← Book details Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 131 OF 193

Sashe 131

Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

Anty Amarya ta dago tana kallonta cikin rawar baki dana jiki tace"Ban..ga ne ba..?
Me kike nufi Uwani..?
Haj.Uwani ta saki wani kayattacen Mirmishi mai hade da cin nasara tana kallon cikin Idanuwan Anty Amarya wacce ta fara tsorata da Lamarin Uwanin tace"Kina sane da abunda nake nufi marliya ko na kira ki da Madina ne..?
Tafada cikin tsaida kallonta kan Anty Amarya wacce ta zaro ido jin Sunan da Uwani ta Kirata dashi Sunan da mutanen da suka santa dashi ba su da yawa suna ne da ta saka ma kanta Tun tuni domin cikar wani Buri nata.
Haj.Uwani ta fara taku acikin Dakinta tana Zagaye Anty Amarya tana Sakin Dariya kasa kasa kafin ta nufi kofar Bedroom dinta ta kulle ta harda Murza key ta juyo tana Fadin"Komai na Bukatar sirri madina duk da bansan da wacce kike zo ba..?
Anty Amarya da tagama Tsorata da mganganun Dake bakin Hj.Uwani baisa ta yi saurin karaya ba yasa cikin Gyara Tsayuwarta tace"Kina sane da duk abunda nazo dashi Uwani..Tunda ke kike aikata shi..Kashe rai fa kike yi fa Uwani..?
Kina lalata duk cikin da Sakina take samu yanzu in wannan mganar ta fita kina Zaton zaki kara Minti Daya acikin gidan nan ne..?
Tafada tana kallon Haj Uwani wacce ba karaya ko nadama ko kaadan a Tare da ita sai ma Zama da tayi gefen gadonta ta Dora kafa Daya kan Daya tabi Anty Amarya da kallo kafin tace"Ranar Biyan Bukata rai ba abakin komai yake ba Marliya a wajen ki na koyi wannan Tsarin sannan Da kike mganar in Labarin nan ya fita bazan kara ko minti Daya agidan nan ba..?
To wayace miki zai fita yanzu..?.
Ai ko zai fita sai na gama cika Burina Likacin na zama giwar mata ko mallam babu yadda ya iya dani marliya ballatana Hajiya da ban Dauketa wata Tsiya ba..Atafin Hannuna take kinsani..!
Bama ita ba gabadayanku a nan dina kuke ba wacce bansan duka motsinta ba..!
Ta karishe Fada tana Nunatafin hannunta cikin gadara Anty Amarya tayi wani mirmishin takaici kafin tace"Aiko kunyi kuskure Uwani..Wlh yadda kika yi sanadiyar Salwartar da Cikin Sakina sai nayi Sanadiyar da asirunki ya Tonu yau a idon Duniya..Yanzu ba sai anjuma ba, zan je na Sanar ma Hajiya komai domin ta gano Muguwar bakar Fusarki..!
Tafada a fusace kafin ta juya zata fita ta tsinkayi muryan Haj.Uwani Cikin Gadara.

"Bani kadai zaki tona ma asiri ba marliya Har da ke karan kanki..da wacce ta hada hannu Dake kuka KASHE YAYA..sannan kuma baya zatayi Zani marliya harta Danmallan zai gano cewa ba da Ra"ayinsa ya auri Sakina ba ke kika shiga kika fita hakan ta kasance..!

Da wani irin mamaki da al"ajabi da Faduwar gaba Anty Amarya taci Burki ta kasa juyowa ta Fuskanci Hj.Uwani Domin tana faman kokuwa da Faduwar gabanta na yadda Uwani ta san wannan Boyayiyun sirrukan da ga ita sai balaraba sai Malaminsu suka san anyi haka sai gashi a bakin Uwani to garin ya akayi ta san duka sirrukan su haka su basu taba sani ba..?
