Sashe 7
Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kai tsaye suka shiga Kayattacen Falon Dauke da wata sabuwar Sallama,Suna Shiga Kamshin Turaran da Duk wanda yasan Baba malam yasan wannan kamshinsa ne wani Turare ne mai kamshi mai Sanya natsuwa Turaren mai Tsada ne dan Kasar Saudi mai suna Arab Saboda yawan amfani da Turaran yasa Duk inda Malan ke yawan zama kamshin ya kama wajen,Kamar yadda Kamshin ya kama Falon Dayake ma mallakinsa.
Kayattacen Falo ne wanda yaji kayan More Rayuwa na alatu Falon babba ne mai Dauke da Royal Chair da Tattausan Cafet na kamfanin Italiayan.
Sannan Daga gefe chan wata Kofa ce data fita Haraban gidan akwai wani Falo shi na ganawa da bakin Baba Mallam ne,Sannan Daga cikin Falon akwai Kofifin Bedroom Guda Biyu sai Daga shashen Yammah akwai wani Cabet na glass mai girma da Fadi kafe ajikin Bango wanda yake Shake da Littafan addini Kala kala nau"i nau"i Dabam Dabam Sannan Daga gefensa wani katon Tebur ne mai Dauke shima Da Tarin Littafai ba masaka Tsinke,sai Kujera Guda Daya wajen zaman mallam ne in zai yi Nazarin wani Littafi kamar yadda ya saba koda yaushe.
Sai katon Talabijin mai kama da Kamar Mutum yana waje ne saboda Girmansa,Sunna Tv ne ke tashi Acikinta Dauke da Muryan Sheik Haruna Kabir Gombe yana kwararo Wa"azi Cikin Barkwancinsa.
Cikin Lokaci kadan Amina ta gama Nazarin Falon Kafin idanuwanta su sauka kan Mafi Daraja a wajenta,Wanda shi kadai ne bata iya kallonsa Kai Tsaye shi kadai take shakka Da bata iya Hada ido dashi shi kadai ne yasan Wasu abubuwa Game da ita Saboda yana janta ajiki Wanda ko Aba dinsu bai kaisa saninta ba.
Cikin Farimciki gabadaya Fararan Hakoranta suna Waje ne ita ce kan Gaba Hanne na binta abaya zuwa Inda Baba malam ke zaune Saman Daya Daga Cikin Kujerun Falon Hajiya Babba na gefensa Zaune..
Kamar yadda take Farimciki da ganinsa haka shima ya Dago kyakyawan Farar Fuskarsa mai Dauke da Farin gashi Daya Lullube gemunsa Dattijo ne mai Kima mai Daraja mai Dattako masanin Addinin Musulunci Dana Zamani SHEIK YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA kenan Shehin Malami na bangaran Addinin Musulunci da na Sunna Gabadaya ba iya garin Gumel ba Kasa gabaki Daya susan da zamansa yana da kyakyawan alaqa wajen Sauran Malamai sannan kowa na girmamasa Malami ne mai Tsoron Allah da Sanin ya kamata ba Malamin Siyasa ba kuma ba mai ci da addini ba ba ga Jama"ar gari ba Hatta ga iyalan Dake Zagaye dasu sun san karamci da Dattakon Sheik Yunus bazanga.
A kama baya kama da duka ya"yansa Domin shi Fari ne sannan yana da Cikar Fuska da zati Duka ya"yansa sun fi kama da matansa Daya Dayane Cikin Jerin ya"yansa ke kama dashi Shuiyasa har acikin Ransa UMAR NA dabam ne..
Akallah a shekaru bazai gaza 78 aduniya ko ya D'ara ma sai dai yanayin Hutu da jin dadi sun boye shekarunsa yana Sanye da Jallabiya Mai ruwan Madara ya Cire Rawanin kansa,Farin gashin kansa da Rabi da kwata ya koma Fari sai kyali kyalin baki,Wanda Saboda Cire Rawaninsa kansa ya bayyana Fuskarsa Sanye da wani Sirrin Farin Gilashi mai karamai karfin gani Jaridar Rariya ce ta Ranar a Hannunta yana karantawa sanda su Amina sukayi Sallama.
Tun kafin ta karisa Tace Cikin Muryanta"Baba...!
Yana kokarin gyara zaman Gilashinsa yacce"Mamana..Sai yau nake ganinki..?
Yafada yana kallonta Cike da wata Kauna da Allah kadai yasan adadinta
Daidai kafafunsa ta zauna tana Fadin"Baba nazo shekaran jiya kana da baki Hajiya bata fada maka ba..?
