← Book details Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 193

Sashe 73

Ta Fita Zakka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Akaron farko Amina ta fashe da kukan daya rike mata zuciya in Tana ganinsu ya Jadwa na kuka sai taji su gwara su yaya bata bar duniya tana Fushi dasu ba gwara su sun samu kyakyawan Mu"amala ita fa bata da wani abu da zata Dorar Tsakaninsu in yaya ta saka baki a lamarinta to na Bacin rai ne ba na Dadin rai ba..!
Kuka take kamar ranta zai fita cikin kukan ta Rarrafa gaban Aba ta kama kafarsa tana fadin"Aba ka yafemin..Don Allah ka yafemin kada kai ma ka rasu ka barni baka yafemin ba kamar yadda yaya tatafi ta barni tana Fushi dani..!
Haka take fada tana wani irin gunjin kuka,wanda duk mai Tsausayi da Imani sai ya Tsausaya mata hatta kuwa da Danmallam Dake gefe sai da ya Dago ya kalleta cikin wani yanayi..!
Hajiya baya ta juya tana sharan kwallah Baba Mallam ne mai Dakiya yana Binsu da kallon Tsausayi..!
Jawaad yayi barci shi yasa Aba ya kwantar dashi kan kujera sannan ya saka Hannu ya Dago Amina yana Fadin"Hadiza bata rasu da Haushinki ba Amina..Komai kikayi sai dai tace Allah ya shiryaki..Bata taba aibataki b .....Addu"ata gareki mai kyau ne Amina..!
Hajiya babba ta amsa da cewa"Kuma addu"anta baza ta taba fadi abanza ba.Da yardan Allah zaku yi alfahari da Amina Hadiza zatayi alfahari da Amina ko bayan kasa ta shafe idanuwanta ne..!

Yanayin falon ya koma na Jimami Barin ma yadda Amina ke kuka Data Rumgume Aba tanayi kuka mai Cin rai Baba Mallam ne yaga kukan yayi yasa yace"Mamana tashi nan bar kukan nan hakanan kina tadama Babanki Hankali..!
Sai Lokacin ta bar jikin Aba ta sulale kasa tana Fadin"Ka yafemin Aba..!
Yana kokarin Dauke Hawayen idonsa yace"Ban taba rike ki ba Amina..Komai kikayi min na bacin rai ina yi miki uzuri Wlh..Hadiza koda yaushe fadi take mu yi mata Fatan Shiriya mu yi fatan Allah yasa in ta Girma ta sauya..Na yafe miki Duniya da Lahira Amina Allah yayi miki albarka..!

Tana kuka take amsawa da Ameen kafin ta Rarrafa gaban Baba Mallan rikota yayi ya Tadata ya zaunar da ita gefensa ya saka Gefen rawaninsa ya Share mata Hawaye yana fadin"Bar kuka..Addu"a zaki rika mata in kin Tunata kinji ko..?
Kai ta gyada mai tana sharan majina Hajiya Babba tace"Kabarta tayi kuka Mallan tun fa rasuwar nan banga tayi kuka ba..!
Sai Alokacin goggo Husai ta tanka"To zainabu sai kuma abarta ta tadama Mutane da Hankali..?
Tana Raye bata huta da Jidalin Amina ba bayan ta rasu bazata barta ta Huta Cikin Salama ba..!
Da sauri Baba Mallan yace"Husai kibar wannan mganar..Hadiza zata Huta cikin kabarinta da yardan Allah Shaidar duniya itace ta Kiyama..!
Dole ta koma tayi shuru domin ita bata da wannan Sakewan da yara shiyasa Tuni taso Sa"idu ya bata Amina tatafi da ita da Tuni duk wannan Tabaran ta daina shi
Ita gani take harda da Laifin Sa"idun da su Mallam din..!
Nan Baba Mallam ya cigaba da Lallashin Amina har sai da ta bar kuka sannan ya kalleta yace"nima zan baki Hakuri Mamana..Nayi miki laifi nayi sonkai..Na rabaki da wanda kike so na aura miki Da"a na..!

Sai kunya ta kama Amina ta kalli Baba Mallam da manyan Idanuwanta kafin tayi mgana Ya saka baki ya Kira Umar Dake gefen Aba kansa na kasa kamar baya Falon
Gaban Baba Mallam yazo ya Durkusa Cikin Sanyin sa yace"Gani Mallam!
Ba zato kawai yaji ya Damki hannunsa ya Hada cikin na Amina cikin Dattakonsa yace"Ga Amanar Hannun Mamana nan Umaru..Ko bayan raina ban yarda ka saki ba..Ko Laifin me ta maka ka Duba girmana ka mata afuwa ka yi juriya kan Hallayarta ka zama mai mata Nasiha yayinda ta bata maka Sannan Daga karshe ina fatan zaka riketa Bisa gaskiya da Amana sannan ka kwantatanta adalci Tsakanin matanka..,!

