yana zagaye dan yafi son ya ringa keɓewa shikaɗai hakan yafi masa daɗi dan ko abinci ma bai fiya zama ya ciba wani loƙacin ma sai Sam yayi masa dole yake ci,
Cikin sanyin murya Hamza yace "kayi haƙuri zan shiga hurumin da banawa ba na fahimci kana cikin damuwa, bankai matsayin da zan san damuwar kaba, dan haka basai ka gaya min matsalar kaba, shawara zan baka yakamata kasamowa kanka mafita zaman ɗaki ba abun da zai haifar maka sai wani ciwon, kamata yayi kaje kasanar da mahaifiyar ka ko kasamu wanda kafi kusanci dashi kasanar dashi faɗar damuwa koda baza ayi maka maganin taba idan ka fitar da ita zaka ɗan samu sassauci akan yanda kakeji, duk wanda yaganka zai gane kana cikin matsananciyar damuwa, ba iya ciwon kai ke damunka tun ba yauba na lura dakai, dan Allah ka daure ko abokin kane ka sanar dashi matsalar ka kar kabari tayi maka illa a ɗaki, Sosai Hamza yashiga nusar dashi illar riƙe damuwa batare da ka fitar da ita ba hakan na ƙaramin cutar da ɗan adam take ba,
Kalaman sa kam sunyi aiki akan Sam sosai yaji maganar sa, kuma sai yaji ba daɗi da yace yasan baikai matsayin da zai san damuwar sa, hakan ba ƙaramin kashe mishi jiki yayi ba bayaso yaringa tunani wani iri da zai ringa sakashi damuwa shiyasa yake jansa ajiki dan ya manta da duk abun da yafaru, amma furucinsa na yanzu kwata kwata baiyi masa daɗi ba,
Dan haka yayi saurin tashi zaune yana fuskantar Hamza da kyau, yace "ko ɗaya ba abun da kake tunani bane indai har zan iya sanar da mahaifiyata ko abokina ko wanda nake da kusanci dashi to dole kaima kana cikin ɗaya daga cikin su, yanda zan ɗaukesu kaima haka zan ɗauke, Nagode da nuna kulawar ka agare ni tabbas akwai abun da yake damuna amma narasa mafita kuma bana tunanin ko na gayawa wani zai iya samamin ita, tunanin ya tsaya gaba ɗaya narasa yanda zanyi Hamza, yaƙarasa maganar cikin sanyin jiki,
Hamza ma jikin sane yayi sanyi kuma yaji daɗi sosai jin matsayin da yabasa mai girma haka duk da laifin da mahaifiyar sa ta aikata musu amma babu wani wanda yake nuna masa kyara da tsangwama, musamman Sam da yafi kowa jansa ajiki hakan ba ƙaramin daɗi yake masa ba,
A hankali shima yafara magana da cewa "indai har dagaske ne abun da kafaɗa to ina mai roƙonka da kagaya min nikuma in sha Allah zanne ma maka mafita da yardar Allah zan taimaka mana,
Ɗan murmushin yaƙe Sam tare da jinjina kai batare da yace masa komai ba, yakai wajen minti bakwai kafin yaɗanyi gyaran murya sannan ya shiga basa labarin abun da yafara tsakanin sa da sumy ɗin tundaga farkon haɗuwar su har ƙarshe, inda yakaita gidan ƙanwar kakar sa, (Ammah) yace kuma yaje amma ta sanar dashi suma tashi sukayi suka nemeta suka rasa.....,
Hamza najin haka yasaki murmushi mai ƙayatarwa da ya daɗe baiyi irinsa ba, da hakan har saida ya bawa Sam mamaki, danshi tunda suka zauna na bai taɓa ganin murmushin saba,
