Sashe 65
Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
****
Cikin wadanda Daurin Auran Amina da Danmallam ya shiga kunnensu yaya na ciki ita da Hajiya da Mamanmu kai kaf wadanda ke gidan sun ji hadda Amina uwar gayyar Domin tatashi alokacin Hamida ta taimaka mata tayi wanka tayi alwala tana Rama Salolinta ta idar kenan tana Zaune Saman Darduma alokacin ma Tunanin Aminu take da Tunanin Halin Dayake ciki.
Kamar mafarki Taji muryan Ladanin nan yana bayyana sunanta da na Ya Danmallam amtsayin mijinta da aka Daurama taaure yanzu nan.
Ta Rude kanta kamar ya Kulle domin bata gane komai ba Sama sama take jin Muryan Mamanmu Daga Tsakar gida inda suka zauna tun bayan Dawowarsu daga asibitu tana Fadin"Kunji Abunda naji kuwa..?
Kamar Naji ana Fadin an Daura ma Amina aure da Danmallam..ku Saurara,kuji..!
Suma sun ji din sai dai sun kara kasa,kunni Saboda su gasgata,Hajiya kuwa tun jinta na Farko ta tabbatar da Duk abunda taji gaskiya ne..Mallan ne fa tasani Daman shurunsa Zai iya zama koma menene..!
To duk abunda akeyi a masallacin kamar agidansu akeyi saboda lasifukun masallacin akwai kara sosai,Radau suka sake jin wannan al"amarin Daya basu matukar mamaki Yaya Dake Dakinta Tana zaune ne sai da ta mike yayinda ya Zeena ta kwalalo ido tana Fadin"Wlh Mamanmu da gaske ne..Amina ce..!
Hamida da Hanne suka kalli juna Cikin mamaki kafin Hanne ta Rumtuma Dakinsu Hamida tana Fadin"Amina..Amiaa..Kin ji an Daura miki aure da ya Danmallam yanzu a masallaci..?
Kallonta Amina takeyi da manyan Idanuwanta da suka Zama wani irin Cikin wani yanayi tace"Naji..Naji Hanne..ammh bangane komai ba wani Danmallam din..?
Ni Umar naji an ce fa..?
Tafada cikin wani yanayi Hamida ce da ta shigo cikin wani yanayi tace"Shine Umar din Amina..Yayansu Hanne..Mijin Anty Sakina da Anty Sarood wanda ke zaune a madina..!
Cak Numfashi Amina ya Tsaya ta Fara Kokuwa dashi bata samu zarafin mgana ba taji muryan Yaya tana Fadin"Hajiya kinsani..?meyasa kikabari Mallan yayi haka..?
Amina bata dace da kamilalle irin Umar ba..Bata dace dashi ba sam..bai kamata kuyi haka ba..!
Sai kuka,acikin ranta kuma wani Sasaauci taji Tana ganin kamar Addu"anta na Shekaru ne Allah ya amsa sai dai Tana jin Tsoro tana jin tsoron An Hada Kamili kamar Umar da Amina kada ta zama mai sonkai kada taso yarta Shiyasa tayi mgana..!
Hajiya kuwa tana zaune sai Mirmishi take saki Annushuwa ta bayyana acikin ranta kafin tace"Sun Dace Hadiza..Duk abunda kikaga Mallam ya yanke mai kyau ne..Naki addu"a ne Allah yasa Alheri muka kulla..Allah yasa su aminan juna ne..!
Da karfi Mamanmu ta amsa da Ameen tana sharan kwallah tace"Yaya Amina fa y'arki ce..Tayaya zaki rika Fadin mgana mara kyau akanta ya zataji in taji abunda kike fada!
Tana mgana tana sharan kwallah..!
Amina Daga cikin Dakinsu Hawaye suka kwanyomata tace"Naji..Naji Mamanmu naji..Gaskiya ta Fada ban dace ba..Ban dace ba..!
Batasan Lokacin da wani kuka ya kwace mata ba Lokaci Daya tana Fadin"Wlh bansani ba..Bansan wannan kaddaran ke Bibiyata ba da Ban fara son ka ba Aminu..Wlh bansani ba..!