Gabadaya sai jikinsa ya Mutu hannuwan nasu yabi da kallo kamar yadda Amina itama take bin Karamin hannunta Sarke cikim Tattaausan hannun yaya Danmallam mai cike da gargasa da kallo..!

Bakinsa yayi nauyi da wannan Abunda Mallam yayi shiyasa ya jinjina kai kafin yace"Insha Allahu Mallam..Allah ya kara girma..!
Ya amsa da Ameen har Lokacin hannayensu na Sarke da juna Hajiya Babba ta kallesu farimciki ya cikata Cikin wani yanayi tace"Yadda kuke rike hannun juna..Allah yasa ko a Lahira tare zaku tashi rike da hannun juna..Allah ya Hada zuciyoyinku Waje daya..!
Gabadaya aka amsa da Ameen Aba na gefe yama kasa mgana Alherin Baba Mallan garesa ai mai girma ce..!
Goggo hussai tace"Sai faman bashi Amana kuke yi kun manta Amina..?Kai Umaru kalleni nan..Kada ka damu da mganar Mallam ko ta Hajiya..Amina sai da wuta..In tayi maka ba Daidai ba kaci Zarafinta kada kayi mata da Sauki Domin kai zaka sha Wahalanta Ahtto..!
Tafada bilhakki da gaskiyanta Dayasa Hajiya ta Murmusa tana fadin"Ke fa Goggo ce Husai..!
Tace"Ai na sani shiyasa nake Fadamai gaskiya..jidalin Amina ai Allah kadai yasan shi Har Hadiza ta bar Duniya bacin ranta Daya kan Amina..Allah yasa ta samu ma uwar goyo ta gari ai da ba Domin Balaraba ba da Amina kuma sai Allah..!

Amina na jinta ita yanzu komai ma ya zama mai Sanyi awajenta in da abayane ta Tabbata Sai ta Tura mata baki tayi gunaguni kamar baya ammh yanzu sai taji ta kasa bata cikin Hayyacinta har yanzu Aminene bata Dawo ba Amina ce da kanta yanzu..!
Ta manta da Hannunsu dake Waje Daya sai da taji ya Sabule hannunta Sannan ta Dago suka hada ido Saurin Dauke kansa yayi saboda wani irin abu yaji acikin ransa kamar na Tsausayi itama kanta ta Dukar tana wasa da Hannunta gabadaya kalaman Baba Mallam sun gama riketa ita kuwa me ta aikata ne..?
!Da Alherin Baba Mallam da Hajiya ya Lullbe Rayuwarta haka..? Har Abada bazata manta dasu ba kamar yadda bazata manta da kaddaran data Hadata da Masoyinta Aminu ba..!
Baba Mallam yayi gyaran Murya yana Fadin"Umaru me ka yanke kan Mamana..?Ina Nufin kana da wani Tsari ne..?
Kansa na kasa har Lokacin yace"Tsari na na Ubangiji ne Mallam..ba ni da wani Tsari..!
Sai dai bazan ki duk abunda ka Zartar ba..!
Baba mallan yaji Dadi Cikin Fara"a yace"Naji Dadin haka shiyasa na Tambayeka..Zan yi ma Mamana adalcin da nake yi ma kowa..Bazata Tare ba sai ta gama makaranta Umar..Nan da shekara Daya da wani abu kenan tunda Hajiya tace suna aji Daya na Babbar makaranta sun kusa shiga Aji Biyu..!
Zata kamallah makaranta da Walimar sauka zan hadata da sauran yan"uwanta Hamida da Hannatu da Sa"aadatu na aurar dasu ita kuma sai ayi Bikin Tarewarta alokacin bazan karbi Uzurinka ba na baka Lokaci ka Tsara komai inda zaka ijiyeta da yadda zaka zauna da iyalanka..!
Goggo Husai tace"Mallam me zai hana tunda anriga an Daura ayi Tarewan ba Nisa?
Kai ya Girgiza kafin yace"A lokacin Auransu nayi gaggawa Husai..ban kuma bama yaran nan dama ba Husai..Bana so na kara maimaita irin haka Shiyasa na Dibi wannan Lokacin bana Fatan wani Daga cikin su yaji aransa ban mai adalci ba..!

