Sashe 89
Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Dariyan ya kara saki kafin yace"ki bani minti goma zan kara kiranki..!
Kit ya Datse kiran sai ta koma ta zauna gefen gado tana share zufan goshinta Dayyaba ta cuceta tun farko taso ta bari su kawar da Amina tace a kyaleta ita din bazata zame musu matsala ba sai gashi yanzu Ta zame mata ciwon ido bata fatan Amina ta Tare agidan Umar tana hango Tarin abubuwan da bazata so faruwarsu ba nan gaba..
Abunda bata sani ba Bakin Alkalami ya Riga ya bushe..Da sun sani..Dama ace suna Tara sani da Allah da basu bar Amina ba..Domin watarana itace Sillar bankadaran sirrikansu..!
Itace kuma zata Shiga Tsakaninsu da cikar Duka Burikansu..!
Tana zaune tana faman Tunanin mafita Minti goma na cika Mallam ya Sake kiranta Hannunta na rawa ta Dauka bai bari ma ta fara mgana ba ya Fara mgana cikin Sauri da karfi yana Fadin"Kin makara Madina..Kin manta na Fadamiki Mallam yunusa yafi karfinki..?Na fada miki bayan ke acikin matansa akwai wacce taso ta mallakesa bai samu ba itama an fadamata Allah yana Tsare bawansa Mijinku yana da Tsari mutum ne mai Ibada da addini aljanun mu bazasu iya Tunkaransa ba..!
Da sauri Anty Amarya ta katseshi da Fadib"Hajiya fa..?
Sai da yayi jim kafin yace"Bazan iya Tankwara zuciyarta Lokaci daya ba Madina itama bazaune take ba..Sannan Lokaci ya kure miki..Nagani Dole yarinyar ta tare..Na hango wani Duhu sannan naga Haske guda Biyu na wata da kuma kananun Taurari Madina sai dai acikin hasken Duhu ya mamaye ganina ban fahimci wani abu ba..!
Anty Amarya taji kamar tayi Fitsari Saboda Tsoro Cikin rawan murya tace"Menene Mafita mallam kaina ya Kulle..?
Mallam yace"Muna kan Bincikenmu ne Madina..ammh Zata tare tabbas..Sai dai zan kara Lalata Tunanin yarinyar wajen kara yawan Tsiwarta da rashin Da"a ga shi Mijin..Sannan na saka tashin Hankalin a Tsakaninsu yadda zaman bazai Dade ba zai lalace na fada miki Aiki Daya muka taba yi kan Shi yaron ya kamasa yanzu haka aljanunmu baza su iya Tunkararsa ba,Yana da Tsari sannan iyayansa Biyu suna Tsaye a kansa ne Shiyasa aikin namu zak fi karfi kan yarinya da dama Tun farko mun samu nasara akanta Sarrafa Tunaninta bazai mana Wahala ba..Kada ki yi wani yunkuri..Zata tare tabbas in kika hana Faruwar haka Madina wani kullin zai Lalace kuma Faruwar haka tamkar Rugujewar Duka aikin ki ne ki kiyaye..!
Kit Kawai taji Anty Amarya Cikinta taji yana Faman juya mata Innalillahi kawai take fadi afili in Har asirin data Binne ya bayyana ta shiga uku ta Lalace Cikinta ne yayi wani yi kara Kuuuu..Data saki waya ma bata sani ba,Ta kwashi gudu zuwa Tiolet kafin ya Zubo mata tana hawa kan sit din Kikaji Zuu..Zuuu..Sai kuma zufa ta koma ta jingina da bango tana ajiyar zuciya Yadda take jin kanta kamar zai Rabe gida Biyu..!
Mafita take nema ido Rufe kafin komai ya kwace mata ta Dade kan masai din tana zawo zawon tsoro da Firgita kafin ta Dauraye jikinta ta fito Tana ji ana kiran wayarta sai da ta Fito ta Duba Dayyaba ce Tsaki taja Domin duk itace silar lalacewar komai nata in da ta amince sun Kauda Amina da yanzu wata mganar ake yi ba wannan ba,Ta fara Tunanin ko Dayyaba ta na so ta juya mata baya ne saboda ita ta samu cikar nata Burin eh mana ko bata samu duka ta fara Hawa matakin nasara Yaya ta bar gidan Duniya ya'yanta sun dawo karkashinta sa"idu yanzu nata ne ita kadai ai kadan ya rage mata ta cika Burinta ita kuma yanzu abubuwa sun fara Lalace mata daga wannan sai wannan kuma duk sanadin wannan shegiyar yarinyar da shiyasa bata taba kaunarta ba..!