Taausayinta ya kama Hanne da Hamida suka karisa gareta suka Rumgumeta suma sai kuka Riris kamar anyi mutuwa..!
Zuwa Lokacin Wannan Daurin auran mai Cike da Bazata da mamaki ya kama Yaduwa a gidajen nan guda Biyu Anty Amarya sai da tayi suman Wucin gadi bata kara gasgata mganar ba sai Da shamsu ya shigo ya kara Tabbatar musu agabansu akayi ita da Hajiya Nasara,Haj.uwa na shashenta bata fito ba Duk da tasan abunda ya Faru domin taji..!
Alokacin da Kowacce take kiran ya"yanta masu aure na nesa tana Fada musu Anty Amarya bata cikin natsuwa ballatana ta iya kiran wani ta Fadamai awannan gabar abubuwan sun bala'in shammatanta
Abunda kowa bai sani ba alokacin Baba Mallam na cikin Falomsa na Shashensa tare da baki Daga Yola..!
Yana gama wayar nan da Umar Motoci biyu suka gyara parking kofar Gidansu kuma wajensa suka zo ya karbesu hannu Biyu ya kuma Saukesu afalonsa zuwa Lokacin mutane sun fara watsewa..!
Jikinsa yayi sanyi da yaji kamar yayi gaggawa AMINU ne saurayin Amina da iyayansa sun zo neman auran Amina da kuma ban Hakurin abubuwan da suka faru..
Ashe ashe jiya da dadaddre Aminu Daga Gumel yola ya wuce Allah ne ya kaisa Lafiya yaje gaban Baba Alhaji ya Fadamai komai yana kuka da Rokon suje Gumel suba ma iyayan Amina Hakuri su bashi auranta sai dai abunda bai sani ba sun makara..!
Mallam yaga Dattakon Alhaji Baba yaji matukar kunya alokacin Dayake Fadamasu Amina ta haramta ga Aminu yanzu taron chan na waje na Daurin auranta ne..!
Yana ganin wanda aka kira da Aminu ya tashi ya fita yana Rangaji hawaye Sunaa zuba Daga idonsa.
Sai yaji jikinsa yayi sanyi yaa ji aransa kodai yayi gaggaawa ne..?
Aminu Dakyar ya kai kansa Bakin Motocinsu da suka zo dashi Wayarsa ya Dauko biyu biyu yake gani da haka ya Kira Nenne..!
Tana ganin kiransa gabanta ya Fadi Daman kiran nasa take jira tana Dauka tace"Aminu ya ake ciki..?
Cikin karyewar murya yace"Na rasata Nenne..Nasara MEENATA..
Na makara Nenne an Daura mata aure da wani bani ba..!
Yana gama fadin haka ya Datse kiran ya Sulale nan kasa Dirshen ya Hada kansa da gwiwa yana kuka kukan Rabuwa da masoyi Rabuwa ta Har Abada..!
Nenne Dake cikin gidansu na Yola gidan Alhaji Baba yayyinta da kannenta sun zagayeta suna tambayata Lafiya Cikin fitar Hawaye ta kalli Mahaifiyarsu tace"Hajjo ya rasata..Aminu ya rasa Amina....an daura mata aure da wani kafin su isa..!
Gabadaya suka hada baki wajen fadin"Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un..!
Sun sani Aminu zai samu matsala Kaddaran ta riga fata duk wani ahalin gidannan yasan yadda Aminu yake kuka yana rokon Alhaji Baba yaje yane masa auran Amina..
Ya Aminu zai yi..?
Bakin Alkali ya riga ya bushe..!
Zanen kaddaransa bata Amina bace..Kila na watace chan Dabam
Inda ya sani..Dama..Dama ace bai Hadu da Amina ba..Dama ace komai daya faru mafarki ne..!