Batare da ya daina murmushin ba yace "ashe ƙanin nawa soyayya ya faɗa, kace munkusa shan biki, macece daman tasaka gaba haka ka kama damuwa har da su rama, tokwa dole intashi tsaye karka damu zamu nemo maka ita duk inda ta shiga afaɗin duniyar nan, bare ma nasan ba wani nisa tayi, tana kusa,
Tunda yafara magana sam yake kallon sa cike da mamakin kalaman sa shi yana masa maganar serious amma shi yazo yana masa wata irin magana marar ma'ana, haushi yaje yakamasa take ya shiga yi masa wani irin kallo saida yabari yayi shiru sannan yace "kaga nifa ba abun da kake tunani bane kanajin yanda nabaka labarin yanda take rayuwa abun tausayi kuma kana min wata maganar daban inma wasa kake Please mubar wanann maganar banaso inbaza ka taimake ni dan Allah ba to kabarshi yana faɗar haka ya miƙe cike da jin haushin Hamza,
Da sauri Hamza ya miƙe yana ƙumshe dariyar sa da take shirin fitowa, sannan yace "tuba nake kayi haƙuri bazan ƙara ba, yanzudai abar ko wane zance muje neman yanzu nan basai anjima ba, amma zamu fara zuwa gidan kakar taka kuma kar kasanar da ita muje kawai yana faɗar haka ya kamo hannun sa yana ƙara cewa muje,
Sam kamar wani soko haka yake kallon Hamza cikin rashin fahimtar inda zancen sa ya dosa, yana buɗe baki zaiyi magana Hamza yayi saurin da katar dashi yace "karkace komai pls muje kawai, haka kwa Sam yayi shirun ya shiga binsa tunani fal cikin sa shiyasa ma yakasa tantance wane iri zaiyi, bashi da zaɓi da ga wuce ya bisa ɗin,
a haka suka fito daga É—akin har suka wuce falo suka fito part É—in fulani suna fitowa sukaga anfita da gudu daga cikin falon,
Ai Hamza baijira wata wata ba ya kwasa aguje yabi bayan wanda ya fita daga ciki, yana fita ya hango wata mace, ta shiga wani part ɗin, girgiza kai yayi yace "zaki ci ubanki Ubaira, duk ma wanda ya aiko ki zakiyi bayani, yana cikin wanann maganar Sam yaƙaraso gurin yace "wacece wacce ta fito ɗin ka ganta ina tayi,
Ɗan dafa kafaɗar sa yayi ya bubbuga yace "muje kawai komai yana da loƙaci yanzu ba wancen loƙacin bane, zamuyi maganar idan mungama waccen, wata mata ce kuma nasanta naganeta naga kuma inda ta shiga ai anyi mai wuyar, dan haka kar kadamu da wannan kaji da abun da yake gabanka, muje yafaɗa yana yin gaba,
Yaudai Sam ya zama ɗan kallo sai yanda Hamza yayi dashi haka, yabi bayansa har suka ƙarasa inda motar sa yake, driver yazo zai buɗe masa ƙofa Hamza ya dakatar dashi yace "yaje sannan ya buɗewa Sam motar da kansa ya shiga shikuma ya shiga driver seat yashiga tare da tayar da motar yajasu suka fice daga masarautar Sam yana masa kwatance, ahaka har suka ƙarasa unguwar abakin gate ɗin gidan Hamza yayi parking,
Sam ne ya É—ago ya kalle sa ganin yayi parking a waje yace "naga ka tsaya anan mushiga mana,
Batare da Hamza ga kallesa ba ya girgiza masa kai, sannan ya buɗe motar ya fita ya zagayo ya buɗewa Sam, shima Sam bai ƙara magana ba, ya fito kawai atare suka nufi gate ɗin gidan, suna zuwa bakin gate ɗin Hamza ya kwanƙwasa, daga ciki mai gadin yace "waye,
Hamza yace "mune,
Buɗe ƙofar akayi, mai gadin yana ganin Sam ya washe baki yana gaida su bayan sun amsa yabasu guri suka shiga,