Tafada tana kallon Hajiya datayi Saurin Cewa"Na fadamai fa Maamah..Mallam na Fadamaka zuwanta ko..?
Yana Dariya ya dafa kanta yana Fadin"Tafadamin Tsokanarki nake Yanzu Sa"idu ya tashi nake Bidarki sai Hajiya tacemin kina ma Cikin gidan nan nace shikenan Tunda Wajen hannatu kikazo ba wajena ba .!.
Yafada Cikin Mirmishinsa na koda yaushe,Amina ta rike baki Tana yar Dariya Hanne Dake gefenta ta Duka Tana gaida Baba mallam ya amsa yana kallonta kafin yace"Ke kika Rikemin Mamana ko Hannatu..?
Hanne kanta na kasa tace"Baba nima yau ba zuwa na bane..Laifi tayi Ya Jafar yace zai daketa sai ta gudo wajena..!
Baba Mallam yace"Laifi..?ba na Hana su Jafaru tabamin Uwata ba..?na fada musu komai zatayi duka baya gyara Tarbiya Nasiha ne kawai mafita ballatana Duka Duka Mamana nawa take..?nan gaba sai kun yi mamakinta..!
Yafada yana kallon Amina da Ta dan Daga idanuwanta Sama kafin tace"Baba bafa Laifi nayi ba..Gidan kawata naje ta bani kudina..Baba Ranta fa tayi fa tace yau zata bani a makaranta kuma taki zuwa makaranta yau fa Baba ina Laifi Domin na Bita na amso kudina..!
Baba Mallam na yar Dariya yace"Baki da Laifi Mamana..Daman ai kyan alkwari Cikawa..!
Amina tace"Yauwa Baba..nasan Dama kai ne kadai zaka Fahimceni..!
Hajiya na Dariya tace"Daman ai Mallam baya kware miki baya..!
Malam yace"Wa kika Taba ganin ya kware ma Uwarsa baya Zainabu..?duk dan kwarai yana neman albarka ne..!
Hajiya Dariya kadai tayi batayi mgana ba Amina ce ta Zunguri Hanne Tana Fadin"Tashi muje..!
Tafada a Hankali Baba Malam Dake kallinsu tace"Ina zaku..?
Hanne tace"Gida zataje Baba..Zan Rakata ne..!
Agogon Dake manne adakin ya Daga ido ya kallah Goma Saura Kadan kafin ya Dawo da Kallonsa kan su yana Fadin"Dare yayi Mamana yau ba ki kwanciyarki wajen Hannatun taki..!
Amina tace"Baba itafa ke da kwana agidanmu ni na kwana na karshe ko Hajiya..?
Hajiya na Dariya tace"Kwarai kasan abun nasu Team team ne..!
Baba maallam ya gyada kai yana Fadin"To..to hakane..To ke Hanne yanzu Zagayowarki ne kenan..?
Hanne tace"Sai gobe in mun Dawo daga Hadda zan kwana Baba..!
Hajiya ya kallah yana Fadin"Yayi kyau..Hajiya bani Wayar nan Dake kusa Dake..!
Ba musu ta mikamai Wata Lafiyayyiyar waya Fara Samsumg ce,Ya karba yana fadin"ku zauna bari na Kira shamsu yazo ya rakaki Amina Dare yayi..!
Alokacin da aka ambaci Shamsu sai da suka Kalli Juna ita da Hanne Amina ta Kada ido aranta tace"Mugu.com kenan..!
Ammh Afili bazata iya mgana ba, bata ma Baba Malam gaddama Hanne kuwa ai tasan Halin ya Shamsu Duk gidanan yafi kowa mugunta Da Dukan Mutane ko bakamai komai ba.
Baba Malam yana Kokarin Kiran Shamsu Kira ya shigo wayarsa Cikin Mamaki ya kalli Hajiya yana Fadin"Sa"idu ke kirana Hajiya..!
Sunan da aka ambata yasa Amina ta Dago tana kallon Baba Malam
Hajiya kuma cewa Tayi"Kila mamah ake Cigiya..!
Ba musu ya Dauka da Cikakkiyar Sallamarsa kamar ko yaushe Sa"idu Daga chan bangaran yana Zaune afalonsa gefensa Mamammu ce Cikin Girmamawa yace"Allah yasa ban katse maka wani abu ba Baba..!
Baba Malam yace"A"a Sa"idu ina fatan Dai Lafiya..?naga baka Dade da fita ba..!