*Janafty*
[11/3, 2:05 PM] Sweet sis: *TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*
_Wannan shafin jinjina ce da godiya gareku masoyana a duk inda kuke masu Sharhi da masu fatan Alheri musamman yan Group dina na TA FITA ZAKKA COMMENTS SECTION da ku yan JANAF NOVELLA Tare da duka sauran gidajen marubuta da ake yin sharhin wannan Littafin nagani kuma na yaba naji dadi Allah ya bar zumunci gaisuwa ta musamman zuwa gare ku yan wattppdians kuma kuna kokari sosai nagode Allah ya bar zumunci.._
*🅿️22*
Zuwa dare duk wanda ya kamata yaji Labarin Auran Amina da Danmallam yaji,kowa mamaki kamasa yake yi in yaji Domin agabadaya da Dubawa ta mahanga ta Dan adam Amina bata Dace da Rayuwar Danmallam ba sai dai Ina Allah shi ke Tsara dukkan Lamuran sannan kuma ya zartar ya riga ya Dora alkalamin kuma ya Bushe akan Amina da Umarun dan bazanga..!
Aba yana asibiti ya jafar ya kirasa ya sanar dashi maimakon ya shiga bakinciki da takaici kamar yadda ransa ya darsu da Tunanin Baba Mallan yayi gaggawa domin Amina bata dace da Rayuwa irin ta kamili Natsattse Irin danmallam ba sai kuma sai yaji kamar zuciyarsa tayi son kai yaga kamar ita diyar tasa irin Mijin Daya dace da ita kenan baisan Lokacin Daya Daidaici gabas ba ya Fadi yayi sujudul Shukur ga Allah ya Dago yana Hawayen Farincikin da bai taba Zaton Daga jiya zuwa Dazu zai iya Fuskarta haka ba yadai ce zai aurar da Amina ammh acikin ransa yanajin kamar bai kyautu ba yana ji kamar wani al"amari zai faru ashe wannan al"amarin ne mai Daraja tuni kimar Baba Mallam ta kara Hauhawa acikin Zuciyarsa ya tabbata ko mahaifinsa Aminu gusai na Raye iyakar kaunar da zai bayyana masa kenan..!
Bangaran Amina kuma tun Lokacin Dataji labari data fara kukan nan bata Daina ba,Har Hajiya Babba da mamanmu sai da suka taru akanta suna ta bata baki bayan sun Fatattaki su Hamida Dake tayata kuka,Agabansu sai tayi kamar taji Duka Nasihansu ta daina Abu Daya ke mata yawo Aminu ta kasa gane wannan wata irin kaddarace da zata Raba ta da masoyinta ta kaita inda Har Abada baza"a taba sonta ba..Wannan wata irin kaddarace haka take ta Tambayan kanta..!
Hajiya Babba na tafiya Amina ta cigaba da gunjin kukanta har ta su Hamida sun daina sun koma suna Lallashinta,Ammh taki daina kuka Mamanmu kuma gajiya tayi ta rabu da ita ya Zeena ce ke kitchen tana samar da abunda zasu ci da wanda za"a kaima Aba Dake chan Asibiti suna Tunanin yasan abunda ke faruwa Tunda Baba Mallam baya Zartar da wani abu sai da saninsa shi da Hajiya Babba basu san wannan karon duka bai nemesu ba shi kadai dagashi sai Allah Daya barma Zabi bayaso yayi mgana da wani ko wata su ce ba haka ba shi yasa wannan karon ko Hajiya babba batasan me ya yanke ba Sai Daga baya..!
Tun Mganar da Yaya tayi ma Hajiya Babba ta koma Daki ko motsinta ba wanda ya sake ji,Sai Lokacin da iskancin kukan Amina ya isheta sannan ta fito ba wanda yaji Shigowarta illah Dundun data Dirkama Amina agadon bayanta wacce ke zaune kasa ta Hade kai da Gwiwa tana gunjin kuka alwala ta Dauro Dakyar shima sai da Hanne da Hamida sukayi ta magiya shine ita batayi sallar ba ta koma tana kuka..!
Dukkansu sai karan Dukan sukaji Amina ta bankare baya wannan Hannu shi kadai ne bata saba dashi ba Hannun Yaya ne..!
