← Book details Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 193

Sashe 74

Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Kwana Goma sha daya da Rasuwar yaya suka koma gida ya rage daga Amina sai hanida sai zeenatu da Jawaad sai mamanmu da Aba. !
Sati biyu da rasuwar suka koma makaranta Boko da Islamiya,Saboda zasu fara jarabawa su ya Zeenatu har sun fara Neco..,!
Komai ya tafi kan tsari sai dai Abu Daya ne yayi ma mamanmu cikas Wannan Raunin data so gani awajen Sa"idu bata gansa ba sai ma wani Takwalli Daya shigesa..!
Ko sau daya bai zubar da Hawaye agabanta ba..!
Balle taga Rauninsa ko kananan kukan gulma take sai dai ya kalleta yace"Muma fa jiranta muke yi Balaraba..Hadiza batayi gaggawa ba..!
Fatanmu Allah ya rahamsheta..!

Bata gani ba har yau bata gani ba..Sannan Gurbin yaya har Abada Sa"idu bazai taba bata ba..bayan Mutuwar taso komai ya zama karkashinta abunda bata sani ba Allah ya riga ya Rubuta kaddaran kowa ciki harda nata in ta Kauda yaya to ba Lalle ta samu cikar Burinta ba zata samu wani wanin kuwa har ta koma ga Allah bazata taba samun sa ba..!

*Janafty**TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*

*🅿️25*

*BAYAN WATA DAYA..!*

Acikin Wata dayan daya gabata na rasuwar yaya komai ya fara dawowa daidai,Wadanda akayi ma rashi sun Dauki Dangana da Tawakkali,Mussaman Aba da su Amina da yanzu ta fara dawowa da Walwalarta sai kuma yanzu take matukar kulawa da Jawaad tana Taausayinsa gani take daga shi sai ita sukayi rashin yaya basu da wata matsala Domin mamanmu tana Tsaye kansu da Fuskar da suka santa da ita,ya taimaka wajen dawowa da walwalar yaran har wadanda ke gidan auran nasu,Uwa uba ga Hajiya babba da bata bari sun yi kukan maraici ba Duk da ga Mamanmu tare dasu tana zaryan zuwa Dubasa barin ma in Taga Amina ta kwana Biyu bata leko ba
Acikin kamshin Nasaran da Mamanmu take gani ta Samu bayan kasa ta Shafe Idon yaya abu Daya ne zuwa Biyu na Farko ta samu yardan yan"uwa da Duka Dangin Baba Sa"idu sannan Aminci Data gina shekaru masu yawa da yaran bai gurbace ba yayi mata amfani sosai gabadaya su ya jafar da komai nasu yana Tafin Hannunta ne tun yaya nada rai yaran da ita Suke shawara sai dai yayan taji Daga bakinta to har yanzu bata Sauya Zani ba ballatana yanzu da ba Uwarsu sai Duka yardan da Amanan ya koma kanta Harta kuwa Jafar da Abaya yake da Kulafunci nuna yaya ce uwarsa ba Ita ba shima yanzu wani girma yake bata kamar me yana ganin ta tamkar makwafin yaya..!
Gida ya zama nata ita kadai Yaran suna Tafin Hannunta sai dai Abu Daya ya Gagareta Samun SA"IDU yadda take so,Sannan kuma wannan Raunin da taso gani atare da Sa"idun bata gansa ba,Sai ma wani Jarumta da Takwalli bata so ta gansa Tsaye kan kafafunsa ba taso ace yana kwance ne yana Fama da wannan Babban rashin sai Taga akasin haka sai dai bata Sare ba ai ta Rabasu Wannan kallon kauna da Tausayin Sai dai in ya Bita chan Lahira ya nuna mata anan Duniya dai ta gama Shiga Tsakaninsu..!