Aba ya Dukar dakai kamar yana Gaban Malam yace"Daman Maman yara nan ne tasa na kira wai ko Amina tazo nan gidan..!
Mallam yayi Mirmishi Kafin yace"Gata ma kusa dani Sa"idu..Ammh yansu zan saka Shamsu zai Rakota..!
Da Sauri yace"Tayi kwanciyarta nan mana Baba..!
Baba Malam yace"Tace ba ita ke da kwana ba Hannatu ce..Kasan mamar tawa yar Ra"ayi ce..!
Aba yar Dariya kawai yayi domin ya Daina mamakin Kaunar Dake Tsakanin Baba Malam da Amina abaya ya Dauka Domin tana da Sunan Mahafiyarsa ne sai Daga baya ya Gane Kaunace kawai Daga Allah..
Sallama sukayi da juna yana Datse Kiran ya Dago yana kallon Mamanmu Dake gefensa Cikin Basarwa yace"Kin ji tana chan yanzu..Shamsu zai Rakota..!
Daga haka ya cigaba da cin Abincinsa Domin Alkawari yayi ya Daina bari Lamarin Amina na Tadamai Hankali yanzu ma Mamansu ce ta matsa sai ya Kira Malam din yaji ko ta na chan
Tun bayan shigowarsa Duka yaran sun zo sun gaishesa banda Amina yasan bata gidan in tana nan itama Zatazo ta gaishesa.
Mamanmu Tayi Mirmishi kafin tace"Daman Nasam ai bata wuce Gidan Malam din..Nace ka Kira ne Saboda na Kore Bacin ran Dake Kan Fuskarka kan Amina din..!
Bai ce komai ba har ta Fidda rai da zai kara mgana sai chan taji yace"Uhm..Nifa ban Damu ba kawai dai naga ya kamata ko bata Fadama kowa zata fita ba..Ke mai karenta baki isa ta Fadamiki ga ta zuwa ba?..!ko don ita ta saba yin gaban kanta da yin abunda taga Dama..!
Mamanmu ta Bude zatayi mgana ya Daga mata Hannu yana Fadin"Ki kyaleni don Allah..Yau na dawo agajiyae bana son sabon bacin rai..!
Yadda ya fada din tasan Har ransa haka yake nufin yasa ta Hadiye mganarta ta koma gefe tana Sauke Numfashi.
Shi kuma bai kara kallon Inda take ba ya Cigaba da cin Abincinsa Kamar acikin Ransa bai da Damuwa nan kuwa Tsoro ne da Fargaban wani abu kuma man Gaba Amina zata jawomai.
Kayattacen Falo ne wanda yaji kayan More Rayuwa na alatu Falon babba ne mai Dauke da Royal Chair da Tattausan Cafet na kamfanin Italiayan.
Sannan Daga gefe chan wata Kofa ce data fita Haraban gidan akwai wani Falo shi na ganawa da bakin Baba Mallam ne,Sannan Daga cikin Falon akwai Kofifin Bedroom Guda Biyu sai Daga shashen Yammah akwai wani Cabet na glass mai girma da Fadi kafe ajikin Bango wanda yake Shake da Littafan addini Kala kala nau"i nau"i Dabam Dabam Sannan Daga gefensa wani katon Tebur ne mai Dauke shima Da Tarin Littafai ba masaka Tsinke,sai Kujera Guda Daya wajen zaman mallam ne in zai yi Nazarin wani Littafi kamar yadda ya saba koda yaushe.
Sai katon Talabijin mai kama da Kamar Mutum yana waje ne saboda Girmansa,Sunna Tv ne ke tashi Acikinta Dauke da Muryan Sheik Haruna Kabir Gombe yana kwararo Wa"azi Cikin Barkwancinsa.
Cikin Lokaci kadan Amina ta gama Nazarin Falon Kafin idanuwanta su sauka kan Mafi Daraja a wajenta,Wanda shi kadai ne bata iya kallonsa Kai Tsaye shi kadai take shakka Da bata iya Hada ido dashi shi kadai ne yasan Wasu abubuwa Game da ita Saboda yana janta ajiki Wanda ko Aba dinsu bai kaisa saninta ba.
Cikin Farimciki gabadaya Fararan Hakoranta suna Waje ne ita ce kan Gaba Hanne na binta abaya zuwa Inda Baba malam ke zaune Saman Daya Daga Cikin Kujerun Falon Hajiya Babba na gefensa Zaune..