Cikin wadanda Daurin Auran Amina da Danmallam ya shiga kunnensu yaya na ciki ita da Hajiya da Mamanmu kai kaf wadanda ke gidan sun ji hadda Amina uwar gayyar Domin tatashi alokacin Hamida ta taimaka mata tayi wanka tayi alwala tana Rama Salolinta ta idar kenan tana Zaune Saman Darduma alokacin ma Tunanin Aminu take da Tunanin Halin Dayake ciki.
Kamar mafarki Taji muryan Ladanin nan yana bayyana sunanta da na Ya Danmallam amtsayin mijinta da aka Daurama taaure yanzu nan.
Ta Rude kanta kamar ya Kulle domin bata gane komai ba Sama sama take jin Muryan Mamanmu Daga Tsakar gida inda suka zauna tun bayan Dawowarsu daga asibitu tana Fadin"Kunji Abunda naji kuwa..?
Kamar Naji ana Fadin an Daura ma Amina aure da Danmallam..ku Saurara,kuji..!
Suma sun ji din sai dai sun kara kasa,kunni Saboda su gasgata,Hajiya kuwa tun jinta na Farko ta tabbatar da Duk abunda taji gaskiya ne..Mallan ne fa tasani Daman shurunsa Zai iya zama koma menene..!
To duk abunda akeyi a masallacin kamar agidansu akeyi saboda lasifukun masallacin akwai kara sosai,Radau suka sake jin wannan al"amarin Daya basu matukar mamaki Yaya Dake Dakinta Tana zaune ne sai da ta mike yayinda ya Zeena ta kwalalo ido tana Fadin"Wlh Mamanmu da gaske ne..Amina ce..!
Hamida da Hanne suka kalli juna Cikin mamaki kafin Hanne ta Rumtuma Dakinsu Hamida tana Fadin"Amina..Amiaa..Kin ji an Daura miki aure da ya Danmallam yanzu a masallaci..?
Kallonta Amina takeyi da manyan Idanuwanta da suka Zama wani irin Cikin wani yanayi tace"Naji..Naji Hanne..ammh bangane komai ba wani Danmallam din..?
Ni Umar naji an ce fa..?
Tafada cikin wani yanayi Hamida ce da ta shigo cikin wani yanayi tace"Shine Umar din Amina..Yayansu Hanne..Mijin Anty Sakina da Anty Sarood wanda ke zaune a madina..!
Cak Numfashi Amina ya Tsaya ta Fara Kokuwa dashi bata samu zarafin mgana ba taji muryan Yaya tana Fadin"Hajiya kinsani..?meyasa kikabari Mallan yayi haka..?
Amina bata dace da kamilalle irin Umar ba..Bata dace dashi ba sam..bai kamata kuyi haka ba..!
Sai kuka,acikin ranta kuma wani Sasaauci taji Tana ganin kamar Addu"anta na Shekaru ne Allah ya amsa sai dai Tana jin Tsoro tana jin tsoron An Hada Kamili kamar Umar da Amina kada ta zama mai sonkai kada taso yarta Shiyasa tayi mgana..!
Hajiya kuwa tana zaune sai Mirmishi take saki Annushuwa ta bayyana acikin ranta kafin tace"Sun Dace Hadiza..Duk abunda kikaga Mallam ya yanke mai kyau ne..Naki addu"a ne Allah yasa Alheri muka kulla..Allah yasa su aminan juna ne..!
Da karfi Mamanmu ta amsa da Ameen tana sharan kwallah tace"Yaya Amina fa y'arki ce..Tayaya zaki rika Fadin mgana mara kyau akanta ya zataji in taji abunda kike fada!
Tana mgana tana sharan kwallah..!
Amina Daga cikin Dakinsu Hawaye suka kwanyomata tace"Naji..Naji Mamanmu naji..Gaskiya ta Fada ban dace ba..Ban dace ba..!
Batasan Lokacin da wani kuka ya kwace mata ba Lokaci Daya tana Fadin"Wlh bansani ba..Bansan wannan kaddaran ke Bibiyata ba da Ban fara son ka ba Aminu..Wlh bansani ba..!