Ba wanda bai gamsu da mganarsa ba Ya Danmallam kamar ya goya Mallam haka yaji dama Fargabansa ace ya tafi da ita ko kuma mganar Tarewa Amina kuwa acikin ranta itama Hamdala Take yi Domin bata shirya ba..Bata Shirya karban wannan Kaddaran ba Har yanzu..!
Goggo Husai tace"Shikenan..Ni na Dauka zaka hadata dasu Zeenatu ne.?

Kai ya girgiza kafin yace"A"a ai ba Sa"aninta bane..So mganar su ma tana nan Rasuwar nan ne ta hanani nayi mgana yaushe ne zasu fara Jarabawar Fita ma kikace Hajiya..?
Hajiya tace"Sati na sama Abida tacemin Mallam.!
Cikin Dattakonsa yace"Zan bama Mazajensu dama zasu fara zuwa su gana dasu..Mai son Zeenatu dan wajen Aminina Mallam Hamza ne Dake Gombe,Babbar D'ansa Ahmad Soja ne..Sai mai son Abida na gida ne Jikan kawuna Lawali na Bazanga Dake Jamus..? To yaron wajensa ne Yana Porthercourt yana aikin Zanen gidaje ko wannan Gaisuwan da suka zo shi kawu Lawalin ya karamin mgana..!
Goggo Husai ta fara fadin"Masha Allah..Allah yasa a kulle alheri..!

Aba ma yayi fatan Alheri shi da Hajiya
Baba mallan ya kalli Danmallam yana Fadin"Baka ce komai ba Umaru..?
Cikin Ladabinsa yace"Hakan yayi mallam..Allah ya saka da Alheri ya kuma kara girma..!
Cikin Fara"a yace"Ameen Allah yayi muku albarka..Tashi kaje ka Dauki iyalanka kuje gidanku ku huta..Ina fatan zaka kwana Biyu kafin ka koma..?
Cikin Kankantar dakai yace"Jibi zamu koma Mallam..Saboda aikina na iya adadin kwanakin da aka bani kenan..!
Baba Mallan ya Jinjina kai yana Fadin"Shikenan Allah ya kaimu..Mamana tashi ki bisa ka rakata har kofar gida ko wajen Hajiya zaki kwana..?
Kai ta girgiza kafin tace"Eh..!
Da sauri domin bata son ahadata dashi jin haka yasa Danmallan yayi musu sallama ya Fice daman shima Takuramai Mallam zai yi ko Cikin gida bai koma ba ya Kira Sakina awaya yace ta fito su tafi..!
Amina kuma sai da tattabatar da sun tafi Domin taga Budewar get da Fitan Mota ta kuma tabbatar da Shine sannan tayi musu sallama ta wuce shashen Hajiya..!
Koda taje har ya Abida tayi barci sai ya Aisha ce da ya Zulaihat ke zaune ashen nan sukayo Dadi taji Dataga su hanne da Hamida Zafira sun koma gida Tun jiya..!
Bata ma kowa mgana ba Kujearan falo mai zaman mutum uku ta Dungule akai tana Sauke ajiyar rai su kuma sai suka sauya hira daman Hirar Aminar Suke da Al"ajabin Auranta da Yaya Danmallam,Sai dai kuma ko su Hanne da sukasan Dalili basu ce komai ba Domin Sirrin Amina Wajensu bazai Taba Faduwa ba koda ba awaje bane na gida ne..!
Sai awannan ranar Amina ta samu barci Domin batasan Dawowar Hajiya ba
Washegari kuma su ya Jawahir suka fara tafiya,sun yi kuka Lokacin sallama kafin yammh gida ya Rage sai ya Jadwa da Goggo Husai da Goggo Jumai duka sun koma Gidajensu har su ya Zahra..!
Chan gidan Baba Mallam ma Duka sun koma gidan auransu gida yayi tsit dayan washegarin kuma Ya Danmallan suka koma shi da Sakina Basu hadu da Amina ba itama Goggo Husai taji Tana mganar Tafiyar tasa..!
Tun Ranar ashashen Hajiya suke kwana har Hamida sai da su goggo Husai suka samu Visa suka tafi gida ya zamana ba kowa yasa Hajiya tace su Amina su koma basoda Mamanmu kada kadaici ya Dameta..!
Chapter 73 · 0% Book details