Kamar yadda take Farimciki da ganinsa haka shima ya Dago kyakyawan Farar Fuskarsa mai Dauke da Farin gashi Daya Lullube gemunsa Dattijo ne mai Kima mai Daraja mai Dattako masanin Addinin Musulunci Dana Zamani SHEIK YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA kenan Shehin Malami na bangaran Addinin Musulunci da na Sunna Gabadaya ba iya garin Gumel ba Kasa gabaki Daya susan da zamansa yana da kyakyawan alaqa wajen Sauran Malamai sannan kowa na girmamasa Malami ne mai Tsoron Allah da Sanin ya kamata ba Malamin Siyasa ba kuma ba mai ci da addini ba ba ga Jama"ar gari ba Hatta ga iyalan Dake Zagaye dasu sun san karamci da Dattakon Sheik Yunus bazanga.
A kama baya kama da duka ya"yansa Domin shi Fari ne sannan yana da Cikar Fuska da zati Duka ya"yansa sun fi kama da matansa Daya Dayane Cikin Jerin ya"yansa ke kama dashi Shuiyasa har acikin Ransa UMAR NA dabam ne..
Akallah a shekaru bazai gaza 78 aduniya ko ya D'ara ma sai dai yanayin Hutu da jin dadi sun boye shekarunsa yana Sanye da Jallabiya Mai ruwan Madara ya Cire Rawanin kansa,Farin gashin kansa da Rabi da kwata ya koma Fari sai kyali kyalin baki,Wanda Saboda Cire Rawaninsa kansa ya bayyana Fuskarsa Sanye da wani Sirrin Farin Gilashi mai karamai karfin gani Jaridar Rariya ce ta Ranar a Hannunta yana karantawa sanda su Amina sukayi Sallama.
Tun kafin ta karisa Tace Cikin Muryanta"Baba...!
Yana kokarin gyara zaman Gilashinsa yacce"Mamana..Sai yau nake ganinki..?
Yafada yana kallonta Cike da wata Kauna da Allah kadai yasan adadinta
Daidai kafafunsa ta zauna tana Fadin"Baba nazo shekaran jiya kana da baki Hajiya bata fada maka ba..?
Tafada tana kallon Hajiya datayi Saurin Cewa"Na fadamai fa Maamah..Mallam na Fadamaka zuwanta ko..?
Yana Dariya ya dafa kanta yana Fadin"Tafadamin Tsokanarki nake Yanzu Sa"idu ya tashi nake Bidarki sai Hajiya tacemin kina ma Cikin gidan nan nace shikenan Tunda Wajen hannatu kikazo ba wajena ba .!.
Yafada Cikin Mirmishinsa na koda yaushe,Amina ta rike baki Tana yar Dariya Hanne Dake gefenta ta Duka Tana gaida Baba mallam ya amsa yana kallonta kafin yace"Ke kika Rikemin Mamana ko Hannatu..?
Hanne kanta na kasa tace"Baba nima yau ba zuwa na bane..Laifi tayi Ya Jafar yace zai daketa sai ta gudo wajena..!
Baba Mallam yace"Laifi..?ba na Hana su Jafaru tabamin Uwata ba..?na fada musu komai zatayi duka baya gyara Tarbiya Nasiha ne kawai mafita ballatana Duka Duka Mamana nawa take..?nan gaba sai kun yi mamakinta..!
Yafada yana kallon Amina da Ta dan Daga idanuwanta Sama kafin tace"Baba bafa Laifi nayi ba..Gidan kawata naje ta bani kudina..Baba Ranta fa tayi fa tace yau zata bani a makaranta kuma taki zuwa makaranta yau fa Baba ina Laifi Domin na Bita na amso kudina..!
Baba Mallam na yar Dariya yace"Baki da Laifi Mamana..Daman ai kyan alkwari Cikawa..!
Amina tace"Yauwa Baba..nasan Dama kai ne kadai zaka Fahimceni..!
Hajiya na Dariya tace"Daman ai Mallam baya kware miki baya..!
Malam yace"Wa kika Taba ganin ya kware ma Uwarsa baya Zainabu..?duk dan kwarai yana neman albarka ne..!
Hajiya Dariya kadai tayi batayi mgana ba Amina ce ta Zunguri Hanne Tana Fadin"Tashi muje..!
Tafada a Hankali Baba Malam Dake kallinsu tace"Ina zaku..?
Hanne tace"Gida zataje Baba..Zan Rakata ne..!
Agogon Dake manne adakin ya Daga ido ya kallah Goma Saura Kadan kafin ya Dawo da Kallonsa kan su yana Fadin"Dare yayi Mamana yau ba ki kwanciyarki wajen Hannatun taki..!