Taausayinta ya kama Hanne da Hamida suka karisa gareta suka Rumgumeta suma sai kuka Riris kamar anyi mutuwa..!
Zuwa Lokacin Wannan Daurin auran mai Cike da Bazata da mamaki ya kama Yaduwa a gidajen nan guda Biyu Anty Amarya sai da tayi suman Wucin gadi bata kara gasgata mganar ba sai Da shamsu ya shigo ya kara Tabbatar musu agabansu akayi ita da Hajiya Nasara,Haj.uwa na shashenta bata fito ba Duk da tasan abunda ya Faru domin taji..!
Alokacin da Kowacce take kiran ya"yanta masu aure na nesa tana Fada musu Anty Amarya bata cikin natsuwa ballatana ta iya kiran wani ta Fadamai awannan gabar abubuwan sun bala'in shammatanta
Abunda kowa bai sani ba alokacin Baba Mallam na cikin Falomsa na Shashensa tare da baki Daga Yola..!
Yana gama wayar nan da Umar Motoci biyu suka gyara parking kofar Gidansu kuma wajensa suka zo ya karbesu hannu Biyu ya kuma Saukesu afalonsa zuwa Lokacin mutane sun fara watsewa..!
Jikinsa yayi sanyi da yaji kamar yayi gaggawa AMINU ne saurayin Amina da iyayansa sun zo neman auran Amina da kuma ban Hakurin abubuwan da suka faru..
Ashe ashe jiya da dadaddre Aminu Daga Gumel yola ya wuce Allah ne ya kaisa Lafiya yaje gaban Baba Alhaji ya Fadamai komai yana kuka da Rokon suje Gumel suba ma iyayan Amina Hakuri su bashi auranta sai dai abunda bai sani ba sun makara..!
Mallam yaga Dattakon Alhaji Baba yaji matukar kunya alokacin Dayake Fadamasu Amina ta haramta ga Aminu yanzu taron chan na waje na Daurin auranta ne..!
Yana ganin wanda aka kira da Aminu ya tashi ya fita yana Rangaji hawaye Sunaa zuba Daga idonsa.
Sai yaji jikinsa yayi sanyi yaa ji aransa kodai yayi gaggaawa ne..?
Aminu Dakyar ya kai kansa Bakin Motocinsu da suka zo dashi Wayarsa ya Dauko biyu biyu yake gani da haka ya Kira Nenne..!
Tana ganin kiransa gabanta ya Fadi Daman kiran nasa take jira tana Dauka tace"Aminu ya ake ciki..?
Cikin karyewar murya yace"Na rasata Nenne..Nasara MEENATA..
Na makara Nenne an Daura mata aure da wani bani ba..!
Yana gama fadin haka ya Datse kiran ya Sulale nan kasa Dirshen ya Hada kansa da gwiwa yana kuka kukan Rabuwa da masoyi Rabuwa ta Har Abada..!
Nenne Dake cikin gidansu na Yola gidan Alhaji Baba yayyinta da kannenta sun zagayeta suna tambayata Lafiya Cikin fitar Hawaye ta kalli Mahaifiyarsu tace"Hajjo ya rasata..Aminu ya rasa Amina....an daura mata aure da wani kafin su isa..!
Gabadaya suka hada baki wajen fadin"Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un..!
Sun sani Aminu zai samu matsala Kaddaran ta riga fata duk wani ahalin gidannan yasan yadda Aminu yake kuka yana rokon Alhaji Baba yaje yane masa auran Amina..
Ya Aminu zai yi..?
Bakin Alkali ya riga ya bushe..!
Zanen kaddaransa bata Amina bace..Kila na watace chan Dabam
Inda ya sani..Dama..Dama ace bai Hadu da Amina ba..Dama ace komai daya faru mafarki ne..!