Tana wannan Tunanin taji Muryan Uwani a saitin kunnenta tana fadin"Kin yi mamakin ya akayi nasan Duka wadanan sirrukan naki ko nace naki keda Balaraba ko..?
Anty Amarya ta kasa gaba ballatana baya ba inda jikinta baya rawa Haj.Uwani ta saki Dariyan nasara kafin ta fara Tafiya zuwa gaban madubin Dake Dakinta tana Fadin"Nayi mamakin da sai a yanzu malaminki ya gano miki ni marliya ai na Dade ina shirina kusan ma nace na Rigaki shirya komai..Ni tuni Mama ta Bincikomin komai naki da ke da wacce ke tayaki dukkan ku wani motsinku ko sirrinku yana Cikin Tafin Hanuna Marliya abunda baku sani ba Kuna aikin ne ni ina warware muku..Kamar yadda Sakina ke barin Cikinta haka in wannan balarabiyar ta samu ciki ita ma haka zatayi ta barinsa hakama Amina ita kanta ban kyaleta ba na shigo da ita cikin Tsarina..Tsarin da zai kai ni nan da Lokaci kadan na cika Burina..!
Sai alokacin Anty Amarya ta Juyo tana kallon bayan Haj.Uwani Cikin Rawan baki tace"Wani irin Buri ne wannan da kika Zabi ni ki hanani Cikar nawa burin.
A bar batun Rufa Rufa Uwani Tunda kinsan komai ba amfani na cigaba da Boye miki manufata ni in kinyi Hakuri ba mallam nake so na mallaka ba..Kawai Sakina nake so ta Zama Mowar mata wajen umar da Danginsa..Sannan ita kadai ce nayi ma alkawarin zata haifa ma Umar magaji ta kuma Haifa ma Hajiya da mallam jika mafi soyuwa bayan ita ban yarda wata tazo Daga baya ta fita ba..Sannan in hakan ta faru nasan nima zam zama Shalele a wajen mallam da Umaru tunda nice silar duk abubuwan da suka faru..!
Ki fadamin meye naki burin da yasa ni kika ki bari nawa burin ya cika..?
Ina so naji irin naki Burin akan mallam da zur"arsa..?
Haj. Uwani ta juyo tana kallon Anty Amarya ido na cikin Ido kafin tace"Ko baki tambayeni ba zan fada miki..Boye boye ai ya kare. tunda malamin ki ya gano miki ni Marliya..Karkade kunnuwanki Ki sha Labari yanzu zan sanar Dake yadda naki Cikar Burin ke neman yayi min Cikas kan nawa Burin da nayi shekaru ina Wahala akansa..!
Komawa tayi ta zauna ta kara Dora kafa Daya kan daya kafin ta fara Fadama Anty Amarya duka shirinta da nata tsarin da Burin datake dashi akan mallam da ahalinsa ta karishe da Fadin"In har na bar Sakina ta Haihu Da Umar kin batamin Tsarina marliya..shiyasa na hana faruwar haka sannan bama ita ba indai ina Raye Umar bazai ga kwansa a Duniya ba..Tunda na gano Mallam yana matukar son yaga jikokinsa ta bangaran sa na mike tsaye na shiga na Fita na hana faruwar hakan..Ya"yana kadai ne zasu haifama mallam jikoki kuma ya sosu ni kadai ce zan zama Tauraruwa ba Hajiya ba..In ta samu mallam a baya awannan gabar Lokacinta ya kusa karewa..!
Nasan zaki ce ina Nazir da Nasir da na bari suka haihu.?
Ai suma din ba gazawata bane Marliya Tsarin aikina ne..Daga ya"yan Nazir din har Nasir din wa kika gani mallam ya Damu dasu?
Ai nasa mama ta Dakushe wannan Tasirin har Abada kuma bazasu yi shi a idanuwansa ba Nazeem ne kadai da Uzairu zasu haifa masa jikoki su zama Sanyin Idanuwan mallam bayan su kuma nayi alkawarin har Abada ba wanda zai haihafama mallam Jika Tun balle ma Danmallam da mallam ya fi so cikin ya'yansa shiyasa kika ga inayin Duk abunda nake so..!