Gefen gadon ta koma ta zauna tayi Tagumi hannu Biyu tana Tunanin mafita ta Dauki tsawon Lokaci ahaka batasan sakina ta shigo ba sai da taji Muryanta saman kanta sannan ta Dawo Hayyacinta yadda idanuwanta suka Fada ne Lokaci Daya yasa Jikin Sakina ya kara yin sanyi cikin Damuwa tace"Anty na jiki shuru ne tun dazu shiyasa na shigo naga ko Lafiya..Na sameki cikin Tunani ina ta mgana baki jini ba..!?
Anty Amarya ta kasa mgana Sakina ta Kurama ido na wani Lokaci kafin tayi Zaraf ta mike tana Fadin"Ke wani ya ganki sanda zaki shigo..?
Da sauri ta Girgizakai ajiyar rai ta Sauke kafin tace"Tashi tashi maza mu tafi..!
Sakina tace"ina kenan Anty..?
Tana kokarin Daukan Hijabinta Cikin Wardrope dinta tace"Gidanki zan maidake sakina..Dole zaki koma Domin chan din ne ya Dace Dake..!
Sakina ta saki baki kafin tace"Yanzu sai naje nayi zaman kishi da wannan yarinyar..?Haba Anty kin manta kin Fadamin hakan bazai faru ba indai kina Numfashi..!
Anty Amarya da ranta ya gama baci ta Juyo tana Fadin"Ke sakina kada ki koma don Ubanki..In kin koma kinci Ubanki nace..to gani da Numfashina Amina zata tare agidan da na gama Tsara ke kadai zaki dinga juyi acikinsa..Wannan karon ba kamar Zuwan wannan balarabiyar nan bane..Wannan mganar ta girmama Hajiya da Mallam ne kuma kinsan babu mai ja da su..ki zauna kina ji kima gani Amina zata tare ta samu Ciki ta Haihu ni dake mun zama yan kallo,ke ba auran ba,ba kuma miji ba Sannan ni kuma kin jamin raini sannan kin saka mafarkina na mallakan gidanan ya tashi a banza Sakina Kada kije ki koma ki zauna ni Dake mu Taru mu rushe gabadaya..!
Kit ya Datse kiran sai ta koma ta zauna gefen gado tana share zufan goshinta Dayyaba ta cuceta tun farko taso ta bari su kawar da Amina tace a kyaleta ita din bazata zame musu matsala ba sai gashi yanzu Ta zame mata ciwon ido bata fatan Amina ta Tare agidan Umar tana hango Tarin abubuwan da bazata so faruwarsu ba nan gaba..
Abunda bata sani ba Bakin Alkalami ya Riga ya bushe..Da sun sani..Dama ace suna Tara sani da Allah da basu bar Amina ba..Domin watarana itace Sillar bankadaran sirrikansu..!
Itace kuma zata Shiga Tsakaninsu da cikar Duka Burikansu..!
Tana zaune tana faman Tunanin mafita Minti goma na cika Mallam ya Sake kiranta Hannunta na rawa ta Dauka bai bari ma ta fara mgana ba ya Fara mgana cikin Sauri da karfi yana Fadin"Kin makara Madina..Kin manta na Fadamiki Mallam yunusa yafi karfinki..?Na fada miki bayan ke acikin matansa akwai wacce taso ta mallakesa bai samu ba itama an fadamata Allah yana Tsare bawansa Mijinku yana da Tsari mutum ne mai Ibada da addini aljanun mu bazasu iya Tunkaransa ba..!
Da sauri Anty Amarya ta katseshi da Fadib"Hajiya fa..?
Sai da yayi jim kafin yace"Bazan iya Tankwara zuciyarta Lokaci daya ba Madina itama bazaune take ba..Sannan Lokaci ya kure miki..Nagani Dole yarinyar ta tare..Na hango wani Duhu sannan naga Haske guda Biyu na wata da kuma kananun Taurari Madina sai dai acikin hasken Duhu ya mamaye ganina ban fahimci wani abu ba..!
Anty Amarya taji kamar tayi Fitsari Saboda Tsoro Cikin rawan murya tace"Menene Mafita mallam kaina ya Kulle..?