Bayan Bakwai da rasuwar yaya ta kasa gane kansa ya daina cin abinci baya Fara"a baya Hira da ita ballatana mgana mai Dadi haka zasu kwana su tashi in ba ita tayimai mgana ba shi bazai ce mata ba  tasan wani Lokacin bai da Hayaniya ammh tasan Rashin mganarsa yafi Faruwa akanta In yaya ce keda Turaka kusan Raba Dare suke suna Hira cikin Nishadi bata san Darare nawa ta bata cikin bakincikinsu ba Domin tana Daga Dakinta in Dare yayi tana jin tashin muryoyinsu In kuma ranar itace keda shi Daya gama cin abinci yayi wanka Sai ya fara Hamman barci tana mai Hira sai ya fara barci ma"ana baya son Hirarta ta Dade tana kunsan bakincikin Sa"idu shiyasa bayan Rasuwar yaya ganin zai bata wahala yasa ta sa madina ta kai ma malaminsu korafi aka Samo mata kansa shine har ta Fara Tunanin Burinta ya fara cika Sa"idu da komai nasa yana Hannunta..
Tunda yanzu In ya dawo aiki yaci abinci yayi wanka ya kan zauna su yi hira koda bazai amsata yadda take so ba ammh cikin kaso goma tana da Nasaran kaso Takwas aciki Abunda ya Rage mata shine ta fara sanin komai nasa kamar yadda yaya ta sani sai dai har zuwa yanzu yaki bata Damar haka!

Yau ma kamar kullum safiya ranar asabar ce ta hutun karshen mako,Ba kowa agidan duk sun tafi Hadda,Sai ita kadai da Aba bai fita yau da wuri ba,Kamar yadda ta tsiro dashi yanzu Gari na wayewa kafin Aba ya fita sai ta Chaba kwalliya Kamar wata yarinya bayan makircin karkashin kasa har da na Kissa Madina tace ta Dinga Hadawa duk a Kokarinta na sai taja Hankalin Sa"idu akanta gabadaya..!
Abunda bata sani ba ita zuciya ba"ayi mata Dole kan abunda tagani kuma tasan dashi ammh ta nuna bata so..Sannan duk da tana son mai kyautata mata bata cika bashi matsayin daya Zarta wanda ta zabe ta da kanta ba koda bai taba mata wani abu na Alheri ba..!
Zaune suke afalonsa yana karyawa ita kuma tana gabansa kamar mai kirga yawan Numfashinsa Hira take yi mai yana jinta yawancin Labaranta ba wasu masu amfani bane,Shiyasa yake mata Shuru kawai batare daya tanka ta ba,Har kuma gobe bazai daina kukan Rashin Hadiza bai jin zAi iya mantawa da ita.
Jin tayi shuru yasa ya Dago Daga cin Soyayyan Dankalin data soyamai ya ganta tayi Tagumi tana kallonsa Cikin dan mamakinta yace"Lafiya..?Me kike Tunani..?
Alokacin bakincikin Tambayarsa taji Saboda tafi kama data rainin wayau ta Zauna tanayimai Hira yayi mata banza sannan ya Dago yana ce mata Lafiya..?Saurin Daidaita kanta tayi ammj bacin rai yasa Kiris ya Rage Dayan Fuskar tata ta bayyana.
Cikin sosa ido da hanci ta fara fadin"Yaya na tuna..Bana iya kwana na Wuni ban yi kukan rashinta ba..Ballatana in na gifta Dakinta sai naji gabadaya Duniyar ta Juyamin baya..!
Tana Fade tana matso hawaye kamar gaske ya Dade yana kallonta kafin ya maida kansa ya cigaba da cin Dankalinsa yana jinta tana Fadin"Wlh nima sai naji Duniyar duk ta isheni Abbansu..Dama nima na mutu kamar yadda yau ba yaya adaron Duniya..!
Sai da ya Kurbi Tea din Dake hannusa sannan ya Dago yana kallonta Cikin Sanyinsa na koda yaushe yace"Zo nan Balaraba..!

Baki ta bude tana kallonsa Ganin haka yasa ya gyada mata kai alaman tazo ba musu ta mike ta isa kusa dashi ta zauna Juyowa yayi suna kallon juna Hannayenta ya kama Duka ya Rike yana Tuna Nasihan Baba Mallam aranar da Hadiza tayi arba"in da Rasuwa ya Horar dashi Kada rashin Hadiza yasa ya cutar da Balaraba ya sani Ko sau Daya ya Danne mata Hakki Allah zai tambayesa..!
Chapter 74 · 0% Book details