Niso nake nan gaba ya"yana su zama sune Hop din mallam gabadaya Sune komai nasa bashi da yarda zai yi sannan kuma alokacin ni zama giwar a cikin matansa ko yana so ko baya so..Ya'ya ne kan gaba a dukiyarsa sannan wajen haifa masa jikoki ma sune kan gaba Dole kauna da soyayya ta koma kaina da Ahalina gabadaya..Mganar Sa"idu bai gabana domin ke da Balaraba kun Rage min wannan aikin..Lokaci kadan nake jira na Aiwatar da Tsarina akansa kamar yadda na Tsara..!
Ta karishe Fada tana kallon Anty Amarya wacce tayi mutuwar tsaye ta kasa ko motsi da jin wannan labarin lalle Haj.Uwani ta fi su zama Shedaniya,Su ashe bakomai ma sukeyi ba,Shekaruna nawa ta kwashe tana Wahala ammh Lokaci kadan Uwani tana neman Tsawartata to bazata bari ba,Bazata yi Saurin karaya ba,sai ta nuna mata in ita a Tsaye take ita a tafe ta kwana..!
Ta kalli Uwani cikin Bakinciki kafin tace"meyasa Burinki ya yi kamanceceniya da nawa .?
Meyasa sai dole kin Tsawartsani Uwani meyasa haka..?
Haj.Uwani tayi kasa da Murya kafin tace"Ki yi kasa da muryanki mana marliya..Ai na riga na Fada miki Dalilina..Bake kadai na taba ba..Na Fada miki yadda na Raba Hajiya da ya"yanta a kusa da ita,Na maida Nasir mara amfani a wajen maallam na hanata ganin jikanta ta Tsatson babbar Danta ita meyasa batace ina so na Tsawartata ba sai ke da Duka Dagani har ke muna kan Turba Daya ne marliya..?
Anty Amarya na Huci tace"To baki isa ba..wlh uwani karyan ki ta sha karya..!
Haj.Uwani tayi Dariya kafin tace"Nama isa ai marliya..Kaawai ki yi Hakuri ki mara min baya Burina ya Cika in hakan ta faru nayi miki alkwarin Raba komai gida uku na Dauki Biyu na baki kashi Daya. !
Anty Amarya ta harareta kamar Idanuwanta zasu fado tace"Me kike nufi..?
Haj.Uwani tayi Dariya kafin tace"Ki hakura da Sai Sakina ta Haihu marliya..!
Anty Amarya ta Zumduma ashar kafin tace"Ina..Baki isa ba Uwani..Bazaki Hada baki dani ba..Kowa ya Tsaya da kafafunsa..Sannan kuma sai dai ki kare a muguntarki kina ji kina gani Sakina zata haifarma mallam da Hajiya jika sai dai bakin ciki ya kasheki. !
Tafada tana kumfar Baki Haj.Uwani ta tabe baki kafin ta Daga kaafadanta tace"Shikenan marliya..Kije ki cigaba da Wahala..Ammh ina mai kara gayamiki..in sau Dubu sakina zata samu Ciki sai ya Zube haka Sarood hakama Amina ke ko aure ya kara itana irin Tsarin dana Dora su itama akan shi Zan dora ta Marliya na Fada miki kan Cikar Burina zan iya aikata komai..!
Anty Amarya taji wani abu ya Tsaya mata a wuya kawai sai tayi kukan kura ta kara shako Haj.Uwani cikin Hargagi take fadin"Me kika baa sakina tasha..?
Ki Fadamin abunda kika Binne da kudin da kika kashe akan hana Sakina Haihuwa Uwani..?
Kwace wuyanta tayi tana Hararan Anty Amarya Lokaci daya tana Fadin"Wlh in kika kara saka hannunki kika rikeni sai na Sharara miki mari marliya..!