Mallam yace"Muna kan Bincikenmu ne Madina..ammh Zata tare tabbas..Sai dai zan kara Lalata Tunanin yarinyar wajen kara yawan Tsiwarta da rashin Da"a ga shi Mijin..Sannan na saka tashin Hankalin a Tsakaninsu yadda zaman bazai Dade ba zai lalace na fada miki Aiki Daya muka taba yi kan Shi yaron ya kamasa yanzu haka aljanunmu baza su iya Tunkararsa ba,Yana da Tsari sannan iyayansa Biyu suna Tsaye a kansa ne Shiyasa aikin namu zak fi karfi kan yarinya da dama Tun farko mun samu nasara akanta Sarrafa Tunaninta bazai mana Wahala ba..Kada ki yi wani yunkuri..Zata tare tabbas in kika hana Faruwar haka Madina wani kullin zai Lalace kuma Faruwar haka tamkar Rugujewar Duka aikin ki ne ki kiyaye..!
Kit Kawai taji Anty Amarya Cikinta taji yana Faman juya mata Innalillahi kawai take fadi afili in Har asirin data Binne ya bayyana ta shiga uku ta Lalace Cikinta ne yayi wani yi kara Kuuuu..Data saki waya ma bata sani ba,Ta kwashi gudu zuwa Tiolet kafin ya Zubo mata tana hawa kan sit din Kikaji Zuu..Zuuu..Sai kuma zufa ta koma ta jingina da bango tana ajiyar zuciya Yadda take jin kanta kamar zai Rabe gida Biyu..!
Mafita take nema ido Rufe kafin komai ya kwace mata ta Dade kan masai din tana zawo zawon tsoro da Firgita kafin ta Dauraye jikinta ta fito Tana ji ana kiran wayarta sai da ta Fito ta Duba Dayyaba ce Tsaki taja Domin duk itace silar lalacewar komai nata in da ta amince sun Kauda Amina da yanzu wata mganar ake yi ba wannan ba,Ta fara Tunanin ko Dayyaba ta na so ta juya mata baya ne saboda ita ta samu cikar nata Burin eh mana ko bata samu duka ta fara Hawa matakin nasara Yaya ta bar gidan Duniya ya'yanta sun dawo karkashinta sa"idu yanzu nata ne ita kadai ai kadan ya rage mata ta cika Burinta ita kuma yanzu abubuwa sun fara Lalace mata daga wannan sai wannan kuma duk sanadin wannan shegiyar yarinyar da shiyasa bata taba kaunarta ba..!
Gefen gadon ta koma ta zauna tayi Tagumi hannu Biyu tana Tunanin mafita ta Dauki tsawon Lokaci ahaka batasan sakina ta shigo ba sai da taji Muryanta saman kanta sannan ta Dawo Hayyacinta yadda idanuwanta suka Fada ne Lokaci Daya yasa Jikin Sakina ya kara yin sanyi cikin Damuwa tace"Anty na jiki shuru ne tun dazu shiyasa na shigo naga ko Lafiya..Na sameki cikin Tunani ina ta mgana baki jini ba..!?
Anty Amarya ta kasa mgana Sakina ta Kurama ido na wani Lokaci kafin tayi Zaraf ta mike tana Fadin"Ke wani ya ganki sanda zaki shigo..?
Da sauri ta Girgizakai ajiyar rai ta Sauke kafin tace"Tashi tashi maza mu tafi..!
Sakina tace"ina kenan Anty..?
Tana kokarin Daukan Hijabinta Cikin Wardrope dinta tace"Gidanki zan maidake sakina..Dole zaki koma Domin chan din ne ya Dace Dake..!
Sakina ta saki baki kafin tace"Yanzu sai naje nayi zaman kishi da wannan yarinyar..?Haba Anty kin manta kin Fadamin hakan bazai faru ba indai kina Numfashi..!
Anty Amarya da ranta ya gama baci ta Juyo tana Fadin"Ke sakina kada ki koma don Ubanki..In kin koma kinci Ubanki nace..to gani da Numfashina Amina zata tare agidan da na gama Tsara ke kadai zaki dinga juyi acikinsa..Wannan karon ba kamar Zuwan wannan balarabiyar nan bane..Wannan mganar ta girmama Hajiya da Mallam ne kuma kinsan babu mai ja da su..ki zauna kina ji kima gani Amina zata tare ta samu Ciki ta Haihu ni dake mun zama yan kallo,ke ba auran ba,ba kuma miji ba Sannan ni kuma kin jamin raini sannan kin saka mafarkina na mallakan gidanan ya tashi a banza Sakina Kada kije ki koma ki zauna ni Dake mu Taru mu rushe gabadaya..!