*Janafty*
[11/3, 2:05 PM] Sweet sis: *TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*
_Wannan shafin jinjina ce da godiya gareku masoyana a duk inda kuke masu Sharhi da masu fatan Alheri musamman yan Group dina na TA FITA ZAKKA COMMENTS SECTION da ku yan JANAF NOVELLA Tare da duka sauran gidajen marubuta da ake yin sharhin wannan Littafin nagani kuma na yaba naji dadi Allah ya bar zumunci gaisuwa ta musamman zuwa gare ku yan wattppdians kuma kuna kokari sosai nagode Allah ya bar zumunci.._
*🅿️22*
Zuwa dare duk wanda ya kamata yaji Labarin Auran Amina da Danmallam yaji,kowa mamaki kamasa yake yi in yaji Domin agabadaya da Dubawa ta mahanga ta Dan adam Amina bata Dace da Rayuwar Danmallam ba sai dai Ina Allah shi ke Tsara dukkan Lamuran sannan kuma ya zartar ya riga ya Dora alkalamin kuma ya Bushe akan Amina da Umarun dan bazanga..!
Aba yana asibiti ya jafar ya kirasa ya sanar dashi maimakon ya shiga bakinciki da takaici kamar yadda ransa ya darsu da Tunanin Baba Mallan yayi gaggawa domin Amina bata dace da Rayuwa irin ta kamili Natsattse Irin danmallam ba sai kuma sai yaji kamar zuciyarsa tayi son kai yaga kamar ita diyar tasa irin Mijin Daya dace da ita kenan baisan Lokacin Daya Daidaici gabas ba ya Fadi yayi sujudul Shukur ga Allah ya Dago yana Hawayen Farincikin da bai taba Zaton Daga jiya zuwa Dazu zai iya Fuskarta haka ba yadai ce zai aurar da Amina ammh acikin ransa yanajin kamar bai kyautu ba yana ji kamar wani al"amari zai faru ashe wannan al"amarin ne mai Daraja tuni kimar Baba Mallam ta kara Hauhawa acikin Zuciyarsa ya tabbata ko mahaifinsa Aminu gusai na Raye iyakar kaunar da zai bayyana masa kenan..!
Bangaran Amina kuma tun Lokacin Dataji labari data fara kukan nan bata Daina ba,Har Hajiya Babba da mamanmu sai da suka taru akanta suna ta bata baki bayan sun Fatattaki su Hamida Dake tayata kuka,Agabansu sai tayi kamar taji Duka Nasihansu ta daina Abu Daya ke mata yawo Aminu ta kasa gane wannan wata irin kaddarace da zata Raba ta da masoyinta ta kaita inda Har Abada baza"a taba sonta ba..Wannan wata irin kaddarace haka take ta Tambayan kanta..!
Hajiya Babba na tafiya Amina ta cigaba da gunjin kukanta har ta su Hamida sun daina sun koma suna Lallashinta,Ammh taki daina kuka Mamanmu kuma gajiya tayi ta rabu da ita ya Zeena ce ke kitchen tana samar da abunda zasu ci da wanda za"a kaima Aba Dake chan Asibiti suna Tunanin yasan abunda ke faruwa Tunda Baba Mallam baya Zartar da wani abu sai da saninsa shi da Hajiya Babba basu san wannan karon duka bai nemesu ba shi kadai dagashi sai Allah Daya barma Zabi bayaso yayi mgana da wani ko wata su ce ba haka ba shi yasa wannan karon ko Hajiya babba batasan me ya yanke ba Sai Daga baya..!
Tun Mganar da Yaya tayi ma Hajiya Babba ta koma Daki ko motsinta ba wanda ya sake ji,Sai Lokacin da iskancin kukan Amina ya isheta sannan ta fito ba wanda yaji Shigowarta illah Dundun data Dirkama Amina agadon bayanta wacce ke zaune kasa ta Hade kai da Gwiwa tana gunjin kuka alwala ta Dauro Dakyar shima sai da Hanne da Hamida sukayi ta magiya shine ita batayi sallar ba ta koma tana kuka..!
Dukkansu sai karan Dukan sukaji Amina ta bankare baya wannan Hannu shi kadai ne bata saba dashi ba Hannun Yaya ne..!