Ki kama kanki kafin Zuciya tajaki ki aikata abunda zaki zo kina Nadama..!
Anty Amarya na Haki ta nuna Haj.Uwanu tana fadin"Wlh kin yi kadan..Nayi alkawarin sai nayi sillar Tona miki asiri..!
Haj Uwani tace"To ai ban Hanaki ba..tunda baki min godiyar Taimakon ki da nayi ba akan Amina da Sarood ba, wato sakina kadai kike so ta Haihu ban da su ko..?
To tunda baki ga Hallacin da nayi miki ba Shikenan jeki fadama wanda zaki Fadamawa ammh ki sani in asirin ya tashi Tonuwa naki sai yafi muni Marliya ni iya ka dai mallam ya Sakeni ko..?
To in ya sakeni ai bai kare ba ina da Zaratan maza har uku ko da sun ji abunda ya faru basu isa su sauya ni a matsayin uwa ba marliya,Sannan kuma dole zasu neme ni kefa wa kike dashi..? Duka ya"yan ki mata ne baki da wani gata anan duniya iyayanki zasu yi Tir Dake ya"yan ki mata zaki bar musu abun kunya in ma bai taba auransu ba,Sannan Uwa uba kuma agaban idon ki Umar zai Saki Sakina kinga Daganan kin kare a Tutar babu..Wahalar ki tatashi a banza kenan kuma ke ahakan ma naki Tonuwar asirin mai kyau ne,akan na Balaraba ita wlh ko kaffara bazan yi ba kare sai ya fita Daraja in sirrin Boye ya fito Fili sai ta wulakanta ta Tozarta a wajen Sa"idu da Danginsa da kuma ya"yan Yaya da kukayi Sanadiyar barinta Duniya Saboda cikar naku burin..!
In kin yarda da duka Faruwar wannan shikenan u can go..Ki je ki Fadama Hajiya sai mu shirya bankadewar siirikan namu dani da ke da balaraba alokaci Daya ko banza na San Dagani har ke bamu samu cikar Burukan namu ba..!
Tafada tana wata yar Dariya Anty Amarya duk yadda taso kada ta nuna Rauninta sai da ta nuna Hawaye ya wanke mata Fuska ta nuna Haj.Uwani da yatsanta Cikin Kaushim murya mai Cike da karkawa tace"Ki Rubuta ki ijiye Uwani Indai ban samu abunda nake so ba..Na rantse ko Zan yi yawo Tsirara sai naga kema baki samu abunda kike so ba..In juran ki sammako ni madina a tafe na kwana mu Zuba mu gani..!
haj.Uwani ta bata amsa da cewa"Shege ka fasa marliya..!
Daga haka Anty Amarya ta murza key din ta Bude kofar ta Fice tana kuka Duk yadda taso ta shanye kukanta ta kasa bakinciki da Takaicin sun taimaka wajen Fitar Da ita daga natsuwarta uwa uba kuma da yadda Gabadaya sirrukansu yake tafin Hannun Haj.Uwani
Hajiya ta fito kenan Daga Shashenta zata shashen Haj.Uwani suyi mganar wani Turaran wuta da suka je Bikin nan maiduguri tace tana so yagana ta kirata kan mganar ne yasa tace bari ta shiga ta fadamata..
Ta sawo kanta Falon kenan Anty Amarya na fita da gudu tana kuka Hajiya sai ta Rude hankalinta ya tashi ta rika fadin"Subhanallah Amarya Lafiyanki kuwa..?
Ina ko jinta batayi ba batama ganta ba Domin kuncin datake ciki ya Rufe mata jinta da ganinta har ta fice Hajiya na Kallonta sai jikinta ya kama rawa tana Fatan Allah yasa ba wani abun ne ya Faru da Sakina ba kamar ta bi bayanta sai kuma ta fasa ta karisa Cikin Falon Haj.Uwani tana Fatan taji abunda ya faru Daga bakinta.
Chapter 131 · 0% Book details