Amina tace"Baba itafa ke da kwana agidanmu ni na kwana na karshe ko Hajiya..?
Hajiya na Dariya tace"Kwarai kasan abun nasu Team team ne..!
Baba maallam ya gyada kai yana Fadin"To..to hakane..To ke Hanne yanzu Zagayowarki ne kenan..?
Hanne tace"Sai gobe in mun Dawo daga Hadda zan kwana Baba..!
Hajiya ya kallah yana Fadin"Yayi kyau..Hajiya bani Wayar nan Dake kusa Dake..!
Ba musu ta mikamai Wata Lafiyayyiyar waya Fara Samsumg ce,Ya karba yana fadin"ku zauna bari na Kira shamsu yazo ya rakaki Amina Dare yayi..!
Alokacin da aka ambaci Shamsu sai da suka Kalli Juna ita da Hanne Amina ta Kada ido aranta tace"Mugu.com kenan..!
Ammh Afili bazata iya mgana ba, bata ma Baba Malam gaddama Hanne kuwa ai tasan Halin ya Shamsu Duk gidanan yafi kowa mugunta Da Dukan Mutane ko bakamai komai ba.
Baba Malam yana Kokarin Kiran Shamsu Kira ya shigo wayarsa Cikin Mamaki ya kalli Hajiya yana Fadin"Sa"idu ke kirana Hajiya..!
Sunan da aka ambata yasa Amina ta Dago tana kallon Baba Malam
Hajiya kuma cewa Tayi"Kila mamah ake Cigiya..!
Ba musu ya Dauka da Cikakkiyar Sallamarsa kamar ko yaushe Sa"idu Daga chan bangaran yana Zaune afalonsa gefensa Mamammu ce Cikin Girmamawa yace"Allah yasa ban katse maka wani abu ba Baba..!
Baba Malam yace"A"a Sa"idu ina fatan Dai Lafiya..?naga baka Dade da fita ba..!
Aba ya Dukar dakai kamar yana Gaban Malam yace"Daman Maman yara nan ne tasa na kira wai ko Amina tazo nan gidan..!
Mallam yayi Mirmishi Kafin yace"Gata ma kusa dani Sa"idu..Ammh yansu zan saka Shamsu zai Rakota..!
Da Sauri yace"Tayi kwanciyarta nan mana Baba..!
Baba Malam yace"Tace ba ita ke da kwana ba Hannatu ce..Kasan mamar tawa yar Ra"ayi ce..!
Aba yar Dariya kawai yayi domin ya Daina mamakin Kaunar Dake Tsakanin Baba Malam da Amina abaya ya Dauka Domin tana da Sunan Mahafiyarsa ne sai Daga baya ya Gane Kaunace kawai Daga Allah..
Sallama sukayi da juna yana Datse Kiran ya Dago yana kallon Mamanmu Dake gefensa Cikin Basarwa yace"Kin ji tana chan yanzu..Shamsu zai Rakota..!
Daga haka ya cigaba da cin Abincinsa Domin Alkawari yayi ya Daina bari Lamarin Amina na Tadamai Hankali yanzu ma Mamansu ce ta matsa sai ya Kira Malam din yaji ko ta na chan
Tun bayan shigowarsa Duka yaran sun zo sun gaishesa banda Amina yasan bata gidan in tana nan itama Zatazo ta gaishesa.
Mamanmu Tayi Mirmishi kafin tace"Daman Nasam ai bata wuce Gidan Malam din..Nace ka Kira ne Saboda na Kore Bacin ran Dake Kan Fuskarka kan Amina din..!
Bai ce komai ba har ta Fidda rai da zai kara mgana sai chan taji yace"Uhm..Nifa ban Damu ba kawai dai naga ya kamata ko bata Fadama kowa zata fita ba..Ke mai karenta baki isa ta Fadamiki ga ta zuwa ba?..!ko don ita ta saba yin gaban kanta da yin abunda taga Dama..!
Mamanmu ta Bude zatayi mgana ya Daga mata Hannu yana Fadin"Ki kyaleni don Allah..Yau na dawo agajiyae bana son sabon bacin rai..!
Yadda ya fada din tasan Har ransa haka yake nufin yasa ta Hadiye mganarta ta koma gefe tana Sauke Numfashi.
Shi kuma bai kara kallon Inda take ba ya Cigaba da cin Abincinsa Kamar acikin Ransa bai da Damuwa nan kuwa Tsoro ne da Fargaban wani abu kuma man Gaba Amina zata jawomai.